Sashe 19
Matar Gwamna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ranan wani Malamin addini ya fito yai bayani akan yarda da ƙaddara mai kyau ko marar kyau. Yai maganar cewa yana cikin rashin yarda da ƙaddara mutum ya fara bibiyar dalilin mutuwar wani. Gwamna Saminu Bacchi lokacinsa ne yayi shiyasa Allah ya ɗauki ransa abinda al'umma za su yi shine a cigaba da yi masa addu'a da shi da duk wanda suka riga mutuwa. Ita kuma Asiya Allah ya shiryeta.
A rana ɗaya tal sunan Asiya ya chanja zuwa maƙaryaciya. Washe gari da safe wani mawaƙi ya shiga studio ya sake waƙa yana yabon Gwamna yana aibata sunan Asiya.
Sai da Asiya ta gama shirya kayanta tsaf kafin ta wuce falon Abba, baya nan dan haka ta tura masa saƙo akan cewa zata koma gidan Baffa Malam.
Idonta yayi jaa duk sun kumbura saboda kuka. Umma ta goyi bayan shawaran data yanke data ce zata je ta zauna a gidan Baffanta har sai saura sati biyu bikinta kafin ta dawo...
***
"Your excellency inada magana"
"Bismillah Malam Baffayo"
"Yarinyar nan Asiya rayuwarta na cikin haÉ—ari"
Gwamna ya zaro ido cike da mamaki.
" na samu labari daga majiya mai ƙarfi cewa mutanen Umaru Kwom suna son kasheta saboda a tada sabuwar fitina tunda wancan ta mutu"
"How could they, ina kaji wannan magana?"
Sakatare yace " Excellency a bar kaza a cikin gashin ta"
Lokacin daya bar office kai tsaye Kachallah house ya wuce wajen Alhaji Sani.
Bayan ya yiwa Alhaji Sani bayanin da Sakatarensa ya masa sai kawai ya ga ya ɓigire da dariya har da kakkautawa.
Ya sake baki yana kallon Baffan nasa.
"Wani lokaci Saifu kaman baka san mi ake nufi da siyasa ba. Ba abin mamaki bane idan sun yi niyyar kasheta saboda wata manufarsu, sai dai duk ta inda suka ɓullo ina nan ina jiransu. Har yaushe ma Umaru ya girma da zai ce zai ja dani"
Wani abu ya daki zuciyar Saifuddeen. Ana maganar kashe ran yarinyar da bata ji ba bata gani ba amma yana dariya. Ba zai taɓa bari a hallaka rai a rikicin Gwamnatinsa ba.
"Baba ba zan bari su taɓa lafiyarta ba balle ma har su kasheta matuƙar ina raye"
Alhaji Sani ya kalli SSK da alamar tambaya a bakinsa amma bai furta ba sai yace " kenan zaka aureta?"
"Baba ban gane ba" Gwamna ya faÉ—a cikin rashin fahimtar manufar Alhaji Sani Kachallah.
"Hanya É—aya da zaka iya kareta kenan Saifu" Alhaji Sani faÉ—a yana cigaba da dariya.
WAIWAYE...
*THE GOVERNOR'S WIFE*
...... MATAR GWAMNA....
*©Azizat Hamza*
wattpad Azi_zat
Bismillahir Rahmanir Rahim
Book one
09
*WAIWAYE*
Abu ne da muka sani cewa Allah zai iya jarrabtar mu ta kowani fanni na rayuwarmu. Zai iya jarrabtarmu ta wajen dukiya, lafiya, 'ya'ya, mata, 'yanuwa, iyaye da sauransu.
Asalin iyayen Lukman Fulanin Baroroji ne wanda basa zama waje guda su jima.
Lukman yaro ne da aka haifeshi da ƙusumbi (hunchback). Yana shekara uku mahaifiyar sa ta rasu wajen haihuwa. Matar uban sa da ake kira da Gaji ta ce ba za ta iya riƙe shi ba, shiyasa Uban sa ya damƙa shi wajen Yayar mahaifiyarsa mai suna Habbi. Yana cika shekara biyar a wajenta ta ɗauke shi ta kaishi wajen Malam AbdulWahab Falke Almajiranci wanda ya kasance Kawu a wajen mijin ta.
Tunda aka damƙa Lukman wajen Malam kuwa Mahaifin sa bai taɓa waiwayan sa ba har Allah ya ɗau ran sa, shekaru biyar bayan rasuwan Asiya mahaifiyar Lukman ɗin. Itama Inna Habbin sau ɗaya ta je ta duba Lukman daga nan ba ta sake zuwa ba har rai yai halin sa.
Malam Falke ya zamewa Lukman Uwa da Uba sannan Malami. Duk cikin Almajiran Malam, Lukman ya fi ƙoƙari da hazaƙa. Ya maida hankali sosai wajen karatu. Ɗan sarari da su ke samu da sauran ke watayawa cikin gari shi yana amfani da wannan lokaci ne yai ta ƙoƙarin rubutu a Allon sa.
Malam Falke Allah bai bashi 'ya'ya dayawa ba. Yaran sa biyar ne kacal sai kuma 'ya'yan da ya ke riƙewa. Huɗu daga ciki mata ɗaya kuma namiji. Kafin a kawo masa Lukman ɗansa namiji ya jima da rasuwa, dan shekaransa shida ya rasu bayan wata ƙaramar jinya.
Dayawa mutane sukan É—auki Lukman a matsayin É—an Malam ne saboda irin kulawar da Malam ke bashi.
A hankali da ya dinga lura da baiwar karatu da Allah ya bawa Lukman sai ya zamana ya fara ba shi karatu na musamman. Duk wani ilimi da ya ke da shi to yana ƙoƙarin ya ga cewa Lukman ya samu, yana ma sa tanadin zama magajin sa. Koyaushe baya rabuwa da yiwa Lukman Du'a'ul Fahmi.
Lukman yana shekara tara yai saukan ƙur'ani (tartil) yana shekaru shahuɗu yai haddar ƙur'ani kuma cikin watanni bakwai ya rubuta ƙur'ani da ka.
A hankali ya dinga haddace manya-manyan litattafai na addini. Yana shekara shabakwai Malam ya tura shi Borno wajen wani Babban Malami. Bai dawo ba sai da yai shekaru huÉ—u a chan. A sanda ya dawo ne kuwa ya tarar da Malam ya aura masa wata 'yarsa.
Rumaysa'u wacce aka fi kira da Tabawa ita ce auta cikin 'ya'yan Malam. Ita ce kuma Allah ya jarrabce shi da ita.
Saɓanin sauran yayyanta da su ka yi karatu sosai har su ka yi sauka tun ma kafin ya aurar da su ita fir ta ƙi karatun.
Bayan nan, ƙiriniya da yawace-yawace da ta tsirfata da tara samari ya sa ya ce zai haɗata aure da wani Almajirin sa. Tabawa ta ƙeƙasa ƙasa ta ce ba za ta auri Almajiri ba. Yayi yayi da ita ta ce ba za ta aure shi ba. Ƙarshe ma ta kai ƙarar sa wajen Maigari.
Malam ya haƙura ya aura ma ta wanda ta kawo ta ce tana so. Da ke babu albarkan iyaye auren dudu wata biyar su ka yi ya rabu ta dawo gida ta fara zawarci. Kafin kace me sunan Tabawan Malam ya sake zama tamkar waƙa a wajen samari da bazawarai.
Lokacin da Malam ya ce ta fito da miji sai ta nuna Chukudi a matsayin wanda ta ke so. Kasuwanci ya kawo Chukudi garin, ɗan kuɗin da ya ke kashewa Tabawa shine ya tsole ma ta ido har ta zaɓeshi a matsayin wanda za ta aura, duk da addinin su ba ɗaya ba, al'adar su ba ɗaya ba, uwa uba ba asan minene asalin sa ba.
Wannan karan da Malam ya hanata auren sai wayan gari aka yi aka ga ta gudu daga gidan. Ita da Chukudi aka neme su a gari aka rasa. Wannan cin mutuncin har kwantar da Malam yai, kamar ma ba zai tashi ba sai kuma bayan ya sha jinyar watanni sai gashi ya samu sauƙi amma baƙin cikin da Tabawa ta ƙunsa ma sa yana nan yana cinsa, kullum addu'ar sa gareta Allah ya shiryar da ita. Ya sha tsayuwar dare akan lamarinta sai dai ita ɗin wata jarrabawa ce da Allah ya ma sa.
Shekara ɗaya da rabi kafin Tabawa ta dawo gida. Ranan da ta dawo mutanen gidan da ƙyar su ka ganeta saboda lalacewa da ta yi. Bayan ta bi Chukudi zuwa ƙauyen su ashe niyyansa shine ya tsafeta yai kuɗi da ita. Da ƙyar Allah ya kuɓutar da ita daga kaidinsa, sai dai tunda ta bar ƙauyen ta rasa gane kanta. Ta jima tana garari kafin ta samu ta warke ta dawo wajen Babanta dan ta san nan ne kawai gatan ta.
Malam ya karɓeta ne da sharaɗi guda, za ta zauna tsakani da Allah da duk wanda ya aura ma ta. Kaman da gaske ta ce ta amince.
A take ya ɗaura ma ta aure da Lukman ya kuma tura wasiƙa akan Lukman ya dawo gida idan Malaminsa ya sallameshi. Bai samu dawowa ba sai bayan wata uku.
Kafin ya dawo Malam ya gyara ma sa É—akuna biyu cikin gidansa inda anan za su zauna da Tabawa.
Lokacin da Malam ya sanar da Lukman maganar auren da yai masa ya sha mamaki sosai. Ya san halin Tabawa sarai kuma duk abinda ke faruwa babu wanda ba shi da masaniya akai. Ba wai ba zai karɓi zaɓin Malam ba ne amma yana tunanin anya kuwa Tabawa za ta zauna da shi?
Tsoronsa kuwa ya tabbata domin lokacin da Malam ya haɗa su zai mu su nasiha Tabawa ta ƙeƙasa ƙasa akan ba za ta auri Mai ƙusumbi ba. Ita duk zaman nan ta ɗauka ɗaya daga cikin manyan Almajiran Malam aka aura mata, bata san Lukman Maiƙusumbi ba ne.
"Baba ba zan zauna da Maiƙusumbi, Miskini, marar asali ba. Duk cikin Almajiranka ba wanda ba sa zuwa wajen 'yan uwan su lokaci zuwa lokaci amma wannan bai taɓa zuwa wajen na shi ba. Ƙila ma ɗan shege ne"
"Rumaysa'u!"
"Baba zan auri kowa amma banda shi Wallahi"
"Na fi ƙarfin Miskini" ta ƙara jadda masa kafin ta fice daga ɗakin Malam ɗin.
Duk ƙoƙarin da Lukman ya ke akan kada yai hawaye agaban Malam sai da hawaye su ka zubo ma sa.
Dai-dai yana gogewa da gefen hannun rigansa Malam ya ce "Lukman ka tashi ka je za a kawo maka ita yanzu"
"Malam ka yi haƙuri Dan Allah, tunda ba ta so a bari na sawwwaƙa ma ta"
Ran Malam cike da ƙuna ya ce " ka san Allah idan har Rumaysa'u ba ta karɓi auren ka ba sai na tsine mata"
Lukman ya zaro ido waje.
"Kai ne aka cuta da na haÉ—aka aure da mace kamar Rumaysa'u, na yi haka ne dan ko Allah zai shiryar min da ita ta hanyar ka"
A chan cikin gida kuwa Tabawa ta dinga faɗa wai a rasa wanda za a aura ma ta sai Maiƙusumbi. Wata Gwoggon ta da ke gidan ta fito ta dinga surfa mata masifa.
Yadda ta dinga kiranta da butulu shiyasa jikinta yai sanyi.
Duk da tarin laifuffukanta itakam ta ƙwammace ta zauna ba aure da ta auri Lukman Maiƙusumbi. Kusan shekaru biyu kawai Lukman ya ba ta. Tun suna yara ta tsaneshi. Yadda Malam ya ja shi a jiki ya maida shi ɗansa na dole ba ƙaramin ɓata ma ta rai ya ke yi ba.
A rana ɗaya tal sunan Asiya ya chanja zuwa maƙaryaciya. Washe gari da safe wani mawaƙi ya shiga studio ya sake waƙa yana yabon Gwamna yana aibata sunan Asiya.
Sai da Asiya ta gama shirya kayanta tsaf kafin ta wuce falon Abba, baya nan dan haka ta tura masa saƙo akan cewa zata koma gidan Baffa Malam.
Idonta yayi jaa duk sun kumbura saboda kuka. Umma ta goyi bayan shawaran data yanke data ce zata je ta zauna a gidan Baffanta har sai saura sati biyu bikinta kafin ta dawo...
***
"Your excellency inada magana"
"Bismillah Malam Baffayo"
"Yarinyar nan Asiya rayuwarta na cikin haÉ—ari"
Gwamna ya zaro ido cike da mamaki.
" na samu labari daga majiya mai ƙarfi cewa mutanen Umaru Kwom suna son kasheta saboda a tada sabuwar fitina tunda wancan ta mutu"
"How could they, ina kaji wannan magana?"
Sakatare yace " Excellency a bar kaza a cikin gashin ta"
Lokacin daya bar office kai tsaye Kachallah house ya wuce wajen Alhaji Sani.
Bayan ya yiwa Alhaji Sani bayanin da Sakatarensa ya masa sai kawai ya ga ya ɓigire da dariya har da kakkautawa.
Ya sake baki yana kallon Baffan nasa.
"Wani lokaci Saifu kaman baka san mi ake nufi da siyasa ba. Ba abin mamaki bane idan sun yi niyyar kasheta saboda wata manufarsu, sai dai duk ta inda suka ɓullo ina nan ina jiransu. Har yaushe ma Umaru ya girma da zai ce zai ja dani"
Wani abu ya daki zuciyar Saifuddeen. Ana maganar kashe ran yarinyar da bata ji ba bata gani ba amma yana dariya. Ba zai taɓa bari a hallaka rai a rikicin Gwamnatinsa ba.
"Baba ba zan bari su taɓa lafiyarta ba balle ma har su kasheta matuƙar ina raye"
Alhaji Sani ya kalli SSK da alamar tambaya a bakinsa amma bai furta ba sai yace " kenan zaka aureta?"
"Baba ban gane ba" Gwamna ya faÉ—a cikin rashin fahimtar manufar Alhaji Sani Kachallah.
"Hanya É—aya da zaka iya kareta kenan Saifu" Alhaji Sani faÉ—a yana cigaba da dariya.
WAIWAYE...
*THE GOVERNOR'S WIFE*
...... MATAR GWAMNA....
*©Azizat Hamza*
wattpad Azi_zat
Bismillahir Rahmanir Rahim
Book one
09
*WAIWAYE*
Abu ne da muka sani cewa Allah zai iya jarrabtar mu ta kowani fanni na rayuwarmu. Zai iya jarrabtarmu ta wajen dukiya, lafiya, 'ya'ya, mata, 'yanuwa, iyaye da sauransu.
Asalin iyayen Lukman Fulanin Baroroji ne wanda basa zama waje guda su jima.
Lukman yaro ne da aka haifeshi da ƙusumbi (hunchback). Yana shekara uku mahaifiyar sa ta rasu wajen haihuwa. Matar uban sa da ake kira da Gaji ta ce ba za ta iya riƙe shi ba, shiyasa Uban sa ya damƙa shi wajen Yayar mahaifiyarsa mai suna Habbi. Yana cika shekara biyar a wajenta ta ɗauke shi ta kaishi wajen Malam AbdulWahab Falke Almajiranci wanda ya kasance Kawu a wajen mijin ta.
Tunda aka damƙa Lukman wajen Malam kuwa Mahaifin sa bai taɓa waiwayan sa ba har Allah ya ɗau ran sa, shekaru biyar bayan rasuwan Asiya mahaifiyar Lukman ɗin. Itama Inna Habbin sau ɗaya ta je ta duba Lukman daga nan ba ta sake zuwa ba har rai yai halin sa.
Malam Falke ya zamewa Lukman Uwa da Uba sannan Malami. Duk cikin Almajiran Malam, Lukman ya fi ƙoƙari da hazaƙa. Ya maida hankali sosai wajen karatu. Ɗan sarari da su ke samu da sauran ke watayawa cikin gari shi yana amfani da wannan lokaci ne yai ta ƙoƙarin rubutu a Allon sa.
Malam Falke Allah bai bashi 'ya'ya dayawa ba. Yaran sa biyar ne kacal sai kuma 'ya'yan da ya ke riƙewa. Huɗu daga ciki mata ɗaya kuma namiji. Kafin a kawo masa Lukman ɗansa namiji ya jima da rasuwa, dan shekaransa shida ya rasu bayan wata ƙaramar jinya.
Dayawa mutane sukan É—auki Lukman a matsayin É—an Malam ne saboda irin kulawar da Malam ke bashi.
A hankali da ya dinga lura da baiwar karatu da Allah ya bawa Lukman sai ya zamana ya fara ba shi karatu na musamman. Duk wani ilimi da ya ke da shi to yana ƙoƙarin ya ga cewa Lukman ya samu, yana ma sa tanadin zama magajin sa. Koyaushe baya rabuwa da yiwa Lukman Du'a'ul Fahmi.
Lukman yana shekara tara yai saukan ƙur'ani (tartil) yana shekaru shahuɗu yai haddar ƙur'ani kuma cikin watanni bakwai ya rubuta ƙur'ani da ka.
A hankali ya dinga haddace manya-manyan litattafai na addini. Yana shekara shabakwai Malam ya tura shi Borno wajen wani Babban Malami. Bai dawo ba sai da yai shekaru huÉ—u a chan. A sanda ya dawo ne kuwa ya tarar da Malam ya aura masa wata 'yarsa.
Rumaysa'u wacce aka fi kira da Tabawa ita ce auta cikin 'ya'yan Malam. Ita ce kuma Allah ya jarrabce shi da ita.
Saɓanin sauran yayyanta da su ka yi karatu sosai har su ka yi sauka tun ma kafin ya aurar da su ita fir ta ƙi karatun.
Bayan nan, ƙiriniya da yawace-yawace da ta tsirfata da tara samari ya sa ya ce zai haɗata aure da wani Almajirin sa. Tabawa ta ƙeƙasa ƙasa ta ce ba za ta auri Almajiri ba. Yayi yayi da ita ta ce ba za ta aure shi ba. Ƙarshe ma ta kai ƙarar sa wajen Maigari.
Malam ya haƙura ya aura ma ta wanda ta kawo ta ce tana so. Da ke babu albarkan iyaye auren dudu wata biyar su ka yi ya rabu ta dawo gida ta fara zawarci. Kafin kace me sunan Tabawan Malam ya sake zama tamkar waƙa a wajen samari da bazawarai.
Lokacin da Malam ya ce ta fito da miji sai ta nuna Chukudi a matsayin wanda ta ke so. Kasuwanci ya kawo Chukudi garin, ɗan kuɗin da ya ke kashewa Tabawa shine ya tsole ma ta ido har ta zaɓeshi a matsayin wanda za ta aura, duk da addinin su ba ɗaya ba, al'adar su ba ɗaya ba, uwa uba ba asan minene asalin sa ba.
Wannan karan da Malam ya hanata auren sai wayan gari aka yi aka ga ta gudu daga gidan. Ita da Chukudi aka neme su a gari aka rasa. Wannan cin mutuncin har kwantar da Malam yai, kamar ma ba zai tashi ba sai kuma bayan ya sha jinyar watanni sai gashi ya samu sauƙi amma baƙin cikin da Tabawa ta ƙunsa ma sa yana nan yana cinsa, kullum addu'ar sa gareta Allah ya shiryar da ita. Ya sha tsayuwar dare akan lamarinta sai dai ita ɗin wata jarrabawa ce da Allah ya ma sa.
Shekara ɗaya da rabi kafin Tabawa ta dawo gida. Ranan da ta dawo mutanen gidan da ƙyar su ka ganeta saboda lalacewa da ta yi. Bayan ta bi Chukudi zuwa ƙauyen su ashe niyyansa shine ya tsafeta yai kuɗi da ita. Da ƙyar Allah ya kuɓutar da ita daga kaidinsa, sai dai tunda ta bar ƙauyen ta rasa gane kanta. Ta jima tana garari kafin ta samu ta warke ta dawo wajen Babanta dan ta san nan ne kawai gatan ta.
Malam ya karɓeta ne da sharaɗi guda, za ta zauna tsakani da Allah da duk wanda ya aura ma ta. Kaman da gaske ta ce ta amince.
A take ya ɗaura ma ta aure da Lukman ya kuma tura wasiƙa akan Lukman ya dawo gida idan Malaminsa ya sallameshi. Bai samu dawowa ba sai bayan wata uku.
Kafin ya dawo Malam ya gyara ma sa É—akuna biyu cikin gidansa inda anan za su zauna da Tabawa.
Lokacin da Malam ya sanar da Lukman maganar auren da yai masa ya sha mamaki sosai. Ya san halin Tabawa sarai kuma duk abinda ke faruwa babu wanda ba shi da masaniya akai. Ba wai ba zai karɓi zaɓin Malam ba ne amma yana tunanin anya kuwa Tabawa za ta zauna da shi?
Tsoronsa kuwa ya tabbata domin lokacin da Malam ya haɗa su zai mu su nasiha Tabawa ta ƙeƙasa ƙasa akan ba za ta auri Mai ƙusumbi ba. Ita duk zaman nan ta ɗauka ɗaya daga cikin manyan Almajiran Malam aka aura mata, bata san Lukman Maiƙusumbi ba ne.
"Baba ba zan zauna da Maiƙusumbi, Miskini, marar asali ba. Duk cikin Almajiranka ba wanda ba sa zuwa wajen 'yan uwan su lokaci zuwa lokaci amma wannan bai taɓa zuwa wajen na shi ba. Ƙila ma ɗan shege ne"
"Rumaysa'u!"
"Baba zan auri kowa amma banda shi Wallahi"
"Na fi ƙarfin Miskini" ta ƙara jadda masa kafin ta fice daga ɗakin Malam ɗin.
Duk ƙoƙarin da Lukman ya ke akan kada yai hawaye agaban Malam sai da hawaye su ka zubo ma sa.
Dai-dai yana gogewa da gefen hannun rigansa Malam ya ce "Lukman ka tashi ka je za a kawo maka ita yanzu"
"Malam ka yi haƙuri Dan Allah, tunda ba ta so a bari na sawwwaƙa ma ta"
Ran Malam cike da ƙuna ya ce " ka san Allah idan har Rumaysa'u ba ta karɓi auren ka ba sai na tsine mata"
Lukman ya zaro ido waje.
"Kai ne aka cuta da na haÉ—aka aure da mace kamar Rumaysa'u, na yi haka ne dan ko Allah zai shiryar min da ita ta hanyar ka"
A chan cikin gida kuwa Tabawa ta dinga faɗa wai a rasa wanda za a aura ma ta sai Maiƙusumbi. Wata Gwoggon ta da ke gidan ta fito ta dinga surfa mata masifa.
Yadda ta dinga kiranta da butulu shiyasa jikinta yai sanyi.
Duk da tarin laifuffukanta itakam ta ƙwammace ta zauna ba aure da ta auri Lukman Maiƙusumbi. Kusan shekaru biyu kawai Lukman ya ba ta. Tun suna yara ta tsaneshi. Yadda Malam ya ja shi a jiki ya maida shi ɗansa na dole ba ƙaramin ɓata ma ta rai ya ke yi ba.