Sashe 30
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
BA’A SHAN
ZUMA…
96,97&98
BA'A SHAN ZUMA… 96
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
BAYAN SHEKARA UKKU
A hankali yake saukowa daga
matattakalar jirgin janye da dan
madaidaicin trolley, yana
shakar iskar da take busawa
mai cike da ni'ima tamkar za'a
saki ruwan sama a dai dai
lokacin. Waige-waige yake
alamar yana neman wanda ya
zo daukarshi, can ya hango ta
sanye da wata light purple d'in
abaya, ta yafa gyalen, ta nade
hannayenta duk biyun ta zuba
mashi idanu tana murmushi.
Sosai ya wara idonshi yana
kare mata kallo, tabbas
Deedonshi ce, ta canja sosai,
ta zama cikakkiyar budurwa,
fatar jikinta ta goge sosai, ga
wani annuri mai haske tattare
da ita. Wani mugun dadi ne ya
tsirga zuciyarsa, nan take
soyayyarta ta dawo masa
sabuwa fil, tayi masa famin
ciwon da yake fama da shi
shekara da shekaru, sai dai
kuma ya san ta riga ta mashi
nisa, ya san son da take ma
Affan ba irin wanda zata yi
fatali da shi ne ba, ya san ba
zai taba samun kar6uwa a
wurin zuciyar da ya hallakar da
tashi zuciyar domin ta ba, dan
haka dole ya kama mutuncinshi
tun kafin ya zube a idonta.
Gintsewa yayi, ya karasa gaban
ta, dariya take mai cike da
wani salo, tana kallonshi, a
lokaci guda tace "sannu da
zuwa Yaa Nawap"
Kaman ya nitse a wurin,
kasancewar muryarta da ya ji,
shekara ukku cif cif rabon da
ya ji wannan zakakkar muryar.
Dakyar ya dawo daga duniyar
da yake, yace "na sameku
lafiya lil sis?" "Lafia lau" ta
fada, yayin da ta anshi trolleyn
da ke hannunsa tayi gaba, shi
kuma ya bita a baya.
Inda tayi parking suka
k'arasa, fuskanta lullu6e da
wani farin ciki wanda ba zai
iya 6oyuwa ba, bayan motan ta
buda ta jefa jakan hannunta,
sannan ta zagaya driver seat ta
zauna ta daura seat belt, duk
idanun Nawap na kanta,
mamakin ta yake yi sosai,
yadda take abu komai a waye,
kanta ya gama fashewa kamar
ba Deedon Goggo ba, kallonshi
tayi ta saki murmushi wanda ya
rasa ko na menene sai dai ya
kawar da kanshi, ita kam ta yi
ma mota key suka kara gaba.
BA'A SHAN ZUMA… 97
NALUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Har suka je gida ba wanda ya
tanka ma wani, illa Deedo da
lokaci zuwa lokaci ta kan kai
dubanta gareshi sannan ta saki
murmushi, wanda ya rasa gane
ko na menene, daga k'arshe
tasa ya tsargu da kanshi, har
yana tunanin kodai wani abu
ne a jikinsa wanda yake sanya
ta dariya? Nan da nan ya hade
rai, ya juyar da kanshi yana ta
faman shan kanshi, har suka
isa.
Wucewa ciki yayi bayan tayi
parking, inda ita kuma ta fito
da jakarsa, ta ja zuwa cikin
gidan.
Da murna Ummi ta tare shi
tana mashi barka da zuwa,
cikin jin dadi da girmamawa ya
isa suka gaisa, sannan suka
mike gaba dayan su zuwa
dining table, kamar sun san da
yunwa ya iso.
A haka suka gama cin
abincinsu hankali kwance,
suna yi suna yar fira jefi-jefi ta
yaushe gamo.
* **—-******
Tun bayan da Nawap ya dawo
kwata-kwata Deedo ta rasa
gane kanshi, baya shiga
harkan ta ko kadan, haka zalika
ko shigowa yayi ya tarar da ita,
to fa baya zama zai bar wurin,
inda a bangarenta take fama
da so da kuma k'aunar shi
wanda su kan tunzura
zuciyarta. Hanyar da zata sanar
dashi yadda soyayyar shi ke
azabtar da ita take nema,
amma ina, babu fuska ta
bangarensa, domin kuwa ya
dade da sallamawa da ita, ya
shafa ma zuciyar sa ruwan
sanyi, ya daukan ma kanshi
alkawarin ba zai taba takurata
ta so shi ba.
Ganin halin ko in kula da
Nawap yake gwada ma Deedo,
yasa Ummi ta kira shi, tana
tambayar "ni kam Nawap ina
maganar ku ta kwana kai da
auta ta?" Ba tare da ya kalleta
ba yace "Ummi wannan
magana ai ta wuce, ita da take
da wanda take so" murmushi
Ummi tayi, ganin yadda yayi
kicin-kicin da ido, tace "me zai
hana ka kara jarraba sa'ar ka,
ka sani ko ka samu kar6uwa
yanzu" bai ce komai ba, sai ma
mikewa da yayi ya wuce part
dinsa…
BA'A SHAN ZUMA… 98
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Yana shiga ya mike a kujera
yana jin wani tiririn son Deedo
na tokarar zuciyar sa, anya zai
iya jure rashinta? Ko dai
shawarar da Ummi ta bashi zai
yi amfani da? Cikin azama ya
mike ya jawo wayarsa, ya cire
screen lock din, nan da nan
hotonsu shida ita da suka
dauka wata rana dazai koma
Abuja ya bayyana, sosai ya
kura ma hoton ido yana ganin
yadda take dariya, ga dukkan
alamu bata da wata damuwa a
wancan lokacin. A fili ya furta
"i can't let yu go Deedo, cuz yu
belongs to me" ya shafa
fuskan wayan, sannan ya
lalubo number ta a sabon layin
mtn din da yake amfani da shi.
Sai da ya kira har ta katse
bata daga ba, inda ya k'ara kira
a karo na biyu, nan ma shiru
kake ji. Text ya tura mata "Ina
fatan lokaci yayi da zan samu
ansar tambayar da na maki
shekaru ukku da suka wuce" ya
tura ba tare da ya sanar da ita
ko wanene ba.
Kwance take tana sana'ar
tata, wato tunanin halin da zata
shiga in ta rasa Nawap, tana
kallo aka kira har ta katse
amma bata ko motsa yatsanta
ba, shigowar text din ne yasa
ta gane mai kiran yana bukatar
wani abu daga gare ta. Hannu
tasa ta janyo wayan ta buda
text din, sai da ta gama
karantawa sannan ta duba
number, amma bata san mai
ita ba, tunani sosai ya cika
kwanyar ta, daga k'arshe
dabara ta fado mata, inda ta
sanya number a TrueCaller,
nan ta ci karo da sunan DR.
NAWAP KHAMIS har ma da pic
dinshi..
Yadda kasan an mata albishir
da gidan aljanna, haka Deedo
ta tsinci kanta cikin farin ciki.
Zumbur ta mike daga
kwanciyar da take ta kara
murza idonta, tabbas ba gizau
sunan yake mata ba, cikin
zazzodi ta fara rubuta mashi
ansa "I'm just waiting for this
day to come" can kuma wata
zuciyar ta bata shawaran ta
dan jaa class mana, tunda dai
har yanzu yana son ta.
Murmushi ta saki sannan ta
goge text din, ta rubuta wani
"nd who's this?" Ta tura masa
ba wai don zuciyarta ta so ba.
Jin shigowar text yasa yayi
saurin duba wayar, bayan ya
karanta, yayi murmushin
takaici, sannan ya rubuta
"someone who can't live
without yu" ya senda mata…
Ganin text din yasa ta taka
rawar disco, domin ta gama
sarewa Nawap ya guje mata,
ashe ba haka abin yake ba,
ashe kallon kitse ne su ke wa
rogo. Wasu hawayen jin dadi
suka gangaro ga bakinta
kunshe da murmushi, ta shafa
idonta taji tabbas hawaye ne,
nan ta kara fadada
murmushinta, domin duk
duniya ba yanayin da ya kai
wannan dadi, kana hawaye a
lokaci guda kuma kana
murmushi, wannan ya nuna
farin cikin ya kai k'arshe
ZUMA…
96,97&98
BA'A SHAN ZUMA… 96
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
BAYAN SHEKARA UKKU
A hankali yake saukowa daga
matattakalar jirgin janye da dan
madaidaicin trolley, yana
shakar iskar da take busawa
mai cike da ni'ima tamkar za'a
saki ruwan sama a dai dai
lokacin. Waige-waige yake
alamar yana neman wanda ya
zo daukarshi, can ya hango ta
sanye da wata light purple d'in
abaya, ta yafa gyalen, ta nade
hannayenta duk biyun ta zuba
mashi idanu tana murmushi.
Sosai ya wara idonshi yana
kare mata kallo, tabbas
Deedonshi ce, ta canja sosai,
ta zama cikakkiyar budurwa,
fatar jikinta ta goge sosai, ga
wani annuri mai haske tattare
da ita. Wani mugun dadi ne ya
tsirga zuciyarsa, nan take
soyayyarta ta dawo masa
sabuwa fil, tayi masa famin
ciwon da yake fama da shi
shekara da shekaru, sai dai
kuma ya san ta riga ta mashi
nisa, ya san son da take ma
Affan ba irin wanda zata yi
fatali da shi ne ba, ya san ba
zai taba samun kar6uwa a
wurin zuciyar da ya hallakar da
tashi zuciyar domin ta ba, dan
haka dole ya kama mutuncinshi
tun kafin ya zube a idonta.
Gintsewa yayi, ya karasa gaban
ta, dariya take mai cike da
wani salo, tana kallonshi, a
lokaci guda tace "sannu da
zuwa Yaa Nawap"
Kaman ya nitse a wurin,
kasancewar muryarta da ya ji,
shekara ukku cif cif rabon da
ya ji wannan zakakkar muryar.
Dakyar ya dawo daga duniyar
da yake, yace "na sameku
lafiya lil sis?" "Lafia lau" ta
fada, yayin da ta anshi trolleyn
da ke hannunsa tayi gaba, shi
kuma ya bita a baya.
Inda tayi parking suka
k'arasa, fuskanta lullu6e da
wani farin ciki wanda ba zai
iya 6oyuwa ba, bayan motan ta
buda ta jefa jakan hannunta,
sannan ta zagaya driver seat ta
zauna ta daura seat belt, duk
idanun Nawap na kanta,
mamakin ta yake yi sosai,
yadda take abu komai a waye,
kanta ya gama fashewa kamar
ba Deedon Goggo ba, kallonshi
tayi ta saki murmushi wanda ya
rasa ko na menene sai dai ya
kawar da kanshi, ita kam ta yi
ma mota key suka kara gaba.
BA'A SHAN ZUMA… 97
NALUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Har suka je gida ba wanda ya
tanka ma wani, illa Deedo da
lokaci zuwa lokaci ta kan kai
dubanta gareshi sannan ta saki
murmushi, wanda ya rasa gane
ko na menene, daga k'arshe
tasa ya tsargu da kanshi, har
yana tunanin kodai wani abu
ne a jikinsa wanda yake sanya
ta dariya? Nan da nan ya hade
rai, ya juyar da kanshi yana ta
faman shan kanshi, har suka
isa.
Wucewa ciki yayi bayan tayi
parking, inda ita kuma ta fito
da jakarsa, ta ja zuwa cikin
gidan.
Da murna Ummi ta tare shi
tana mashi barka da zuwa,
cikin jin dadi da girmamawa ya
isa suka gaisa, sannan suka
mike gaba dayan su zuwa
dining table, kamar sun san da
yunwa ya iso.
A haka suka gama cin
abincinsu hankali kwance,
suna yi suna yar fira jefi-jefi ta
yaushe gamo.
* **—-******
Tun bayan da Nawap ya dawo
kwata-kwata Deedo ta rasa
gane kanshi, baya shiga
harkan ta ko kadan, haka zalika
ko shigowa yayi ya tarar da ita,
to fa baya zama zai bar wurin,
inda a bangarenta take fama
da so da kuma k'aunar shi
wanda su kan tunzura
zuciyarta. Hanyar da zata sanar
dashi yadda soyayyar shi ke
azabtar da ita take nema,
amma ina, babu fuska ta
bangarensa, domin kuwa ya
dade da sallamawa da ita, ya
shafa ma zuciyar sa ruwan
sanyi, ya daukan ma kanshi
alkawarin ba zai taba takurata
ta so shi ba.
Ganin halin ko in kula da
Nawap yake gwada ma Deedo,
yasa Ummi ta kira shi, tana
tambayar "ni kam Nawap ina
maganar ku ta kwana kai da
auta ta?" Ba tare da ya kalleta
ba yace "Ummi wannan
magana ai ta wuce, ita da take
da wanda take so" murmushi
Ummi tayi, ganin yadda yayi
kicin-kicin da ido, tace "me zai
hana ka kara jarraba sa'ar ka,
ka sani ko ka samu kar6uwa
yanzu" bai ce komai ba, sai ma
mikewa da yayi ya wuce part
dinsa…
BA'A SHAN ZUMA… 98
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Yana shiga ya mike a kujera
yana jin wani tiririn son Deedo
na tokarar zuciyar sa, anya zai
iya jure rashinta? Ko dai
shawarar da Ummi ta bashi zai
yi amfani da? Cikin azama ya
mike ya jawo wayarsa, ya cire
screen lock din, nan da nan
hotonsu shida ita da suka
dauka wata rana dazai koma
Abuja ya bayyana, sosai ya
kura ma hoton ido yana ganin
yadda take dariya, ga dukkan
alamu bata da wata damuwa a
wancan lokacin. A fili ya furta
"i can't let yu go Deedo, cuz yu
belongs to me" ya shafa
fuskan wayan, sannan ya
lalubo number ta a sabon layin
mtn din da yake amfani da shi.
Sai da ya kira har ta katse
bata daga ba, inda ya k'ara kira
a karo na biyu, nan ma shiru
kake ji. Text ya tura mata "Ina
fatan lokaci yayi da zan samu
ansar tambayar da na maki
shekaru ukku da suka wuce" ya
tura ba tare da ya sanar da ita
ko wanene ba.
Kwance take tana sana'ar
tata, wato tunanin halin da zata
shiga in ta rasa Nawap, tana
kallo aka kira har ta katse
amma bata ko motsa yatsanta
ba, shigowar text din ne yasa
ta gane mai kiran yana bukatar
wani abu daga gare ta. Hannu
tasa ta janyo wayan ta buda
text din, sai da ta gama
karantawa sannan ta duba
number, amma bata san mai
ita ba, tunani sosai ya cika
kwanyar ta, daga k'arshe
dabara ta fado mata, inda ta
sanya number a TrueCaller,
nan ta ci karo da sunan DR.
NAWAP KHAMIS har ma da pic
dinshi..
Yadda kasan an mata albishir
da gidan aljanna, haka Deedo
ta tsinci kanta cikin farin ciki.
Zumbur ta mike daga
kwanciyar da take ta kara
murza idonta, tabbas ba gizau
sunan yake mata ba, cikin
zazzodi ta fara rubuta mashi
ansa "I'm just waiting for this
day to come" can kuma wata
zuciyar ta bata shawaran ta
dan jaa class mana, tunda dai
har yanzu yana son ta.
Murmushi ta saki sannan ta
goge text din, ta rubuta wani
"nd who's this?" Ta tura masa
ba wai don zuciyarta ta so ba.
Jin shigowar text yasa yayi
saurin duba wayar, bayan ya
karanta, yayi murmushin
takaici, sannan ya rubuta
"someone who can't live
without yu" ya senda mata…
Ganin text din yasa ta taka
rawar disco, domin ta gama
sarewa Nawap ya guje mata,
ashe ba haka abin yake ba,
ashe kallon kitse ne su ke wa
rogo. Wasu hawayen jin dadi
suka gangaro ga bakinta
kunshe da murmushi, ta shafa
idonta taji tabbas hawaye ne,
nan ta kara fadada
murmushinta, domin duk
duniya ba yanayin da ya kai
wannan dadi, kana hawaye a
lokaci guda kuma kana
murmushi, wannan ya nuna
farin cikin ya kai k'arshe