← Book details Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 36

Sashe 17

Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

BA’A SHAN
ZUMA… 51, 52
& 53
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Da sauri ya katse wayan Aysha,
inda ya daga kiran na Deedo
kai tsaye, a hankali kwance ta
fara magana, inda ya nemi
tunaninshi gaba daya ya rasa,
jin muryanta yake har cikin
bargonshi, lumshe
idanuwanshi yayi inda a lokaci
guda ya nemi damuwar da take
tare dashi ya rasa, cikin
kunnenshi ya tsinkayi muryanta
tana cewa "kaji Yaa Nawap?"
Firgigit, ya dawo daga duniyar
da yake, yace "mei kika ce ne?"
Tace "zan bada sako wurin
Hally ne" "go ahead ina jinki"
ya fada, ita kuma ta cigaba da
cewa "kace ina gaisheta, kuma
dan Allah ka bata number ta
kace ta kira ni" duk a tsorace
take maganan, gani take
kaman zai ce ta raina shi ne,
dan haka take maganan cikin
wani salo na yarinta da neman
afuwa.
Wani numfashi ya ja, sannan
yace "shikenan sakon naki?"
Kai ta girgiza kaman yana
kallonta, sannan ta ansa mashi
da "eh shikenan, sai da safe"
da sauri ta katse wayan, inda
shi kuma ta barshi da tsananin
tunani da muradin sauraren
muryanta mai dadi. Yana cikin
wannan hali wayan Ayshan ta
kara shigowa, wanda dama
kiran take ta faman yi tun yana
cikin magana da Deedo.
Daga wayan yayi, ba tare da
yace komai ba, a tunaninshi
kukan zata cigaba da yi, sai
yaji ta buda murya tace
"Nawap na gano dalilinka na
wulakantani, yanzu nasan
menene dalilinka na kin ansar
soyayyata, abinda nake so ka
gane shine, bazan taba rayuwa
ba tare da kai ba, sannan kuma
wata yar ficiciyar yarinya bata
isa tazo ta wargaza mun plans
din da na dade ina shiryawa
shekara da shekaru ba
Wata tsawa ya daka mata,
wadda tasa ta shiga taitayinta
lokaci guda, cikin wata
kakkausar murya ya fara
magana "who do yu think yu
re? Nd where all this ur
nonsense are heading to?"
Kasa ansa shi tayi, inda shi
kuma ya cigaba da cewar
"thou, ban san ina maganan ki
ya dosa ba, amma ina so ki
gane ba wanda ya isa ya juya
ni, ni nake da ikon kaina kuma
ba wanda ya isa ya sani yin
abinda ba shi nake so ba, shin
wai ke yaushe ne ranar da zaki
farka daga dogon mafarkin da
kike yi? Yaushe ne zaki gane
abinda kikeyi is so old
fashion? Ya kamata ki neman
ma kanki Mafita Aysha, me nd
yu ain't belong to each other,
plz ki barni naji da rayuwata, ki
fita harka ta plz.. "
Bata bari ya karasa fadar
abinda yake son fada ba, ta
katse shi da cewar "lallai kana
da aiki Nawap, idan har kana
tunanin akwai ranar da zan
daina sonka, ina mai tabbatar
maka da cewar na bar dunia a
wannan ranan, sannan kuma
duk wulakancin da kake ganin
ka iya, bazan hana ka yi mun
ba, amma ka sani, wannan
fitsararriyar yarinyar daka baro
a gida, a kanta abin zai kare,
so yu better becareful.." tana
gama fadin haka ta katse
wayan tayi wurgi da ita, a
lokaci guda kuma ta fashe da
wani matsanancin kuka, ta
rasa wane irin so take ma
Nawap wanda ta kasa cire shi
daga cikin ranta shekara kusan
biyar kenan!
Sai a lokacin ya gane inda
maganan Aysha ya dosa,
amma babban abinda ke bashi
mamaki baya wuce yadda take
neman kulla wata alaka ta
daban tsakanin shi da Deedo,
yarinyar da tausayinta yasa
yake bata duk wani
muhimmanci da yake bata,
yarinyar da ya dauka a
matsayin kanwarshi, shin wai
menene dalilinta na yin wannan
exaggerating din? Amsar da ya
rasa inda zai samo ta, mikewa
yayi jiki ba kwari ya karasa
cikin bedroom, a lokaci guda
ya cire jallabiyan jikinshi yaja
towel ya daura sannan ya wuce
bathroom…
Ranan Monday da misalin karfe
5 na asuba Nawap ya mike,
bayan ya dawo masallaci bai
jira komai ba ya fara shiri, duk
wani abu da zai bukata ya
gama tattarawa. Karfe 7 dai dai
ya isa office din su, anan ya
samu yayi breakfast inda daga
bisani ya karasa nashi office
din, anan ya tadda reply na
letter da yayi na son yin tafiya
ta sati daya.
P.A dinshi ne ya shigo ya
gaishe da shi, sannan ya ke
fada mashi cewar dazu aka
kawo lettern daga office din
director. Godia yai mashi, inda
ya koma kan wata 2seater da
ke aje a tsakiyan office din ya
zauna. Zaro lettern yayi, ya fara
dubawa, nan da nan murmushi
ya bayyana a kan fuskanshi,
cikin hanzari ya mike yayi kiran
P.A din yai mashi bayanin duk
abinda ya kamata, sannan ya
tattara laptop dinshi da sauran
documents din da zai bukata
yai mashi sallama ya fito ..
Inda yayi parking mota ya nufa,
ya zuba tarkacen a baya,
sannan ya shiga ya tada motan
ya fito.
Gudu sosai ya rinka yi
hankalinshi kwance, jin
zuciyanshi yake fari tass
kaman anyi mashi albishir da
wani babban abun alkairi. Cikin
ikon Allah ya shigo garin Ningi,
bai jira komai ba ya wuce
skool din su Deedo, cikin
kankanin lokaci yayi duk wani
abu da ya kamata, sannan ya
anshi result din yai masu
sallama ya fito.
A hankali ya fara shiga cikin
garin yana tunanin ta ina zai
gano gidan su Hally, hanyar
gidan Goggo ya dosa, dan ya
san ta can ne kawai zai iya
samun damar da zai gane
gidan su yarinyar…
Chapter 17 · 0% Book details