Sashe 15
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
BA’A SHAN
ZUMA… 45&46
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Da dan sauri ya karasa wurin
ajiyar motocin, inda ya darzo
wata dark blue din Audi R8,
reverse yayi, sannan ya gyara
tsayuwar motar, inda su kuma
a lokaci daya suka bude suka
shiga. Deedo ce a gaba, yayin
da Ummi ta kame a owner's
corner. Wuta ya ba motar,
sannan suka lula saman titi
hankali kwance.
Tafiya suka yi mai dan nisa,
Deedo har ta fara tunanin ko
garin zasu bari. Daga karshe
dai ta ware idanunta ta cigaba
da yan kalle kalle, cikin hikima
Nawap ke satar kallonta yana
ganin yadda farin ciki ke
bayyane a fuskanta, yanayinta
kawai, zai sanar da kai cewar
bata da sauran damuwa.
Murmushi ya saki wanda bai
san lokacin da ya sufce mashi
ba, a haka suka iso main
house din su Ummi da yake
Hayin Banki. Ba tare da bata
lokaci ba ya samu wuri yayi
parking, sannan duk suka fito
suka shige ciki.
Zaune suka tarar da mai gidan
a cikin wata yar baranda, idon
shi sanye da medical glass
yana duba jaridar Daily Trust.
Inda yake zaune suka karasa
duk suka kwashi gaisuwa,
sannan suka mike gaba
dayansu zuwa cikin gidan.
Kallon Deedo yake kaman ya
taba sanin mai irin fuskarta,
sai dai bai ce komai ba har
suka shige ciki. Ita ma tunda
suka shiga take kallon dattijon
mai cikar kamala da kwarjini,
kamar shi sosai ta gani da
Nawap, sai dai yanayin tsufa
kawai da yake tattare dashi.
A palon suka samu Inna zaune
da yar casbaharta tana lazumi.
Kallo daya tai wa Deedo taji
gabanta ya fadi, a take kuma ta
yardar wa kanta cewar duk
yadda akai wannan yarinyar
jininta ce. A daddafe suka
gaisa, yau ko tsokanar da ta
saba yiwa Nawap ba ta mai ba,
cikin zakuwa ta kalli Ummi tace
"ke kam ina kika samo mai
kama da ke?" Murmushi Ummi
tayi, ba tare da bata lokaci ba
kuma ta warware masu komai
dangane da Deedo, ta kara da
cewar "amma yanzu ta dawo
nan da zama kenan in sha
Allah"
Salati Inna ta kwasa, sannan ta
saki kuka, tana cewa "yaki nan
Firdausi, ashe dama kina
wannan duniyar?" Matsawa
Deedo tayi, suka rungume juna,
inda Malam ya kallesu
fuskarshi dauke da murmushin
dattako yace "to ke banda
abinki wannan ai abun farin
ciki ne, menene abun kukan?"
Nawap kallon Inna yake yana
daria, Ummi kam itama sai da
ta dan matse kwalla, nan fa
wuri ya kaure da murna, yan
tsofaffin sai nan nan suke da
Deedo, gani suke kaman
Rukayyar su ce ta dawo.
Hamdala suka yi, suka yima
Allah godia da ya dawo da
yarinyar cikin danginta. Itama
Deedo taga gata, banda
hamdala babu abinda take yi.
Godia tayi ma Allah daya sada
ta da dangin mahaifiyar ta,
jinta take tamkar yau ce ranar
da aka haifeta..
Nawap tsintar kanshi yayi a
yanayi na mugun farin ciki,
ganin Deedo cikin walwala da
jin dadin rayuwa. Sai da suka
yi sallan azahar sannan suka yi
haramar tafia, daga nan ma
gidajen kannen Ummi suka je,
duk wani dangi na nesa da na
kusa babu inda basu kai
Deedo ba, a nan ta tabbatar ma
kanta lallai ita mai gata ce,
sannan ta kara tantancewa dan
uwa rahma ne, ko ba komai
wannan soyayyar da zai nuna
maka ma wani abu ce a
rayuwa.
Wurin karfe shidda na yamma,
sannan suka dau hanyar gida,
a nan Ummi ke ce ma Nawap
"ya kamata ace Deedo tayi
jamb fa, don bana so ta bata
lokaci, so nake da result din su
ya fito ta wuce makaranta"
Sai da ya saci kallon Deedo
wadda tsananin farin cikin da
take ciki yasa sai faman
murmushi take, murmushin
yayi shima, sannan yace "nima
nayi wannan tunanin sai dai
kaman an gama jamb yanzu fa"
Ummi tace "ba naga sun bullo
da wani sabon system na
computer base ba?" Yace "haka
ne, zan bincika gobe kafin na
wuce in sha Allah" ta ansa da
"amen" inda a dai dai lokacin
kuma suka kawo gida.
The next day kamar yadda
Nawap yayi alkawari haka ya
gudanar da duk wani bincike,
inda bai bar Kaduna ba sai da
ya tabbatar ya gama mata duk
wani abu da ya kamata.
Misalin karfe biyu na rana suka
dawo gida, wanka kawai yayi,
yayi sallah ya ci abinci, sannan
ya dau hanyar Abuja, yana mai
cike da tunani da maraicin
Deedo da Umminshi..
*****
Haka rayuwa ta cigaba da
tafiyan ma Deedo cikin jin dadi
da walwala, weather garin ta
anshe ta sosai, tayi fresh tayi
das das abinta, gashi Ummi
tana kokarin koya mata
abubuwa, in ka ganta baza ka
taba gane ta ba, balle har kayi
zaton ita ce Deedon Goggo ta
kauyen Ningi..
ZUMA… 45&46
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Da dan sauri ya karasa wurin
ajiyar motocin, inda ya darzo
wata dark blue din Audi R8,
reverse yayi, sannan ya gyara
tsayuwar motar, inda su kuma
a lokaci daya suka bude suka
shiga. Deedo ce a gaba, yayin
da Ummi ta kame a owner's
corner. Wuta ya ba motar,
sannan suka lula saman titi
hankali kwance.
Tafiya suka yi mai dan nisa,
Deedo har ta fara tunanin ko
garin zasu bari. Daga karshe
dai ta ware idanunta ta cigaba
da yan kalle kalle, cikin hikima
Nawap ke satar kallonta yana
ganin yadda farin ciki ke
bayyane a fuskanta, yanayinta
kawai, zai sanar da kai cewar
bata da sauran damuwa.
Murmushi ya saki wanda bai
san lokacin da ya sufce mashi
ba, a haka suka iso main
house din su Ummi da yake
Hayin Banki. Ba tare da bata
lokaci ba ya samu wuri yayi
parking, sannan duk suka fito
suka shige ciki.
Zaune suka tarar da mai gidan
a cikin wata yar baranda, idon
shi sanye da medical glass
yana duba jaridar Daily Trust.
Inda yake zaune suka karasa
duk suka kwashi gaisuwa,
sannan suka mike gaba
dayansu zuwa cikin gidan.
Kallon Deedo yake kaman ya
taba sanin mai irin fuskarta,
sai dai bai ce komai ba har
suka shige ciki. Ita ma tunda
suka shiga take kallon dattijon
mai cikar kamala da kwarjini,
kamar shi sosai ta gani da
Nawap, sai dai yanayin tsufa
kawai da yake tattare dashi.
A palon suka samu Inna zaune
da yar casbaharta tana lazumi.
Kallo daya tai wa Deedo taji
gabanta ya fadi, a take kuma ta
yardar wa kanta cewar duk
yadda akai wannan yarinyar
jininta ce. A daddafe suka
gaisa, yau ko tsokanar da ta
saba yiwa Nawap ba ta mai ba,
cikin zakuwa ta kalli Ummi tace
"ke kam ina kika samo mai
kama da ke?" Murmushi Ummi
tayi, ba tare da bata lokaci ba
kuma ta warware masu komai
dangane da Deedo, ta kara da
cewar "amma yanzu ta dawo
nan da zama kenan in sha
Allah"
Salati Inna ta kwasa, sannan ta
saki kuka, tana cewa "yaki nan
Firdausi, ashe dama kina
wannan duniyar?" Matsawa
Deedo tayi, suka rungume juna,
inda Malam ya kallesu
fuskarshi dauke da murmushin
dattako yace "to ke banda
abinki wannan ai abun farin
ciki ne, menene abun kukan?"
Nawap kallon Inna yake yana
daria, Ummi kam itama sai da
ta dan matse kwalla, nan fa
wuri ya kaure da murna, yan
tsofaffin sai nan nan suke da
Deedo, gani suke kaman
Rukayyar su ce ta dawo.
Hamdala suka yi, suka yima
Allah godia da ya dawo da
yarinyar cikin danginta. Itama
Deedo taga gata, banda
hamdala babu abinda take yi.
Godia tayi ma Allah daya sada
ta da dangin mahaifiyar ta,
jinta take tamkar yau ce ranar
da aka haifeta..
Nawap tsintar kanshi yayi a
yanayi na mugun farin ciki,
ganin Deedo cikin walwala da
jin dadin rayuwa. Sai da suka
yi sallan azahar sannan suka yi
haramar tafia, daga nan ma
gidajen kannen Ummi suka je,
duk wani dangi na nesa da na
kusa babu inda basu kai
Deedo ba, a nan ta tabbatar ma
kanta lallai ita mai gata ce,
sannan ta kara tantancewa dan
uwa rahma ne, ko ba komai
wannan soyayyar da zai nuna
maka ma wani abu ce a
rayuwa.
Wurin karfe shidda na yamma,
sannan suka dau hanyar gida,
a nan Ummi ke ce ma Nawap
"ya kamata ace Deedo tayi
jamb fa, don bana so ta bata
lokaci, so nake da result din su
ya fito ta wuce makaranta"
Sai da ya saci kallon Deedo
wadda tsananin farin cikin da
take ciki yasa sai faman
murmushi take, murmushin
yayi shima, sannan yace "nima
nayi wannan tunanin sai dai
kaman an gama jamb yanzu fa"
Ummi tace "ba naga sun bullo
da wani sabon system na
computer base ba?" Yace "haka
ne, zan bincika gobe kafin na
wuce in sha Allah" ta ansa da
"amen" inda a dai dai lokacin
kuma suka kawo gida.
The next day kamar yadda
Nawap yayi alkawari haka ya
gudanar da duk wani bincike,
inda bai bar Kaduna ba sai da
ya tabbatar ya gama mata duk
wani abu da ya kamata.
Misalin karfe biyu na rana suka
dawo gida, wanka kawai yayi,
yayi sallah ya ci abinci, sannan
ya dau hanyar Abuja, yana mai
cike da tunani da maraicin
Deedo da Umminshi..
*****
Haka rayuwa ta cigaba da
tafiyan ma Deedo cikin jin dadi
da walwala, weather garin ta
anshe ta sosai, tayi fresh tayi
das das abinta, gashi Ummi
tana kokarin koya mata
abubuwa, in ka ganta baza ka
taba gane ta ba, balle har kayi
zaton ita ce Deedon Goggo ta
kauyen Ningi..