Sashe 8
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Yau Allah ya taimaka ta kiran
sallar farko a kan kunnen ta
dan haka tayi zumbur ta mike,
tashin ta keda wuya, goggo ta
shigo da robar ruwan ta, tana
haska fitila ta ganta a tsaye,
tace "la'ananniya, da kar ki
tashi mana" tayi kwafa tace,
"kin wuce kin wanke kayan
fitsarin can na shehu ko sai
nasa kafa na hanbare ki?" Sum
sum Deedo ta fito tana rawar
sanyi, kayan fitsarin ta kwashe
ta wanke, sannan ta doro
alwala tazo ta gabatar da sallar
asuba, sannan ta dauki bahon
nan, ta wuce borehole.
Bayan ta dawo tayi duk wani
aiki da tasan nata ne, ta gama
ta jawo uniform dinta, ta saka
sannan ta fito ta karasa kofar
dakin goggo. Ita daya ce zaune
a bakin gado, dan su Hadiza
sun dade da tafia makaranta.
Tace "goggo zan tafi" ta watsa
mata harara tace "na rike miki
kafa ne? Ko wata tsiyar zan
miki ne? Eyee?" Ta girgiza
kanta, sannan ta mike ta fito
daga dakin ta nufi makarantar.
Tana isa har an fara exam,
malamin ya kalle ta kaman
wadda aka koro, yace "Firdausi
Kabeer" dam taji gaban ta ya
fadi, ta tsaya cak a inda take,
yace "mei sa tunda aka fara
exam kullun sai kinzo late?" Ta
rasa abin cewa, sai can ta tuna
da goggo ta fasa mata baki
jiya wurin dukan ta har ma ya
kunbura, tayi saurin cewa "I'm
sorry sir, na taho ne na fadi a
hanya saida na tsaya chemist
na ansa magani" ya kare mata
kallo, tabbas ga alama nan a
tattare da ita, dan haka ya bata
question paper yace ta wuce ta
zauna, ta ansa da sauri ta
wuce seat dinta ta zauna.
Nawap kasa bacci yayi a daren
jiya, yana tunanin ta ena zai
biyo ma mace mai mugun hali
da rashin imani irin goggo; shi
dai yayi alkawarin taimakon
yarinyar nan no matter what;
amma ya rasa ta wane hanya
zai bi dan ya kubutar da ita
daga hannun azzalumar matar
nan. Tunani ya fara yi ko court
zai mika ta, sai kuma wata
zuciyar tace "a matsayin ka na
wa? In kaje gaban alkali kace
me?" Yaja tsaki, ya watsar da
wannan tunanin can kuma
wata dabarar ta fado mashi,
murmushi ya saki wanda ya
kara mashi kwarjini, da sauri
ya canja akalar motar shi yabi
wani titi, ba tare da yasan ko
ina cikin garin Bauchi ba, haka
ya bi main road na cikin garin,
nan ya samu wani katon mall,
ya karasa yayi parking ya fito
ya shige ciki. Duk wani abu da
dan adam zai bukata akwai shi,
haka ya zage yayi kyakkyawan
shopping na dangin kayan
abinci masu uban yawa,
tarkacen man shafawa,
sabulun wanka dana wanki, ya
koma bangaren kayan sawa
nan ma ya kwasa son ran shi,
har da kayan yara maza ya
kwaso, akai mashi total kudi
wurin 150, 000, credit card din
shi ya ciro ya basu suka cire,
sannan aka kwashi kayan aka
sa mashi a pickup ta shopping
mall din, dan motar shi baza ta
iya daukar lodin ba, ya shiga
yana gaba masu motan na bin
shi har cikin garin Ningi.
A kofar gidan Hajia goggo
suka tsaya, ya kira wasu
almajirai suka taimaka ma
masu motan suka shiga da
kayan ciki. Goggo dake kofar
daki tana sakacen hakori taga
mutane da kaya niki niki, ta yi
zumbur ta mike tace "kai
malam daga ina wannan
kayan?" Wani cikin su yace
"wani ne yace mu shigo dasu
yana nan waje" tana tambayar
wanene amma bai bi ta kanta
ba, suka juya suka fita. Saida
aka gama shigo da kayan tsab,
sannan Nawap ya shigo ya
tsaya bakin zaure yayi sallama,
goggo data kagara taga wanda
ya kawo wannan kantin guda
(inji ta tace wannan ai kanti ne
guda ya kwaso) tayi saurin
cewa "shigo mana" ganin
tsayayyen namiji, jarumi,
matashi, dan boko, wanda ya ji
hutu, ya kuma ji bugun A.C,
mai asalin zati da kwar jini!
Yasa goggo tayi saurin ja da
baya kamar wadda tayi karya,
ta samu gefe ta rakube, bakin
ta na rawa tace "yaro daga
ena?" Yanayin da goggo ta
shiga ya bala'in bama Nawap
daria; haka dai ya gintse, yace
"bari mu gaisa mana goggo
ta"..
sallar farko a kan kunnen ta
dan haka tayi zumbur ta mike,
tashin ta keda wuya, goggo ta
shigo da robar ruwan ta, tana
haska fitila ta ganta a tsaye,
tace "la'ananniya, da kar ki
tashi mana" tayi kwafa tace,
"kin wuce kin wanke kayan
fitsarin can na shehu ko sai
nasa kafa na hanbare ki?" Sum
sum Deedo ta fito tana rawar
sanyi, kayan fitsarin ta kwashe
ta wanke, sannan ta doro
alwala tazo ta gabatar da sallar
asuba, sannan ta dauki bahon
nan, ta wuce borehole.
Bayan ta dawo tayi duk wani
aiki da tasan nata ne, ta gama
ta jawo uniform dinta, ta saka
sannan ta fito ta karasa kofar
dakin goggo. Ita daya ce zaune
a bakin gado, dan su Hadiza
sun dade da tafia makaranta.
Tace "goggo zan tafi" ta watsa
mata harara tace "na rike miki
kafa ne? Ko wata tsiyar zan
miki ne? Eyee?" Ta girgiza
kanta, sannan ta mike ta fito
daga dakin ta nufi makarantar.
Tana isa har an fara exam,
malamin ya kalle ta kaman
wadda aka koro, yace "Firdausi
Kabeer" dam taji gaban ta ya
fadi, ta tsaya cak a inda take,
yace "mei sa tunda aka fara
exam kullun sai kinzo late?" Ta
rasa abin cewa, sai can ta tuna
da goggo ta fasa mata baki
jiya wurin dukan ta har ma ya
kunbura, tayi saurin cewa "I'm
sorry sir, na taho ne na fadi a
hanya saida na tsaya chemist
na ansa magani" ya kare mata
kallo, tabbas ga alama nan a
tattare da ita, dan haka ya bata
question paper yace ta wuce ta
zauna, ta ansa da sauri ta
wuce seat dinta ta zauna.
Nawap kasa bacci yayi a daren
jiya, yana tunanin ta ena zai
biyo ma mace mai mugun hali
da rashin imani irin goggo; shi
dai yayi alkawarin taimakon
yarinyar nan no matter what;
amma ya rasa ta wane hanya
zai bi dan ya kubutar da ita
daga hannun azzalumar matar
nan. Tunani ya fara yi ko court
zai mika ta, sai kuma wata
zuciyar tace "a matsayin ka na
wa? In kaje gaban alkali kace
me?" Yaja tsaki, ya watsar da
wannan tunanin can kuma
wata dabarar ta fado mashi,
murmushi ya saki wanda ya
kara mashi kwarjini, da sauri
ya canja akalar motar shi yabi
wani titi, ba tare da yasan ko
ina cikin garin Bauchi ba, haka
ya bi main road na cikin garin,
nan ya samu wani katon mall,
ya karasa yayi parking ya fito
ya shige ciki. Duk wani abu da
dan adam zai bukata akwai shi,
haka ya zage yayi kyakkyawan
shopping na dangin kayan
abinci masu uban yawa,
tarkacen man shafawa,
sabulun wanka dana wanki, ya
koma bangaren kayan sawa
nan ma ya kwasa son ran shi,
har da kayan yara maza ya
kwaso, akai mashi total kudi
wurin 150, 000, credit card din
shi ya ciro ya basu suka cire,
sannan aka kwashi kayan aka
sa mashi a pickup ta shopping
mall din, dan motar shi baza ta
iya daukar lodin ba, ya shiga
yana gaba masu motan na bin
shi har cikin garin Ningi.
A kofar gidan Hajia goggo
suka tsaya, ya kira wasu
almajirai suka taimaka ma
masu motan suka shiga da
kayan ciki. Goggo dake kofar
daki tana sakacen hakori taga
mutane da kaya niki niki, ta yi
zumbur ta mike tace "kai
malam daga ina wannan
kayan?" Wani cikin su yace
"wani ne yace mu shigo dasu
yana nan waje" tana tambayar
wanene amma bai bi ta kanta
ba, suka juya suka fita. Saida
aka gama shigo da kayan tsab,
sannan Nawap ya shigo ya
tsaya bakin zaure yayi sallama,
goggo data kagara taga wanda
ya kawo wannan kantin guda
(inji ta tace wannan ai kanti ne
guda ya kwaso) tayi saurin
cewa "shigo mana" ganin
tsayayyen namiji, jarumi,
matashi, dan boko, wanda ya ji
hutu, ya kuma ji bugun A.C,
mai asalin zati da kwar jini!
Yasa goggo tayi saurin ja da
baya kamar wadda tayi karya,
ta samu gefe ta rakube, bakin
ta na rawa tace "yaro daga
ena?" Yanayin da goggo ta
shiga ya bala'in bama Nawap
daria; haka dai ya gintse, yace
"bari mu gaisa mana goggo
ta"..