← Book details Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 36

Sashe 6

Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

BA’A SHAN
ZUMA… 18
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Angaji da jiranta hakan yasa
aka fara kawai, dasauri tashigo
tazauna, ruwan tumatur agefen
riganta tana kokarin
kakkabewa, kanta a kasa
yayinda wacce tafarayi
agefensu takeyi, kasancewar
sune yan supporting, tana
gamawa daga yan opposing ,
first speakernsu yafito yayi
sannan yakoma anan aka kira
sunanta
Firdausi kabir sani, tafito a
sanyaye ta tsaya, sannan
takalli high table din tafara
bayaninta
"Mr.principal sir, honourable
panel of judges, accurate
timekeeper, co-debators, my
collegue,ladies and
gentlemen…….." Kanshi na
kasa daga kan high table
yadago dob ganinta, fararen
idanunta yagani, yayinda take
bayaninta, yadda take furta
haruffanta bawanda zaiyi
tunanin daga kauye take,
tashin birni kawai, don tana
fitar da kowanni kowanii hakki
na kalamunta, yadda take
Haka yata kallonta harta idar
da batunta, wani tafi hall din
yadauka kowa na tofa
albarkacin bakinsa, yayinda
alkalai suketa zuba mata mark,
haka kowa yazo yayi nasa.
Shikam hankalinsa yayi kanta,
idonsa zur akanta har abokinsa
nagefensa yadan sunkuyo
sannan yace
"Yadai lafiya naganka haka?"
Yadan gyra murya don muryan
takame ta ciki yace
"Wacan yarinyan, second
speaker"
[10/12 01:16] Lubieee: BA'A
SHAN ZUMA.. NA
LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Murmushi Faroukh ya saki,
yace "kai ko meye hadin ka da
ita? Ko ka santa ne?" Ya
girgiza kai, yace "voice dinta
ne exactly irin na ummi na,
look at ha, hatta yanayin ta
wlh" yace "haba abokina, ni
kam banga kaman ba, ko dai
ko dai?" Ya fada yana daria.
Suna haka, aka fara kiran
daliban don su anshi
kyaututtukan da aka tanadar
masu, aka kira 3rd position,
sannan 2nd, sai daga karshe,
principal ya anshi mic ya fara
jawabi, wanda duk yawancin
bayanan nashi yayi su ne akan
namijin kokarin da deedo tayi,
ya yaba mata, sannan daga
karshe yace "I'll like to call on
stage Dr. NAWAF KHAMIS!" Ya
mike cikin takun shi na kasaita,
kowa a wurin hankalin shi yayi
kan shi, the most honourable
nd young academic Dr. Ya
karasa gaban principal ya mika
mashi hannu, bayan sun gaisa
ne principal din ya bashi mic,
tare da wata yar paper ya koma
wurin shi ya zauna. Ya buda
papern cikin voice din shi mai
wani irin zaki da girma, irin ta
cikakken namijin da ya ansa
sunan shi, ya kuma san abinda
yake yi, ya fara jera tsararran
turancin shi wanda ya tafi da
imanin mutanen da suke wurin,
most especially Deedo, wadda
a duniya ba abinda take so irin
taga hadadden namiji dan boko
wanda ya iya tsara turanci. Ya
gama jawabin shi, sannan ya
kira FIRDAUSI KABIR SANI a
matsayin dalibar da ta zo 1st a
cikin daliban, nan da nan wuri
ya kaure da tafi, ita kuma a
natse ta mike, kanta a kasa ta
karasa saman stage din. Nawaf
wanda tunda ta taso ya zuba
mata idanun shi, har ta karaso
gaban shi, nan ya dauko gifts
dinta, ya bata, haka duk abinda
ake ya kasa dauke idon shi a
kanta.

BA’A SHAN
ZUMA… 19
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
A haka aka gama gabatar da
duk abinda ya dace, sannan
aka rufe taro da addu'a, kowa
ya kama gaban shi.
Ana fitowa Deedo tare da hally
suka rungume juna,suna
murna, nan da nan wasu
hawayen farin ciki suka saukan
mata, ta kalli hally tace "ina ma
ina da wani wanda zaiyi proud
dani a irin wannan ranar, ina
ma iyayena suna raye suga
wannan abin farin cikin da ya
same ni" hally tace "kar ki
damu Deedo, Allah yana tare
dake, haka nima ina tare da ke
100%, iyayen ki kam ki dage
da yi masu addu'a, shine
babban abin da suke bukata
daga gare ki" ta share
hawayen, tace "in sha Allah
hally, nagode miki da duk wani
abun alkairi da kikai mun a
rayuwa, bazan manta dake ba
har abada" suka jero da niyyar
tafiya gida, sun zo ta wurin
staff room zasu wuce wani
yaro yazo yace "Deedo ana
neman ki a office din principal"
bata tsaya bata lokacin komai
ba, ta mika wa hally gifts din
da suke hannun ta, sannan ta
wuce zuwa kiran da ake mata.
Tana shiga ya dago dara daran
idanun shi masu matukar
haske da sheki, bai aje su a ko
ina ba sai saman kyakkaywar
fuskar ta. Dam taji gaban ta ya
buga, ta karasa da sallamar ta,
ta samu gefe ta duka. Principal
ya maida kallon shi ga Nawaf
yace "Wannan kake nufi?" Ya
girgiza kan shi alaman ita fa,
principal din yace "no problem,
ga ka ga ta ai" kafin Nawap ya
buda bakin shi, wani teacher
ya leko, yayi ma principal
magana, haka ya mike ya fita,
ya bar su a office din daga shi
sai ita. Kallon ta yake, yana
son ya karanci wani abu da ya
gani tattare da ita, ba komai
bane illa damuwa da rashin
samun natsuwa tare da
kwanciyar hankali. A hankali ya
fara magana "Firdausi ko?"
Kanta na kasa, dan ta kasa
hada ido dashi, wani irin
Kwarjini yake mata, cikin siriyar
murya tace "yes sir" yace "yu
did a good job today, kin fita
kunyar makarantar ki, malaman
ki tare da dalibai yan uwanki, I
know they 're proud of yu" har
cikin zuciyan ta abin yai mata
dadi, dan har sai da wani
murmushi ya bayyana akan
fuskar ta!

BA’A SHAN
ZUMA… 20
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Ya cigaba da cewa "well,
dalilin kiran ki ba komai bane
illa ina son na san ko ke
wacece, ba don komai ba sai
don mugun kama da kike yi da
ummi na, maganan ki, nd a lot
of things" cikin tashin hankali
ta dago fuskar ta, caraf suka
hada ido, dan dama ita din
yake kallo, sai da ta tattara
natsuwar ta, sannan ta fara
magana "ni kam ba kowa bace,
ba kuma komai bace, asali ma,
marainiya ce ni, ina zaune da
goggo na, wadda ta kasance
kanwar mahaifina, iyayena sun
rasu tun ina shekara 5 a
dunia" tana kai wa nan, taja
bakin ta tayi shiru. Shiru na
yan dakiku ya ratsa wurin,
sannan ya saki ajiyar zuciya,
yace "ehnn ina sauraren ki" ba
tare da ta kalle shi ba, tace
"shikenan ai" ya kura wa
kyakkaywar fuskar ta ido,
tabbas ya ga damuwa a tattare
da yarinyar, amma ya rasa
dalilin da yasa a lokaci daya
yaji ta shiga ran shi, ya rasa
dalilin da yasa yaji yana son ya
san wani abu dangane da
damuwar da ya gani bayyane a
saman fuskar ta. Ya dan gyara
zaman shi, sannan yace "a
matsayina na psychologist, na
karanci wani abu a tare da ke,
wanda baki son ki sanar dani"
ta dan firgita, sannan tace
"bakomai fa" ya shafi tarin
sumar da take saman kanshi,
sannan yace "alright then, zaki
iya tafia" bata kai ga mikewa
ba principal ya dawo office din,
a haka tayi musu sallama, tasa
kai ta fita ta bar office din.
Hally ta gani zaune a gefe ta
karasa kusa da ita, tace "muje
ko" ta mike suka jera,ta fara
tambayar "me ya faru ne
Deedo?" Ba tare da ta boye
mata komai ba, ta fada mata
abinda ya faru tsakanin ta da
wanda taji an kira da Dr.
NAWAP KHAMIS..

BA’A SHAN
ZUMA… 21, 22
& 23
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
A haka suka kawo layin su
Deedo, inda suka yi sallama
kowa ya kama gaban shi. Tana
shiga gidan da murnar ta,
sallama tayi, a lokacin goggo
tana kofar daki, ta dago ta
watsa mata wani kallo mai
tattare da tsana da tsangwama,
da sauri ta karasa gaban ta,
tana "sannu goggo" ta dago
fuskar ta a murtuke tace "uban
mi zanyi da sannunki? Shine
sai yanzu zaki dawo mun gidan
nan ko? Kina can kina yawon
naki na iskanci da kika saba"
tayi kasa da kanta, tace "kiyi
hakuri goggo, wlh a makaranta
ne aka tsaida mu" tayi kwafa,
sannan tace "uban miyye nan a
hannun ki?" Tace "kyautar da
aka bamu ce" goggo ta warce,
ta farka wrapping sheet din,
sannan ta fara fito da text
books da math set, da note
books da sabbin uniform gal,
da sauran tarkace dai na
students, ta kwashi uniform
din tare da text books ta watsa
mata, tace "wannan kadai zaki
samu shegiya, wannan sauran
kuma duk su shehu zan ba su"
ta tattara ta tura su bayan ta, ta
kara da cewar "wai ke nan a
wannan shegen kan naki har
wani kallon mai kokari suke
maki, tashi wuce ki bani wuri,
kin zura mun ido kamar na
mujiya, kuma ga kayana nan, ki
tattare su ki wanke tass" ta
kwashe yan kayan da ta bata,
ta shige daki, ita murna ma
take yi, dan bata yi zaton zata
samu wani abu daga cikin
kyautar da aka bata ba.
Dr. NAWAP KHAMIS, matashi
ne mai kimanin shekarun da
basu wuce 28 ba a dunia.
Dogo ne sosai dan har ya dan
rankwafa saboda tsabar
tsawon shi, yana da kirji mai
fadi wanda a kallo daya zaka
ga bayyanannun 6-packs din
shi. Yana da muscles a
damtsen hannun shi,
kasancewar shi masoyin gym
ne na bala'i, yana da doguwar
fuska wadda ke dauke da dara
daran idanu tare da dogon
hancin da ya dace da
kyawawan lips din shi. In fact,
Nawap namiji ne wanda ya
ansa sunan shi namiji, yayi
degree din shi na daya dana
biyu a jami'ar Bayero da ke
garin kano, inda daga bisani ya
wuce England inda ya hada
PhD din shi akan psychology.
Shine da na farko a wurin
mahaifiyar shi haj. Fatima
wadda yake kira da ummi,
mahaifin shi Alh. Khamis
shaharraren dan kasuwa ne a
garin kaduna, wanda Allah yai
mashi rasuwa shekara biyu da
suka gabata, kanwar shi kwaya
daya Hafsat wadda take aure a
garin Abuja. Yanzu haka yana
aiki da federal ministry of
education, wannan ne dalilin
da ya bashi damar zuwa
kauyen su Deedo, kasancewar
su masu inganta ilimin matasa
yan secondary skool.
Chapter 6 · 0% Book details