Sashe 34
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
BA’A SHAN
ZUMA..107&108
BA'A SHAN ZUMA… 107
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Bayan sun gama ta wuce ta
fesa wanka, ta dau gayu na
musamman domin taryar rabin
ran nata.
K'arfe biyu da kwata dai dai
suka iso gidan, da sallamarshi
ya shigo palon babu kowa sai
Mahmoud yaron Hafsat yana
kallon cartoon a MBC3. Da
gudu ya taso ya rungume
Nawap yana cewa
"ga Uncle ga Uncle."
D'aga shi sama Nawap yayi,
yana fadin "my boy, ka zama
babban mutum"
Dariya ya kyalkyale da shi,
"sosai ma, har na kai nursery 2
fa uncle"
"Smart boy" Nawap ya fada
yana dariya, sannan ya sauke
shi, ganin Deedo na saukowa
fuskarta kunshe da wani
murmushi na ban mamaki.
Karasawa yayi inda take tsaye
ta nannade hannayenta, ya
kalleta yace "yan mata na,
yakike?"
"Ina wuni" ta fada, yayin da ya
ansa a daburce, "na same ku
lafia?"
"Lafia lau, ya hanya?"
"Alhamdulillah, ina ta sauri na
zo nayi tozali da abin k'aunata
"
Rufe fuskarta tayi, alamar
kunya, tayi gaba tana cewa
"muje ka ci abinci, dan na san
yanzu haka ko breakfast baka
yi ba"
Bayanta ya biyo yana cewa
"banda abinki waye zai ba
gauro abinci"
Dariya tayi lokacin da suka iso
kan dining table din, sai da ta
rage muryanta, sannan tace
"just two weeks ya rage, ka
daina zama da yunwa in sha
Allah"
Ta juya ta cigaba da serving
dinshi, inda shi kuma yana
murmushi yace "I trust my
baby doll"
Ta kalle shi ta murmusa,
sannan ta mika mashi plate din
abincin, ta wuce kitchen domin
kwaso drinks.
A haka Hafsat ta tarar dasu
yana cin abincin, yayin da
Deedo ke zaune gefenshi suna
tadinsu cikin jin dadi.
Suka gaisa dashi, yana
tambayar
"ina mama small" tace
"dak'yar na lallabata, tana
sama tana bacci."
Sannan ta wuce cikin palon
inda Mahmoud yake a zaune.
Tunda Nawap yazo kullun
suna manne da Deedo, shi ke
kaita skool, sannan ya jirata
office din Dr. Kashim, har sai
ta fito exams, sannan ya dauko
ta su dawo gida kullun, har
zuwa yau da take gamawa.
A hanya take ce mashi
"Ummi ta fada maka da su Yaa
Hafsat zamu tafi?"
"Me zasuyi mana ne in mun
tafi dasu? Me sa Ummi take
mun haka, bata son ina
ke6ewa da matata" ya dan ja
tsaki, ya kara gudun da yake,
yace "ke kuma me kika ce
mata?"
Dariyar da take ta dan
tsagaita, tace "ni har na isa
ince wani abu ne bayan Ummi
ta gama yanke hukunci, lallai
ma"
"Duk ke kika ja mana ai da
kika fada mata"
"Zan bi wani ne ba tare da
sanin Ummi na ba aka fada
maka" tana yi tana kallon
yadda yayi kicin kicin shi dole
ga wanda aka shiga hakkinsa.
"Zaki maimaita ranar da kika
zo hannuna yarinya, dan sai
kinyi wata biyu baki ga Ummin
taki ba" ya fada a dai dai
lokacin da suka iso kofar gida,
ya fara danna horn kamar
wanda ya d'auko majinyaci.
Ita dai dariya kawai take,
yana yin parking ta fito zata
shige, yace "wa kika bar ma
wannan tilin books din naki?"
"Wa fa in ba mijin yar auta
ba" ta shige tana ta dariyar
mugunta.
Yayi kwafa, ya kwashi k'atin-
k'atin din text books din har
guda ukku, shi kanshi sai da
hannuwansa suka k'age, ya
zube mata su a palo, yana
banbami "koma ya ake tana
daukan books din nan, gata dai
abu kamar a karya ta"
Mahmoud yace "uncle kai da
wa kake fada?"
Yace "wannan yar siririyar
auntyn taka mana, ta sanya ni
daukar books masu nauyi"
Yayi dariya, yace "ai idan ta
dauka zasu fadar da ita ne shi
yasa, kai kuma kana da k'arfi
kaga"
Shafa kanshi yayi, ya wuce
kitchen ya dauka robar ruwa,
sannan ya wuce side dinsa.
[24/04 21:45] Nty Lubiee:
BA'A SHAN ZUMA…
108
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
K'arfe goma dai dai na safe,
kowa ya gama shiryawa tsab,
suna zaune a palo suna jiran
fitowar oga Nawap wanda yake
ta faman cika yana batsewa
shi dole an takura masu, za'a
hana su sakewa shi da Deedo.
Karasowa yayi, ya dau wanka
cikin farar gezna, hularshi da
takalminshi har ma da agogo
duk bak'ak'e, yana ta kanshin
Tom Ford Velvet Orchid,
Mahmoud kawai yai ma dariya,
ya kama hannunsa suka fita.
Deedo da Hafsat da suke
kunshe dariya suka kyalkyale,
sannan Deedo ta sa6i mama
small suka fito, yayin da Saude
take kwaso kayan da zasu tafi
dasu tana lodawa a boot.
A gaba suka zauna ita dashi,
sai mama small a hannunta,
yayin da Mahmoud da Hafsat
suke a baya. Haka suka fara
tafiyar kamar kurame, in banda
Mahmoud da mamah da suke
yan surutansu na yara.
* ********
K'arfe d'aya na rana Nawap
yayi parking motarsa a kofar
wani kwarmad'ad'd'an gida
wanda yake da tabbacin tabbas
nan ne gidan Goggo, domin ko
ba zai taba manta gidan da ya
fara ganin mamallakiyar
zuciyarsa ba.
Kallon Deedo yayi, yace
"kamar munyi batan kai
ko?"
"Anya kuwa?" Bari dai in shiga
mu ga"
Ta 6alla murfin motar ta fito,
yayin da shi ma ya bude nashi
kofar ya bita a baya.
Cikin gidan wanda ga
dukkan alamu rabon da ya ga
shara akalla anyi shekara
hud'u, domin ko yadda kasan
kango, haka bola ta samu wuri
ta basar, suka kutsa kansu,
Nawap ya kalle ta
"Bana tunanin akwai dan
Adam din da yake rayuwa a irin
wannan wurin, fito mu shiga
makwabta mu tambaya ko sun
koma wani wuri ne"
Basu ankara ba suka tsinkayi
murya daga cikin dan akurkin
dakin da Deedo take da, wanda
shi kadai yayi saura a cikin
dakunan da suke gidan, domin
kuwa sauran duk sun rufta,
kana iya hango komai daga
inda suke a tsaye.
"Wane dan banzan ne nan?
Iyii? Ko bakwa ji na ne
la'anannu"
Ta fara laluben sandarta,
dakyar ta dafa bango ta mik'e
tsaye, tana bin bangon ba tare
da sanin ta ba ta taka wani
kwano, aiko ba tare da 6ata
lokaci ba ta fadi kasa, ji kake
wani rigijib!!!
Nawap da Deedo da suke
tsaye bakin dakin suka yi
saurin kutsa kai ciki, amma
wani mahaluk'in k'arni tare da
wani gagarumin wari ne suka
yi ma hancinsu sallama nan da
nan suna rige-rige suka yo
waje da gudun bala'i, Nawap
ya rik'e cikinshi wanda yake
murd'a mishi, nan take ya fara
shek'a amai ba k'akk'autawa…
"Allah dai ya tsine muku, wai
su uban waye a nan?" Ta
cigaba da laluben inda ta
wurga sandar, ko Allah zai
taimaketa ta fita ta warci daya
a cikin irin yan iskan yaran da
suke shigowa suna tsokanarta
ko wacce rana.
(Nayi iya kokarina na karasa
labarin nan yau, amma hakan
bai samu ba, I promise yu
zuwa gobe in sha Allah.
Thanks y'all for the love. I love
yu too)
ZUMA..107&108
BA'A SHAN ZUMA… 107
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Bayan sun gama ta wuce ta
fesa wanka, ta dau gayu na
musamman domin taryar rabin
ran nata.
K'arfe biyu da kwata dai dai
suka iso gidan, da sallamarshi
ya shigo palon babu kowa sai
Mahmoud yaron Hafsat yana
kallon cartoon a MBC3. Da
gudu ya taso ya rungume
Nawap yana cewa
"ga Uncle ga Uncle."
D'aga shi sama Nawap yayi,
yana fadin "my boy, ka zama
babban mutum"
Dariya ya kyalkyale da shi,
"sosai ma, har na kai nursery 2
fa uncle"
"Smart boy" Nawap ya fada
yana dariya, sannan ya sauke
shi, ganin Deedo na saukowa
fuskarta kunshe da wani
murmushi na ban mamaki.
Karasawa yayi inda take tsaye
ta nannade hannayenta, ya
kalleta yace "yan mata na,
yakike?"
"Ina wuni" ta fada, yayin da ya
ansa a daburce, "na same ku
lafia?"
"Lafia lau, ya hanya?"
"Alhamdulillah, ina ta sauri na
zo nayi tozali da abin k'aunata
"
Rufe fuskarta tayi, alamar
kunya, tayi gaba tana cewa
"muje ka ci abinci, dan na san
yanzu haka ko breakfast baka
yi ba"
Bayanta ya biyo yana cewa
"banda abinki waye zai ba
gauro abinci"
Dariya tayi lokacin da suka iso
kan dining table din, sai da ta
rage muryanta, sannan tace
"just two weeks ya rage, ka
daina zama da yunwa in sha
Allah"
Ta juya ta cigaba da serving
dinshi, inda shi kuma yana
murmushi yace "I trust my
baby doll"
Ta kalle shi ta murmusa,
sannan ta mika mashi plate din
abincin, ta wuce kitchen domin
kwaso drinks.
A haka Hafsat ta tarar dasu
yana cin abincin, yayin da
Deedo ke zaune gefenshi suna
tadinsu cikin jin dadi.
Suka gaisa dashi, yana
tambayar
"ina mama small" tace
"dak'yar na lallabata, tana
sama tana bacci."
Sannan ta wuce cikin palon
inda Mahmoud yake a zaune.
Tunda Nawap yazo kullun
suna manne da Deedo, shi ke
kaita skool, sannan ya jirata
office din Dr. Kashim, har sai
ta fito exams, sannan ya dauko
ta su dawo gida kullun, har
zuwa yau da take gamawa.
A hanya take ce mashi
"Ummi ta fada maka da su Yaa
Hafsat zamu tafi?"
"Me zasuyi mana ne in mun
tafi dasu? Me sa Ummi take
mun haka, bata son ina
ke6ewa da matata" ya dan ja
tsaki, ya kara gudun da yake,
yace "ke kuma me kika ce
mata?"
Dariyar da take ta dan
tsagaita, tace "ni har na isa
ince wani abu ne bayan Ummi
ta gama yanke hukunci, lallai
ma"
"Duk ke kika ja mana ai da
kika fada mata"
"Zan bi wani ne ba tare da
sanin Ummi na ba aka fada
maka" tana yi tana kallon
yadda yayi kicin kicin shi dole
ga wanda aka shiga hakkinsa.
"Zaki maimaita ranar da kika
zo hannuna yarinya, dan sai
kinyi wata biyu baki ga Ummin
taki ba" ya fada a dai dai
lokacin da suka iso kofar gida,
ya fara danna horn kamar
wanda ya d'auko majinyaci.
Ita dai dariya kawai take,
yana yin parking ta fito zata
shige, yace "wa kika bar ma
wannan tilin books din naki?"
"Wa fa in ba mijin yar auta
ba" ta shige tana ta dariyar
mugunta.
Yayi kwafa, ya kwashi k'atin-
k'atin din text books din har
guda ukku, shi kanshi sai da
hannuwansa suka k'age, ya
zube mata su a palo, yana
banbami "koma ya ake tana
daukan books din nan, gata dai
abu kamar a karya ta"
Mahmoud yace "uncle kai da
wa kake fada?"
Yace "wannan yar siririyar
auntyn taka mana, ta sanya ni
daukar books masu nauyi"
Yayi dariya, yace "ai idan ta
dauka zasu fadar da ita ne shi
yasa, kai kuma kana da k'arfi
kaga"
Shafa kanshi yayi, ya wuce
kitchen ya dauka robar ruwa,
sannan ya wuce side dinsa.
[24/04 21:45] Nty Lubiee:
BA'A SHAN ZUMA…
108
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
K'arfe goma dai dai na safe,
kowa ya gama shiryawa tsab,
suna zaune a palo suna jiran
fitowar oga Nawap wanda yake
ta faman cika yana batsewa
shi dole an takura masu, za'a
hana su sakewa shi da Deedo.
Karasowa yayi, ya dau wanka
cikin farar gezna, hularshi da
takalminshi har ma da agogo
duk bak'ak'e, yana ta kanshin
Tom Ford Velvet Orchid,
Mahmoud kawai yai ma dariya,
ya kama hannunsa suka fita.
Deedo da Hafsat da suke
kunshe dariya suka kyalkyale,
sannan Deedo ta sa6i mama
small suka fito, yayin da Saude
take kwaso kayan da zasu tafi
dasu tana lodawa a boot.
A gaba suka zauna ita dashi,
sai mama small a hannunta,
yayin da Mahmoud da Hafsat
suke a baya. Haka suka fara
tafiyar kamar kurame, in banda
Mahmoud da mamah da suke
yan surutansu na yara.
* ********
K'arfe d'aya na rana Nawap
yayi parking motarsa a kofar
wani kwarmad'ad'd'an gida
wanda yake da tabbacin tabbas
nan ne gidan Goggo, domin ko
ba zai taba manta gidan da ya
fara ganin mamallakiyar
zuciyarsa ba.
Kallon Deedo yayi, yace
"kamar munyi batan kai
ko?"
"Anya kuwa?" Bari dai in shiga
mu ga"
Ta 6alla murfin motar ta fito,
yayin da shi ma ya bude nashi
kofar ya bita a baya.
Cikin gidan wanda ga
dukkan alamu rabon da ya ga
shara akalla anyi shekara
hud'u, domin ko yadda kasan
kango, haka bola ta samu wuri
ta basar, suka kutsa kansu,
Nawap ya kalle ta
"Bana tunanin akwai dan
Adam din da yake rayuwa a irin
wannan wurin, fito mu shiga
makwabta mu tambaya ko sun
koma wani wuri ne"
Basu ankara ba suka tsinkayi
murya daga cikin dan akurkin
dakin da Deedo take da, wanda
shi kadai yayi saura a cikin
dakunan da suke gidan, domin
kuwa sauran duk sun rufta,
kana iya hango komai daga
inda suke a tsaye.
"Wane dan banzan ne nan?
Iyii? Ko bakwa ji na ne
la'anannu"
Ta fara laluben sandarta,
dakyar ta dafa bango ta mik'e
tsaye, tana bin bangon ba tare
da sanin ta ba ta taka wani
kwano, aiko ba tare da 6ata
lokaci ba ta fadi kasa, ji kake
wani rigijib!!!
Nawap da Deedo da suke
tsaye bakin dakin suka yi
saurin kutsa kai ciki, amma
wani mahaluk'in k'arni tare da
wani gagarumin wari ne suka
yi ma hancinsu sallama nan da
nan suna rige-rige suka yo
waje da gudun bala'i, Nawap
ya rik'e cikinshi wanda yake
murd'a mishi, nan take ya fara
shek'a amai ba k'akk'autawa…
"Allah dai ya tsine muku, wai
su uban waye a nan?" Ta
cigaba da laluben inda ta
wurga sandar, ko Allah zai
taimaketa ta fita ta warci daya
a cikin irin yan iskan yaran da
suke shigowa suna tsokanarta
ko wacce rana.
(Nayi iya kokarina na karasa
labarin nan yau, amma hakan
bai samu ba, I promise yu
zuwa gobe in sha Allah.
Thanks y'all for the love. I love
yu too)