Sashe 7
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BA'A
SHAN ZUMA… 2⃣2⃣
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Tun ranan da Nawap ya bar
kauyen su Deedo bashi da abin
tunani wanda ya wuce ta,
babban tashin hankalin shi
shine damuwar da ya gani
shimfIda saman fuskar ta,
gashi ya rasa gane menene
ainahin dalilin damuwar ta a
matsayin ta na yarinyar da
duka duka bata wuce shekara
15 ba a dunia, idan zai iya
tunawa principal din su yace
suna 3rd term ne yanzu a ss2.
Babu abinda ke mashi yawo a
kan shi irin kalaman principal
na karshe da yace "Deedo ta
kasance yarinya hazika wadda
zan iya cewa babu kamar ta
kaf cikin makarantar nan, sai
dai kuma yarinya ce wadda
take bukatar taimako cikin
gaggawa!" Dam! Gaban shi ya
Kara bugawa, to wane irin
taimako ne take bukata? Shine
abinda bai tsaya ya samu
cikakken labari ba. Mikewa
yayi daga kan kujeran da yake
zaune, ya tattara laptop din
dake saman cinyan shi ya dora
kan center table, sannan ya
fara zagaya palon a hankali.
Tunani ya fara yi shin me yasa
ya damu da yarinyar bayan
kuma ya kan hadu da cases
sosai irin nata a yawancin
makarantun da suke zuwa, a
fili ya furta "nata is different! I
saw the sorrow in ha, she's
desperately in need of my
help!" Ya sa hannu ya ciro
wayan shi da ke ta faman
ringing cikin aljihu, ya zaro
wayan ya kaima screen din
kallo, lokaci daya yayi wurgi da
ita saman kujera har ta katse
bai daga ba. Aka sake kiran
wayan, a karo na biyu shima
kaman ba zai dauka ba, can
dai ya daga cikin muryar nan
tashi mai kwantar da hankali,
yace "Aysha ya akayi ne?" Ba
tare da mun jiyo ansar da aka
bashi ba, yace "I'm kinda busy
yanzu gaskia, May be I'll call
back later" bai jira ansar ta ba
ya katse wayar yaja tsaki, tare
da komawa kan kujeran ya
lumshe idon shi, Deedo ya
gani cikin kodaddun uniform
dinta, fuskar nan ta ta cikin
yanayi na damuwa da bukatar
tallafin gaggawa, firgit ya bude
idon, amma bai ganta ba,
hakan ya sa ya cika bakin shi
da iska sannan ya fitar, yace
"I'll come 4 yu Deedo nd I
promise I'll help yu" ya mike ya
shige bathroom ya sakan ma
kanshi shower…
Katon bahon ruwan ta, ta
doro a kai tana ta bunguza
sauri kasancewar maghriba ta
gabato, kayan jikin ta duk sun
jike sai rawar sanyi take yi,
kafar nan ta ta firi firi kaman
tayi birgima cikin kasa, shehu
ne tare da wasu yara suke
binta a baya suna mata daria,
bata ko damu da su ba, dan ta
san idan ta tsaya yau kashin ta
ya bushe wurin goggo. Hango
shi tayi rungume da hannayen
shi, ya zuba mata idanu kamar
mai nazarin wani abu a tattare
da ita. Kanshin turaren shi da
ta shako daga inda take shi ya
tabbatar mata da abin da take
tunani! Cikin jin kunyar yanayin
da take ciki tazo, ta raba ta
gefen shi zata wuce ba tare da
ta sake kallon inda yake ba,
bai tanka mata ba, ta shige
cikin gidan da saurin ta dan
har an kwalla kiran sallah.
Shehu ne ya shigo da sauri
yana kwala wa goggo kira, ta
fito daga daki zanin ta a
hannu, tace "Shehu na Allah,
yau kuma da waccen ka
shigo?" Yace "wani mai mota
ne wai a kira mai Deedo" ta
zaro ido tace "mai mota da
neman Deedo? Kai shehu ko
dai dijangala yace?" Yace "wlh
Deedo yace, har ma yace wai
wadda ta shigo yanzu" goggo
ta rafka salati tace "na shiga
ukku, ubanwa kuma kika jawo?
Wlh in masifa ce yau a kanki
zata kare, dan ni dai ina zaman
zama na baki isa ki jawo mun
bala'i ba" ta dafe kanta tace
"oh ni Batula! Wannan
tsintacciyar mage na neman
jefa ni cikin masifun ta" ta
damko kunnen ta, ta wurga ta,
tace "wuce kije ki san yadda
zakiyi da bala'in da kika
tattago, idan ma tafiya zasuyi
dake wlh ko kofar zaure bazan
je ba, tunda ban san sadda
kika je yawon iskancin ki ba
har kika jawo bala'in" Deedo
tasa kara, tace "wlh goggo
banje wani yawon iskanci ba,
wlh ban ja kowa ba" goggo ta
hankada ta, tace "ki wuce ki
fita wlh jar ki ja tsinannun su
shigo mun cikin gida, dan wlh
duk wanda ya shigo sai na
fasa mai kai da tabarya" Deedo
ta share yan hawayen ta, taja
lamusassun silifas dinta da
suka ji wahalar dunia ta bi
hanyar zauren zata fita, shehu
kuma ya sa ihu yace "bari muje
muga irin dukan da za a
nakadawa shegiya, dama su
tafi da ita mu huta" goggo tace
"ka tsaya daga bakin zaure dai,
dan kar su hada mun da dakai"
bai bi ta kanta ba ya juya da
gudu ya fita kofar gidan.
BA’A SHAN
ZUMA… 24, 25
& 26
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Koda ta fita baya kofar gidan,
sai dai motan shi kawai, har ta
juya zata koma ciki ta jiyo ana
kwala mata kira, waigowa tayi,
ta hango shi yana tahowa, da
alama daga masallaci ya fito.
Da sallama ya iso, ita kuma
tana tsaye tana matse kwallan
da suka taran mata, kallon ta
yake cike da tausayin rawar
sanyin da take yi, gata dai
yarinya karama amma alamun
damuwar da take tattare dasu
sun bayyana karara akan
fuskar ta, ba tare da yace
komai ba. Dukawa tayi har
kasa sannan tace "ina wuni" ya
ansa a taqaice, sannan yace
"kin gane ni kuwa?" Ta daga
kai alaman eh, ya gyara
tsayuwar shi, sannan yace "na
tambaye ki labarin ki, amma
baki fada mun komai, a yanzu
kam, ba sai kince dani komai
ba, domin yanayi da kike ciki
ya sanar dani irin matsalar da
kike fuskan ta a gidan nan" ta
dago jajayen idanun ta da suka
rine da kuka, tace "ni bana tare
da matsalan komai" kallon ta
yake yana nazarin yadda tayi
maganar, murmushi yayi, ya
juyar da kanshi ya ce "well,
tunda baza ki fada mun
matsalar ki ba, bara na shiga
gidan sai inji dalilin da yasa
kike daukan wannan katon
bahon na ruwa a kanki, a
matsayin ki na yarinya mai
karancin shekaru" ya sa kanshi
alamar zai shiga zauren, shehu
na ganin ya nufo inda yake ya
tashi ya runtuma da gudu cikin
gidan, itama tayi sauri tasha
gaban shi tace "kayi mun rai
dan Allah, ba dan ni ba, yau
muddin kaje ma goggo da
maganar nan wlh sai ta kusan
kashe ni" murmusawa yayi,
sannan yace "zaki fada man ko
ke wacece ko kuwa?" Ta
girgiza kanta, "zan fada maka"
ya ja da baya ya jingine jikin
kofan zauren, yace "ina
sauraren ki" ba tare da bata
lokaci ba Deedo ta warware
mashi komai, ta fada mashi
duk halin da take ciki a gidan
goggo, hatta da mutuwar mal.
Ilu bata boye ma Nawap ba, ji
yayi kafafun shi na neman
kasa daukar shi, bai taba
tunanin mutane marassa imani
irin goggo suna rayuwa ba har
yanzu a doron kasa, ya zata
irin su sun gama karewa tun
zamanin jahiliyya. Tausayin
yarinyar ya kara shigar shi, ga
wani irin kuka da take yi marar
sauti, kallon ta yake a matsayin
tilon kanwar shi Hafsat, har
yana imagining idan ita ce
wane irin mataki zai dauka.
Kallon ta yayi, yace "kukan nan
ya isa, ki shiga gida kinji, zan
karasa cikin bauchi na kwana,
zuwa gobe zan dawo in sha
Allah" ta mike jiki ba kwari ta
shige ciki, shi kuma ya shiga
motan shi yai mata key ya
kama gaban shi.
Tana shiga ta tarar goggo da
Hadiza da shehu sun jera sun
zuba ma kofar ido suna jiran
suga mei zai faru, damko ta
goggo tayi tace "uban wanene
wancan?" Deedo tasa kara tace
"wani ne" goggo tace "wani
wa?" Ta fara kame kame dan
bata san ya za tai ma goggo
bayani ba, ta daka mata tsawa
tace "baza ki fada ba?" Tace
"daga makarantan mu ne"
goggo tace "naga alamar yau
yan iskan ne a kanki, yanzu
zanyi maganin ki idan baza kiyi
magana ba" cikin tsoro da
fargaba ta fada ma goggo
yadda ta san Nawap, ta kara da
cewar "yazo garin ne shine ya
biyo ta nan" goggo ta sa salati,
tace "ke Deedo ki fita a ido na
wlh, yanzu ke yawon iskancin
naki ya kai har da yan birni
kike yi? Yau zaki gaya wa yan
garin ku" ta damki yarinyar nan
ta fara bugu, Hadiza ma ta
mike ta debo ruwa a randa ta
watsa mata, suka ci gaba da
jibgar ta, shehu kam sai tsalleh
yake yana jin dadi, dan duk
dunia ba abinda ya ke so irin
yaga goggo na kwalfar Deedo,
saida sukai mata liiis,sannan
suka shige daki suka barta a
wurin. Dakyar ta lallaba ta
shige dan akurkin dakin ta,
kuka take yi sosai, ita kanta
tausayin kanta take yi, wannan
azaba ta ishe ta, neman hanyar
da zata kubutar da kanta kawai
take yi, ta lallaba tayi alwala
tazo ta fara sallah ta gama, ta
jawo littafin ta Geography
tasha karatu sosai, abinka da
mai sharp brain, dandanan ta
kwashe komai da take bukata,
ga yunwa ta addabe ta, ga
kuma wani mugun bacci da
yake figan ta, nan inda take ta
dan shingida, kafin kace wani
abu tuni bacci yayi gaba da ita,
abin ka da ansha bauta da
rana an gaji.
SHAN ZUMA… 2⃣2⃣
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Tun ranan da Nawap ya bar
kauyen su Deedo bashi da abin
tunani wanda ya wuce ta,
babban tashin hankalin shi
shine damuwar da ya gani
shimfIda saman fuskar ta,
gashi ya rasa gane menene
ainahin dalilin damuwar ta a
matsayin ta na yarinyar da
duka duka bata wuce shekara
15 ba a dunia, idan zai iya
tunawa principal din su yace
suna 3rd term ne yanzu a ss2.
Babu abinda ke mashi yawo a
kan shi irin kalaman principal
na karshe da yace "Deedo ta
kasance yarinya hazika wadda
zan iya cewa babu kamar ta
kaf cikin makarantar nan, sai
dai kuma yarinya ce wadda
take bukatar taimako cikin
gaggawa!" Dam! Gaban shi ya
Kara bugawa, to wane irin
taimako ne take bukata? Shine
abinda bai tsaya ya samu
cikakken labari ba. Mikewa
yayi daga kan kujeran da yake
zaune, ya tattara laptop din
dake saman cinyan shi ya dora
kan center table, sannan ya
fara zagaya palon a hankali.
Tunani ya fara yi shin me yasa
ya damu da yarinyar bayan
kuma ya kan hadu da cases
sosai irin nata a yawancin
makarantun da suke zuwa, a
fili ya furta "nata is different! I
saw the sorrow in ha, she's
desperately in need of my
help!" Ya sa hannu ya ciro
wayan shi da ke ta faman
ringing cikin aljihu, ya zaro
wayan ya kaima screen din
kallo, lokaci daya yayi wurgi da
ita saman kujera har ta katse
bai daga ba. Aka sake kiran
wayan, a karo na biyu shima
kaman ba zai dauka ba, can
dai ya daga cikin muryar nan
tashi mai kwantar da hankali,
yace "Aysha ya akayi ne?" Ba
tare da mun jiyo ansar da aka
bashi ba, yace "I'm kinda busy
yanzu gaskia, May be I'll call
back later" bai jira ansar ta ba
ya katse wayar yaja tsaki, tare
da komawa kan kujeran ya
lumshe idon shi, Deedo ya
gani cikin kodaddun uniform
dinta, fuskar nan ta ta cikin
yanayi na damuwa da bukatar
tallafin gaggawa, firgit ya bude
idon, amma bai ganta ba,
hakan ya sa ya cika bakin shi
da iska sannan ya fitar, yace
"I'll come 4 yu Deedo nd I
promise I'll help yu" ya mike ya
shige bathroom ya sakan ma
kanshi shower…
Katon bahon ruwan ta, ta
doro a kai tana ta bunguza
sauri kasancewar maghriba ta
gabato, kayan jikin ta duk sun
jike sai rawar sanyi take yi,
kafar nan ta ta firi firi kaman
tayi birgima cikin kasa, shehu
ne tare da wasu yara suke
binta a baya suna mata daria,
bata ko damu da su ba, dan ta
san idan ta tsaya yau kashin ta
ya bushe wurin goggo. Hango
shi tayi rungume da hannayen
shi, ya zuba mata idanu kamar
mai nazarin wani abu a tattare
da ita. Kanshin turaren shi da
ta shako daga inda take shi ya
tabbatar mata da abin da take
tunani! Cikin jin kunyar yanayin
da take ciki tazo, ta raba ta
gefen shi zata wuce ba tare da
ta sake kallon inda yake ba,
bai tanka mata ba, ta shige
cikin gidan da saurin ta dan
har an kwalla kiran sallah.
Shehu ne ya shigo da sauri
yana kwala wa goggo kira, ta
fito daga daki zanin ta a
hannu, tace "Shehu na Allah,
yau kuma da waccen ka
shigo?" Yace "wani mai mota
ne wai a kira mai Deedo" ta
zaro ido tace "mai mota da
neman Deedo? Kai shehu ko
dai dijangala yace?" Yace "wlh
Deedo yace, har ma yace wai
wadda ta shigo yanzu" goggo
ta rafka salati tace "na shiga
ukku, ubanwa kuma kika jawo?
Wlh in masifa ce yau a kanki
zata kare, dan ni dai ina zaman
zama na baki isa ki jawo mun
bala'i ba" ta dafe kanta tace
"oh ni Batula! Wannan
tsintacciyar mage na neman
jefa ni cikin masifun ta" ta
damko kunnen ta, ta wurga ta,
tace "wuce kije ki san yadda
zakiyi da bala'in da kika
tattago, idan ma tafiya zasuyi
dake wlh ko kofar zaure bazan
je ba, tunda ban san sadda
kika je yawon iskancin ki ba
har kika jawo bala'in" Deedo
tasa kara, tace "wlh goggo
banje wani yawon iskanci ba,
wlh ban ja kowa ba" goggo ta
hankada ta, tace "ki wuce ki
fita wlh jar ki ja tsinannun su
shigo mun cikin gida, dan wlh
duk wanda ya shigo sai na
fasa mai kai da tabarya" Deedo
ta share yan hawayen ta, taja
lamusassun silifas dinta da
suka ji wahalar dunia ta bi
hanyar zauren zata fita, shehu
kuma ya sa ihu yace "bari muje
muga irin dukan da za a
nakadawa shegiya, dama su
tafi da ita mu huta" goggo tace
"ka tsaya daga bakin zaure dai,
dan kar su hada mun da dakai"
bai bi ta kanta ba ya juya da
gudu ya fita kofar gidan.
BA’A SHAN
ZUMA… 24, 25
& 26
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Koda ta fita baya kofar gidan,
sai dai motan shi kawai, har ta
juya zata koma ciki ta jiyo ana
kwala mata kira, waigowa tayi,
ta hango shi yana tahowa, da
alama daga masallaci ya fito.
Da sallama ya iso, ita kuma
tana tsaye tana matse kwallan
da suka taran mata, kallon ta
yake cike da tausayin rawar
sanyin da take yi, gata dai
yarinya karama amma alamun
damuwar da take tattare dasu
sun bayyana karara akan
fuskar ta, ba tare da yace
komai ba. Dukawa tayi har
kasa sannan tace "ina wuni" ya
ansa a taqaice, sannan yace
"kin gane ni kuwa?" Ta daga
kai alaman eh, ya gyara
tsayuwar shi, sannan yace "na
tambaye ki labarin ki, amma
baki fada mun komai, a yanzu
kam, ba sai kince dani komai
ba, domin yanayi da kike ciki
ya sanar dani irin matsalar da
kike fuskan ta a gidan nan" ta
dago jajayen idanun ta da suka
rine da kuka, tace "ni bana tare
da matsalan komai" kallon ta
yake yana nazarin yadda tayi
maganar, murmushi yayi, ya
juyar da kanshi ya ce "well,
tunda baza ki fada mun
matsalar ki ba, bara na shiga
gidan sai inji dalilin da yasa
kike daukan wannan katon
bahon na ruwa a kanki, a
matsayin ki na yarinya mai
karancin shekaru" ya sa kanshi
alamar zai shiga zauren, shehu
na ganin ya nufo inda yake ya
tashi ya runtuma da gudu cikin
gidan, itama tayi sauri tasha
gaban shi tace "kayi mun rai
dan Allah, ba dan ni ba, yau
muddin kaje ma goggo da
maganar nan wlh sai ta kusan
kashe ni" murmusawa yayi,
sannan yace "zaki fada man ko
ke wacece ko kuwa?" Ta
girgiza kanta, "zan fada maka"
ya ja da baya ya jingine jikin
kofan zauren, yace "ina
sauraren ki" ba tare da bata
lokaci ba Deedo ta warware
mashi komai, ta fada mashi
duk halin da take ciki a gidan
goggo, hatta da mutuwar mal.
Ilu bata boye ma Nawap ba, ji
yayi kafafun shi na neman
kasa daukar shi, bai taba
tunanin mutane marassa imani
irin goggo suna rayuwa ba har
yanzu a doron kasa, ya zata
irin su sun gama karewa tun
zamanin jahiliyya. Tausayin
yarinyar ya kara shigar shi, ga
wani irin kuka da take yi marar
sauti, kallon ta yake a matsayin
tilon kanwar shi Hafsat, har
yana imagining idan ita ce
wane irin mataki zai dauka.
Kallon ta yayi, yace "kukan nan
ya isa, ki shiga gida kinji, zan
karasa cikin bauchi na kwana,
zuwa gobe zan dawo in sha
Allah" ta mike jiki ba kwari ta
shige ciki, shi kuma ya shiga
motan shi yai mata key ya
kama gaban shi.
Tana shiga ta tarar goggo da
Hadiza da shehu sun jera sun
zuba ma kofar ido suna jiran
suga mei zai faru, damko ta
goggo tayi tace "uban wanene
wancan?" Deedo tasa kara tace
"wani ne" goggo tace "wani
wa?" Ta fara kame kame dan
bata san ya za tai ma goggo
bayani ba, ta daka mata tsawa
tace "baza ki fada ba?" Tace
"daga makarantan mu ne"
goggo tace "naga alamar yau
yan iskan ne a kanki, yanzu
zanyi maganin ki idan baza kiyi
magana ba" cikin tsoro da
fargaba ta fada ma goggo
yadda ta san Nawap, ta kara da
cewar "yazo garin ne shine ya
biyo ta nan" goggo ta sa salati,
tace "ke Deedo ki fita a ido na
wlh, yanzu ke yawon iskancin
naki ya kai har da yan birni
kike yi? Yau zaki gaya wa yan
garin ku" ta damki yarinyar nan
ta fara bugu, Hadiza ma ta
mike ta debo ruwa a randa ta
watsa mata, suka ci gaba da
jibgar ta, shehu kam sai tsalleh
yake yana jin dadi, dan duk
dunia ba abinda ya ke so irin
yaga goggo na kwalfar Deedo,
saida sukai mata liiis,sannan
suka shige daki suka barta a
wurin. Dakyar ta lallaba ta
shige dan akurkin dakin ta,
kuka take yi sosai, ita kanta
tausayin kanta take yi, wannan
azaba ta ishe ta, neman hanyar
da zata kubutar da kanta kawai
take yi, ta lallaba tayi alwala
tazo ta fara sallah ta gama, ta
jawo littafin ta Geography
tasha karatu sosai, abinka da
mai sharp brain, dandanan ta
kwashe komai da take bukata,
ga yunwa ta addabe ta, ga
kuma wani mugun bacci da
yake figan ta, nan inda take ta
dan shingida, kafin kace wani
abu tuni bacci yayi gaba da ita,
abin ka da ansha bauta da
rana an gaji.