Sashe 25
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
BA’A SHAN
ZUMA… 76-78
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Kwanakin da tayi tana fita
zuwa makaranta registration
yasa tafara jin kad'aici da bata
fita yau ba, zaune take tana
karyawa da dankali soyayye da
k'wai, wanda ta lafta ketchup
akai, wayanta a hannunta tana
game d'in candy crush,
message ne ya shigo mata,
cikin hanzari ta fita sannan ta
duba, Affan ne ya turo mata
"hey, ya gajiya?, sannan ya
shirin fara lectures?" Tayi
murmushi sannan ta ajiye fork
d'in ta masa reply da "ga
munan, munata shiri"
Message taji ya k'ara shigowa,
da sauri ta d'auka zata duba a
zatonta Affan ne sai kuma taga
sunan Ya Nawap, cikin sanyin
jiki ta bud'e ta karanta "kin
gama registration d'in ko da
saura?" Ta mayar masa da
"nagama Yaya, Allah bada lada"
Murna yake ji da walwala idan
yana musayar txt da ita, don
haka sai yafara tunanin me zai
kara ce mata, don yanzu so
yake ya jata ajiki kasancewar
yasan inda zata je, jami"a ba
gidan wasa da dama bane, kar
wani yaje ya hure mata kunne
duk shukan da yayi wani k'ato
ya girbe, ita kuwa tattara
abincin tayi sannan takai
kitchen ta nufi d'aki ta fara
gyran wardrope d'inta wanda
bata samu tayi ba saboda fita
data keyi kwana biyu.
Affan na k'ok'arin jan
hankalinta wanda itama ta
tattara hankalinta ta mayar
gunsa, k'arshe yaga message
d'in bazai yiwu ba don haka
kawai ya kirata, murmushi tayi
ta jawo earpiece ta saka
sannan ta saka wayan a
aljihun riganta ta cigaba da
gyaran yayin da suke magana.
Shikuwa Nawap ya mata text
yana jira ta mayar masa da
martani yaji shiru, ya fara
tunani me yarinyan nan take yi
tana gida yau kuma babu wani
aiki da takeyi, baya son kiranta
akan message d'in don haka
ya kira Ummi ya fake da
gaisheta yake yi sannan ya
tambaya ina Deedo?, tace "tana
d'aki"
Sallama yai ma Ummi, sannan
ya kira numbanta, sai kuma ya
kashe, sai da ya samo abin
cewa sannan ya kirata, number
busy yaji, domin bata sa
wayanta a call waiting ba balle
ta san yana kira, tuni yaji
gabanshi ya fad'i ganin sai kira
yake yi amma bai shiga ba, har
lokacin wayan take yi, tuni yaji
zuciyarsa ta tokare,
numfashinsa na neman
guduwa gagara zama yayi yana
jan tsaki, a kalla yakai minti
talatin yana kira yana jin busy,
bai san Affan da Deedo sunyi
nisa a tad'insu na duniya ba.
Wanda muka rasa gane shin
soyayya ce ko kuma tsabar
shak'uwa ce?
Deedo da Affan suna cikin
nishad'i domin kuwa wayan da
sukeyi kowanne acikinsu najin
kamar kada su rabu, sai taji
tana Allah Alah afara lectures
ko zasu na had'uwa da Affan
sosai, siffarsa na mata gizo,
tana tunanin halittarsa, duk da
cewa bai manyanta sosai ba,
anma namiji ne wanda ko
wacce mace zata so ya kulata,
don haka har ta gama aikinta,
ta wanke toilet duk suna
wayan, ta kunna ruwan wanka,
sannan ta zauna akan gado,
tanason cemasa zata shiga
wanka tanajin kunya, don haka
kawai sukayi ta tad'in
makaranta yana bata labarin
abubuwan dariya da al'ajabi
dake faruwa acikin makarantan,
Can dai ya dan nisa, yace "bari
naje na karb'i aiki, zan kiraki
anjima" suna sallama ta ajiye
wayan, bata lura da text din
daya shigo ba kai tsaye toilet
ta shiga tafara wanka, tana
shiga taji wayan na kara,
Nawap ne yake kira akalla awa
daya da minti sha biyar suna
waya, jin wayan ta shiga yasa
shi jan numfashi yana jira ta
d'auka ya sauke mata kwandon
masifa, sai kuma ikon Allah
yana ta kira shiru, feedo kuwa
jin kukan wayan ya tsananta
tafara tunanin waye, don dai
ita tasan Affan bazai kira yanzu
ba, toh ko ma waye ya jira ta
ta gama kammalawa.
Sai da ta gama wankanta tafito,
har lokacin wayan na kara, ta
duba kawai ta d'auka gabanta
na fad'i ganin sunan Yaa
Nawap, a hankali ta saka a
kunnenta sannan tace "ina
wuni Yaya?" "Dawa kike waya
for more than one hour?" Shiru
tayi bata bashi amsa ba, wanda
hakan ya kara kular dashi "Me
kike so ki mayar da kanki?,
daga fara makaranta tun kafin
muje ko ina har kin fara tara
maza?, ba na hanaki ba?, ko so
kike na kwace wayan?, ki
kiyayeni fa!, ki gaya mun da wa
kike waya kuma!" Duk fad'an
da yake yi bata bashi amsa ba,
sai ma kukan da ta saka, a
duniya babu abunda ya tsana ji
kaman kukanta, a take ya rud'e
sannan yace "Ji fa, fisabililah
daga miki magana kin fara min
kuka ke kinfi kowa yawan
ruwan hawaye ne?"
Bata amsa shi ba sannan ba ta
daina kukan ba, zuciyanta na
kunci, ta rasa meke mata dad'i,
kashe wayan tayi alokacin ta
ga missed call 42, ga
messages guda hudu, duk
nashi ne, sai taji wani iri ta
tabbata yayi ta kirane yaji shiru
yasa yake fad'a, batason taji
yana mita ko fad'a , don haka
saida ta ida hawayenta a
lokacin text d'in affan ya shigo
"Yh, how far r u done?" Saitayi
shiru tana tunani, ta tabbata ita
bata ce masa zata yi wani abu
ba, shi yace bari yayi abu
anma sai gashi yana
tambayanta, murmushi tayi
ganin cewa ya gane akwai
uzuri agabanta har ya saurara
mata, tuni ta manta da batun
Nawap, yayinda shikuwa gogan
yana zaune yana jira yaga text
d'in ban hakuri,
Ba tare da bata lokaci ba ta yi
reply wa Affan da "ae am
done" Aikuwa sai gashi ya kira,
aka cigaba daga inda aka
tsaya, Nawap ganin bata turo
masa komai ba yasa yayi
tunanin ko kuka take har
lokacin don haka sai ya kara
kiran numban don yaji ko
lafiya, number busy da ya ji
yasa ya daki teburin dake
gabanshi, sannan yaja wani
mugun tsaki! Wanda muma sai
da muka tsorata..
Wayansu suke hankalinsu
kwance, domin kuwa yadda
Affan ke fada mata kalamai
masu kwantar da hankalin mai
sauraro yasa ta manta da
batun fad'an da Nawap ke
mata kwata kwata, cikin wani
irin salo na karya murya yace
"Feedo na yaushe zan ganki
dan Allah?" Wani irin abu taji
har cikin zuciyarta, dak'yar ta
gyara murya tace "ni ba sunana
Feedo ba, ka kira ni Deedo
yadda kowa ke kira na" kaman
yana gabanta ya mak'ale
kafad'anshi yace "no, ni ba
kowa bane so zan na kiranki
Feedo cuz ya fi mun dadi"
Bata k'ara cewa komai ba sai
wani farin ciki da take ji yana
ziyartanta, haka suka yini suna
wayan nan inda ta b'angaren
Nawap kuwa, fashewa ne
kawai bai yi ba saboda bak'in
ciki. Ana gab da kiran azahar
sannan Affan yayi mata
sallama, ba wai dan sun gaji
da juna ba, kawai dan ya bata
daman aiwatar da abubuwan
da suke gabanta hankali
kwance. Suna gama wayan ta
d'an mik'e rigingine a gado
sannan ta rungume wayan a
k'irjinta, ta rasa me sa take
jinshi har cikin jininta, saboda
ita dai bata tab'a shiga irin
yanayin nan ba.
Mik'ewa tayi da niyyar ta d'oro
alwalla, amma taga wayanta
yana blinking alaman tana da
sak'o murmushi ta saki, inda
cikin zuciyarta tace "Affan baya
gajiya shi kam" toilet din ta
zarce tayi alwalanta ta fito ta
tada sallah ta gama, ta shirya
tsab, sannan ta dauka wayan
ta sauka k'asa. Dinning ta
wuce ta zuba abinci, sai da ta
fara cin abincin sannan ta
duba wayan, gabanta ne ya
fad'i dam! Kasancewar karo da
tayi da text din Ya Nawap
kamar haka "are yu insane? Kin
maida ni k'aramin yaro ko? Shi
yasa ina maki magana kika
share kika cigaba da wayanki.
Ki shiga hankalinki tun kafin
na iso garin nan"
Ture plate din tayi a gefe ta
dafe kanta, "wai shi meye
nashi da yake neman matsa
ma rayuwata?"
ZUMA… 76-78
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Kwanakin da tayi tana fita
zuwa makaranta registration
yasa tafara jin kad'aici da bata
fita yau ba, zaune take tana
karyawa da dankali soyayye da
k'wai, wanda ta lafta ketchup
akai, wayanta a hannunta tana
game d'in candy crush,
message ne ya shigo mata,
cikin hanzari ta fita sannan ta
duba, Affan ne ya turo mata
"hey, ya gajiya?, sannan ya
shirin fara lectures?" Tayi
murmushi sannan ta ajiye fork
d'in ta masa reply da "ga
munan, munata shiri"
Message taji ya k'ara shigowa,
da sauri ta d'auka zata duba a
zatonta Affan ne sai kuma taga
sunan Ya Nawap, cikin sanyin
jiki ta bud'e ta karanta "kin
gama registration d'in ko da
saura?" Ta mayar masa da
"nagama Yaya, Allah bada lada"
Murna yake ji da walwala idan
yana musayar txt da ita, don
haka sai yafara tunanin me zai
kara ce mata, don yanzu so
yake ya jata ajiki kasancewar
yasan inda zata je, jami"a ba
gidan wasa da dama bane, kar
wani yaje ya hure mata kunne
duk shukan da yayi wani k'ato
ya girbe, ita kuwa tattara
abincin tayi sannan takai
kitchen ta nufi d'aki ta fara
gyran wardrope d'inta wanda
bata samu tayi ba saboda fita
data keyi kwana biyu.
Affan na k'ok'arin jan
hankalinta wanda itama ta
tattara hankalinta ta mayar
gunsa, k'arshe yaga message
d'in bazai yiwu ba don haka
kawai ya kirata, murmushi tayi
ta jawo earpiece ta saka
sannan ta saka wayan a
aljihun riganta ta cigaba da
gyaran yayin da suke magana.
Shikuwa Nawap ya mata text
yana jira ta mayar masa da
martani yaji shiru, ya fara
tunani me yarinyan nan take yi
tana gida yau kuma babu wani
aiki da takeyi, baya son kiranta
akan message d'in don haka
ya kira Ummi ya fake da
gaisheta yake yi sannan ya
tambaya ina Deedo?, tace "tana
d'aki"
Sallama yai ma Ummi, sannan
ya kira numbanta, sai kuma ya
kashe, sai da ya samo abin
cewa sannan ya kirata, number
busy yaji, domin bata sa
wayanta a call waiting ba balle
ta san yana kira, tuni yaji
gabanshi ya fad'i ganin sai kira
yake yi amma bai shiga ba, har
lokacin wayan take yi, tuni yaji
zuciyarsa ta tokare,
numfashinsa na neman
guduwa gagara zama yayi yana
jan tsaki, a kalla yakai minti
talatin yana kira yana jin busy,
bai san Affan da Deedo sunyi
nisa a tad'insu na duniya ba.
Wanda muka rasa gane shin
soyayya ce ko kuma tsabar
shak'uwa ce?
Deedo da Affan suna cikin
nishad'i domin kuwa wayan da
sukeyi kowanne acikinsu najin
kamar kada su rabu, sai taji
tana Allah Alah afara lectures
ko zasu na had'uwa da Affan
sosai, siffarsa na mata gizo,
tana tunanin halittarsa, duk da
cewa bai manyanta sosai ba,
anma namiji ne wanda ko
wacce mace zata so ya kulata,
don haka har ta gama aikinta,
ta wanke toilet duk suna
wayan, ta kunna ruwan wanka,
sannan ta zauna akan gado,
tanason cemasa zata shiga
wanka tanajin kunya, don haka
kawai sukayi ta tad'in
makaranta yana bata labarin
abubuwan dariya da al'ajabi
dake faruwa acikin makarantan,
Can dai ya dan nisa, yace "bari
naje na karb'i aiki, zan kiraki
anjima" suna sallama ta ajiye
wayan, bata lura da text din
daya shigo ba kai tsaye toilet
ta shiga tafara wanka, tana
shiga taji wayan na kara,
Nawap ne yake kira akalla awa
daya da minti sha biyar suna
waya, jin wayan ta shiga yasa
shi jan numfashi yana jira ta
d'auka ya sauke mata kwandon
masifa, sai kuma ikon Allah
yana ta kira shiru, feedo kuwa
jin kukan wayan ya tsananta
tafara tunanin waye, don dai
ita tasan Affan bazai kira yanzu
ba, toh ko ma waye ya jira ta
ta gama kammalawa.
Sai da ta gama wankanta tafito,
har lokacin wayan na kara, ta
duba kawai ta d'auka gabanta
na fad'i ganin sunan Yaa
Nawap, a hankali ta saka a
kunnenta sannan tace "ina
wuni Yaya?" "Dawa kike waya
for more than one hour?" Shiru
tayi bata bashi amsa ba, wanda
hakan ya kara kular dashi "Me
kike so ki mayar da kanki?,
daga fara makaranta tun kafin
muje ko ina har kin fara tara
maza?, ba na hanaki ba?, ko so
kike na kwace wayan?, ki
kiyayeni fa!, ki gaya mun da wa
kike waya kuma!" Duk fad'an
da yake yi bata bashi amsa ba,
sai ma kukan da ta saka, a
duniya babu abunda ya tsana ji
kaman kukanta, a take ya rud'e
sannan yace "Ji fa, fisabililah
daga miki magana kin fara min
kuka ke kinfi kowa yawan
ruwan hawaye ne?"
Bata amsa shi ba sannan ba ta
daina kukan ba, zuciyanta na
kunci, ta rasa meke mata dad'i,
kashe wayan tayi alokacin ta
ga missed call 42, ga
messages guda hudu, duk
nashi ne, sai taji wani iri ta
tabbata yayi ta kirane yaji shiru
yasa yake fad'a, batason taji
yana mita ko fad'a , don haka
saida ta ida hawayenta a
lokacin text d'in affan ya shigo
"Yh, how far r u done?" Saitayi
shiru tana tunani, ta tabbata ita
bata ce masa zata yi wani abu
ba, shi yace bari yayi abu
anma sai gashi yana
tambayanta, murmushi tayi
ganin cewa ya gane akwai
uzuri agabanta har ya saurara
mata, tuni ta manta da batun
Nawap, yayinda shikuwa gogan
yana zaune yana jira yaga text
d'in ban hakuri,
Ba tare da bata lokaci ba ta yi
reply wa Affan da "ae am
done" Aikuwa sai gashi ya kira,
aka cigaba daga inda aka
tsaya, Nawap ganin bata turo
masa komai ba yasa yayi
tunanin ko kuka take har
lokacin don haka sai ya kara
kiran numban don yaji ko
lafiya, number busy da ya ji
yasa ya daki teburin dake
gabanshi, sannan yaja wani
mugun tsaki! Wanda muma sai
da muka tsorata..
Wayansu suke hankalinsu
kwance, domin kuwa yadda
Affan ke fada mata kalamai
masu kwantar da hankalin mai
sauraro yasa ta manta da
batun fad'an da Nawap ke
mata kwata kwata, cikin wani
irin salo na karya murya yace
"Feedo na yaushe zan ganki
dan Allah?" Wani irin abu taji
har cikin zuciyarta, dak'yar ta
gyara murya tace "ni ba sunana
Feedo ba, ka kira ni Deedo
yadda kowa ke kira na" kaman
yana gabanta ya mak'ale
kafad'anshi yace "no, ni ba
kowa bane so zan na kiranki
Feedo cuz ya fi mun dadi"
Bata k'ara cewa komai ba sai
wani farin ciki da take ji yana
ziyartanta, haka suka yini suna
wayan nan inda ta b'angaren
Nawap kuwa, fashewa ne
kawai bai yi ba saboda bak'in
ciki. Ana gab da kiran azahar
sannan Affan yayi mata
sallama, ba wai dan sun gaji
da juna ba, kawai dan ya bata
daman aiwatar da abubuwan
da suke gabanta hankali
kwance. Suna gama wayan ta
d'an mik'e rigingine a gado
sannan ta rungume wayan a
k'irjinta, ta rasa me sa take
jinshi har cikin jininta, saboda
ita dai bata tab'a shiga irin
yanayin nan ba.
Mik'ewa tayi da niyyar ta d'oro
alwalla, amma taga wayanta
yana blinking alaman tana da
sak'o murmushi ta saki, inda
cikin zuciyarta tace "Affan baya
gajiya shi kam" toilet din ta
zarce tayi alwalanta ta fito ta
tada sallah ta gama, ta shirya
tsab, sannan ta dauka wayan
ta sauka k'asa. Dinning ta
wuce ta zuba abinci, sai da ta
fara cin abincin sannan ta
duba wayan, gabanta ne ya
fad'i dam! Kasancewar karo da
tayi da text din Ya Nawap
kamar haka "are yu insane? Kin
maida ni k'aramin yaro ko? Shi
yasa ina maki magana kika
share kika cigaba da wayanki.
Ki shiga hankalinki tun kafin
na iso garin nan"
Ture plate din tayi a gefe ta
dafe kanta, "wai shi meye
nashi da yake neman matsa
ma rayuwata?"