Sashe 18
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
BA’A SHAN
ZUMA… 54, 55
& 56
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Tun daga nesa ya fara hango
taron mutane, wuri ya samu
yayi parking, sannan ya fito
daga motan, a kafa ya karasa,
nan ya tarar da yan sanda har
guda ukku, biyu mata da namiji
guda. Hannuwan Goggo matan
suka kama suka rike ta gam
kamar wadda tayi kisan kai,
tirjewa take tana kuka kaman
ranta zai fita, amma matan nan
kokarin tura ta suke cikin
motarsu.
Da sauri Nawap ya karasa
gabansu yana tambayar abinda
ke faruwa amma babu wanda
ya tanka shi. Namijin dan
sandan ne ma ya juyo yace
"idan kana bukatar jin ba'asi
zaka iya biyo mu station
malam" a dai dai lokacin su
kuma suka yi nasarar tura kan
Goggo cikin motar suka shige
suka bata wuta.
Ba tare da bata lokaci ba
shima ya shige ta shi motar ya
bi bayan su har zuwa police
station din. Suna isa suka fito
da ita hannunta sagale da
handcuffs suka tusa keyarta
gaba, tana kuka tana komai,
amma ko tausayin tsufanta
basa yi, haka suka tura ta cikin
cell suka jawo shi suka rufe.
Da saurinshi ya karasa wurin
dan sandan yana tambayar
abinda ke faruwa, sai da
officern ya gama wasu 'yan
rubuce rubuce sannan ya dago
yace "malam ya kuke da matar
nan ne?" Nawap ya gyara
tsayuwarshi, yace "kanwar
mahaifi na ce, plz ka fada mun
abinda tayi" dan sandan ya
cigaba da jawabi kamar haka
"ita kam babu abinda tayi,
amma kasan dan kuka ya kan
ja ma uwarshi jifa, dan haka
shafin danta ne ya shafeta.."
"Ban fahimce ka ba" Nawap ya
fada yana kallonshi. Dan
sandan ya cigaba "yaronta
Shehu ne ya karya kafar wani
yaro, sannan kuma ya caka
mashi wuka a ciki, kuma an
nemeshi sama da kasa a cikin
garin nan an rasa, gashi kuma
iyayen wanda aka yi ma raunin
sunce baza su taba hakura ba,
saboda yaro yana can a asibiti
tsakanin rayuwa da mutuwa,
yau kuma kusan kwana hudu
kenan muna neman Shehu
amma babu wani labari, dan
haka muka yanke shawaran
kama uwashi, idan yana sonta
ya bayyana kanshi, sai mu
saketa"
Wani irin gumi ne ya yayyafo
ma Nawap, a lokaci guda kuma
ya fara karanto innalillahi wa
inna ilaihir raji'un…
Komawa yayi da baya, ya samu
wani dan benci ya zauna,
hannuwan shi duk biyun ya sa
ya tallabi kanshi, yana mai
cigaba da karanta innalillahi wa
inna ilaihir raji'un. Tunanin
abinda Goggo tai ma Deedo ya
fara yi, har wata zuciyar tace
ya tafi ya barta anan, amma
tunowan da yayi da ko
bakomai kanwar mahaifin
Deedonshi ce, shi ya bashi
damar mikewa ya koma gaban
dan sandan yace "abokina
yanzu menene abin yi?"
Officer yace "abin yi anan
shine kaje kaga dangin yaron a
asibiti, duk yadda kuka yi sai
ka dawo kai mana bayani"
Nawap yace "ka taimaka muje
tare mana" sai da yayi jim,
kaman ba zai je ba, sai kuma
yace "ok muje mana."
A tare suka fito suka shiga
motan Nawap din, sannan suka
doshi asibitin kai tsaye. Dakin
da akayi admitting yaron suka
nufa, nan suka tarar da baban
yaro yana matse kwalla.
Bayanin abinda ke tafe da su
dan sandan yai mashi, baban
ya dago yace "Allah dai ya
tsinewa yaron nan, Ian zaman
zamana ya jawo mun masifa,
yanzu gashi nan ance sai an
mishi aiki a ciki, kuma wai sai
na bada kudi naira dubu
saba'in, ni yanzu ina na
gansu?" Ya karasa maganan
yana matse hawayen da suka
taran mashi.
Dukawa gaban shi Nawap yayi,
yace "Baba kayi hakuri ka
daina kukan nan, alfarma zan
roke ka, kasa a saki mahaifiyar
Shehu da aka kama, ni kuma
zan biyawa yaronka kudin aiki
har ma dana magani, su kuma
yan sanda zasu cigaba da
neman Shehu har zuwa ranan
da za'a ganshi" dan tsohon ya
dago yace "in dai kayi wannan
alkawarin to zan sa a sake ta,
amma fa bazan taba yafewa
Shehu ba, dole ne alkali ya
raba mu"
Nawap yace "na maka alkawari
baba, muje in biya maku kudin
aikin, daga nan mu wuce
police station kasa a saki
Goggon" mikewa duk sukayi,
saida suka biya ATM Nawap ya
cire 100, 000 yaba dan tsoho,
sannan suka karasa station
aka gama rubuta statements,
daga nan aka fito da Goggo
ido yai mata gwale gwale
kaman danyen nama saboda
kukan da tasha, Nawap bai bari
ta ganshi ba, ya shige motarshi
ya kara gaba.
Unguwan ya koma, dakyar da
tambaya ya samu wani dan
matashi ya kai shi gidansu
Hally, a hanya ne yake
tambayar yaron abinda ya faru
da su Goggo, yaro da yaji
sanyin A.C, nan da nan ya baje
baki ya fara bashi labari yana
cewa "shi ai Shehun ne kasan
yanzu wasu mutane ne yake bi,
ni a yadda naji ma haka ake
cewa wai kashe yaron suka so
suyi, Allah ne bai basu sa'a ba,
sai dai suka caka mai wuka a
ciki kuma suka karya mashi
kafa saboda wata kungiya ce
garesu, shi kuma yaron ya fita
daga cikin su shine fa sukai
mai wannan danyen aiki."
"Allah ya kyauta" Nawap ya
fada, yaro ya cigaba da cewa
"amin fa, amma al'amarin
Shehu sai addu'a, gashi nan
yanzu ya ja ma uwar tashi ai" a
haka suka karaso kofar gidan,
ba tare da Nawap ya kara tanka
mashi ba, 1k ya zaro ya mika
mashi, sannan yace "shiga ciki
kace ana sallama da Hallyn"
yana kyarma ya anshe dubun
ya fara rafka godia, sannan ya
wuce cikin gidan yana ta
murna.
A tare suka fito, yana tsaye
jikin motan ya nade
hannayenshi yana dan kalle
kalle. Tana ganinshi ta gane,
dan haka ta karaso da dan
sauri ta gaishe shi, ya ansa
fuskanshi sake, cikin zakuwa
ta fara tambayar "ya wajen su
Deedo? Tana lafia?" Murmushin
shi mai tsada ya saki, yace
"tana nan lafia lau, nazo ansan
mata result dinta nema, tace na
biyo nace tana gaishe ki, kuma
na baki number ta" a dai dai
lokacin ya duka cikin motan ya
samo wata yar paper ya rubuta
mata number, ya dago ya mika
mata.
Hannu biyu tasa ta ansa tana
ta washe baki, ta san ko
bakomai, Deedo tana cikin jin
dadi tunda gashi har waya gare
ta. Godia tai mashi, sannan ta
juya zata koma ciki, kudi ya
ciro ya bata, amma taki ansa,
dakyar ya samu ta ansa, yai
mata sallama ya shige motan
ya bar kofan gidan.
Sai da ya hau titi sosai, ya fara
tafia, sannan ya jawo wayanshi
da niyyar kiran Ummi don ya
shaida mata ya taho, missed
calls din Aysha ya gani kusan
guda 5. Wani mugun tsaki ya
jaa, inda a lokaci guda kuma
yayi wurgi da wayan a seat din
dake kusa dashi..
ZUMA… 54, 55
& 56
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Tun daga nesa ya fara hango
taron mutane, wuri ya samu
yayi parking, sannan ya fito
daga motan, a kafa ya karasa,
nan ya tarar da yan sanda har
guda ukku, biyu mata da namiji
guda. Hannuwan Goggo matan
suka kama suka rike ta gam
kamar wadda tayi kisan kai,
tirjewa take tana kuka kaman
ranta zai fita, amma matan nan
kokarin tura ta suke cikin
motarsu.
Da sauri Nawap ya karasa
gabansu yana tambayar abinda
ke faruwa amma babu wanda
ya tanka shi. Namijin dan
sandan ne ma ya juyo yace
"idan kana bukatar jin ba'asi
zaka iya biyo mu station
malam" a dai dai lokacin su
kuma suka yi nasarar tura kan
Goggo cikin motar suka shige
suka bata wuta.
Ba tare da bata lokaci ba
shima ya shige ta shi motar ya
bi bayan su har zuwa police
station din. Suna isa suka fito
da ita hannunta sagale da
handcuffs suka tusa keyarta
gaba, tana kuka tana komai,
amma ko tausayin tsufanta
basa yi, haka suka tura ta cikin
cell suka jawo shi suka rufe.
Da saurinshi ya karasa wurin
dan sandan yana tambayar
abinda ke faruwa, sai da
officern ya gama wasu 'yan
rubuce rubuce sannan ya dago
yace "malam ya kuke da matar
nan ne?" Nawap ya gyara
tsayuwarshi, yace "kanwar
mahaifi na ce, plz ka fada mun
abinda tayi" dan sandan ya
cigaba da jawabi kamar haka
"ita kam babu abinda tayi,
amma kasan dan kuka ya kan
ja ma uwarshi jifa, dan haka
shafin danta ne ya shafeta.."
"Ban fahimce ka ba" Nawap ya
fada yana kallonshi. Dan
sandan ya cigaba "yaronta
Shehu ne ya karya kafar wani
yaro, sannan kuma ya caka
mashi wuka a ciki, kuma an
nemeshi sama da kasa a cikin
garin nan an rasa, gashi kuma
iyayen wanda aka yi ma raunin
sunce baza su taba hakura ba,
saboda yaro yana can a asibiti
tsakanin rayuwa da mutuwa,
yau kuma kusan kwana hudu
kenan muna neman Shehu
amma babu wani labari, dan
haka muka yanke shawaran
kama uwashi, idan yana sonta
ya bayyana kanshi, sai mu
saketa"
Wani irin gumi ne ya yayyafo
ma Nawap, a lokaci guda kuma
ya fara karanto innalillahi wa
inna ilaihir raji'un…
Komawa yayi da baya, ya samu
wani dan benci ya zauna,
hannuwan shi duk biyun ya sa
ya tallabi kanshi, yana mai
cigaba da karanta innalillahi wa
inna ilaihir raji'un. Tunanin
abinda Goggo tai ma Deedo ya
fara yi, har wata zuciyar tace
ya tafi ya barta anan, amma
tunowan da yayi da ko
bakomai kanwar mahaifin
Deedonshi ce, shi ya bashi
damar mikewa ya koma gaban
dan sandan yace "abokina
yanzu menene abin yi?"
Officer yace "abin yi anan
shine kaje kaga dangin yaron a
asibiti, duk yadda kuka yi sai
ka dawo kai mana bayani"
Nawap yace "ka taimaka muje
tare mana" sai da yayi jim,
kaman ba zai je ba, sai kuma
yace "ok muje mana."
A tare suka fito suka shiga
motan Nawap din, sannan suka
doshi asibitin kai tsaye. Dakin
da akayi admitting yaron suka
nufa, nan suka tarar da baban
yaro yana matse kwalla.
Bayanin abinda ke tafe da su
dan sandan yai mashi, baban
ya dago yace "Allah dai ya
tsinewa yaron nan, Ian zaman
zamana ya jawo mun masifa,
yanzu gashi nan ance sai an
mishi aiki a ciki, kuma wai sai
na bada kudi naira dubu
saba'in, ni yanzu ina na
gansu?" Ya karasa maganan
yana matse hawayen da suka
taran mashi.
Dukawa gaban shi Nawap yayi,
yace "Baba kayi hakuri ka
daina kukan nan, alfarma zan
roke ka, kasa a saki mahaifiyar
Shehu da aka kama, ni kuma
zan biyawa yaronka kudin aiki
har ma dana magani, su kuma
yan sanda zasu cigaba da
neman Shehu har zuwa ranan
da za'a ganshi" dan tsohon ya
dago yace "in dai kayi wannan
alkawarin to zan sa a sake ta,
amma fa bazan taba yafewa
Shehu ba, dole ne alkali ya
raba mu"
Nawap yace "na maka alkawari
baba, muje in biya maku kudin
aikin, daga nan mu wuce
police station kasa a saki
Goggon" mikewa duk sukayi,
saida suka biya ATM Nawap ya
cire 100, 000 yaba dan tsoho,
sannan suka karasa station
aka gama rubuta statements,
daga nan aka fito da Goggo
ido yai mata gwale gwale
kaman danyen nama saboda
kukan da tasha, Nawap bai bari
ta ganshi ba, ya shige motarshi
ya kara gaba.
Unguwan ya koma, dakyar da
tambaya ya samu wani dan
matashi ya kai shi gidansu
Hally, a hanya ne yake
tambayar yaron abinda ya faru
da su Goggo, yaro da yaji
sanyin A.C, nan da nan ya baje
baki ya fara bashi labari yana
cewa "shi ai Shehun ne kasan
yanzu wasu mutane ne yake bi,
ni a yadda naji ma haka ake
cewa wai kashe yaron suka so
suyi, Allah ne bai basu sa'a ba,
sai dai suka caka mai wuka a
ciki kuma suka karya mashi
kafa saboda wata kungiya ce
garesu, shi kuma yaron ya fita
daga cikin su shine fa sukai
mai wannan danyen aiki."
"Allah ya kyauta" Nawap ya
fada, yaro ya cigaba da cewa
"amin fa, amma al'amarin
Shehu sai addu'a, gashi nan
yanzu ya ja ma uwar tashi ai" a
haka suka karaso kofar gidan,
ba tare da Nawap ya kara tanka
mashi ba, 1k ya zaro ya mika
mashi, sannan yace "shiga ciki
kace ana sallama da Hallyn"
yana kyarma ya anshe dubun
ya fara rafka godia, sannan ya
wuce cikin gidan yana ta
murna.
A tare suka fito, yana tsaye
jikin motan ya nade
hannayenshi yana dan kalle
kalle. Tana ganinshi ta gane,
dan haka ta karaso da dan
sauri ta gaishe shi, ya ansa
fuskanshi sake, cikin zakuwa
ta fara tambayar "ya wajen su
Deedo? Tana lafia?" Murmushin
shi mai tsada ya saki, yace
"tana nan lafia lau, nazo ansan
mata result dinta nema, tace na
biyo nace tana gaishe ki, kuma
na baki number ta" a dai dai
lokacin ya duka cikin motan ya
samo wata yar paper ya rubuta
mata number, ya dago ya mika
mata.
Hannu biyu tasa ta ansa tana
ta washe baki, ta san ko
bakomai, Deedo tana cikin jin
dadi tunda gashi har waya gare
ta. Godia tai mashi, sannan ta
juya zata koma ciki, kudi ya
ciro ya bata, amma taki ansa,
dakyar ya samu ta ansa, yai
mata sallama ya shige motan
ya bar kofan gidan.
Sai da ya hau titi sosai, ya fara
tafia, sannan ya jawo wayanshi
da niyyar kiran Ummi don ya
shaida mata ya taho, missed
calls din Aysha ya gani kusan
guda 5. Wani mugun tsaki ya
jaa, inda a lokaci guda kuma
yayi wurgi da wayan a seat din
dake kusa dashi..