Sashe 6
Mata Iyayen Giji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Musina:
Alwala nake ɗaurawa, ina zaune akan wani dutsi. Kukan Yarona Ƙasimu na jiyo, a zabure na miƙe, dan inje in ɗaukoshi, shekaran jiya_jiyannan ya faɗo akan maulidi (gado mai rumfa) ya dauje hanci. Salati na jiyo Baba Hauwa na rabtaɓawa harda tafa hannaye.
"Kai amma Musina baki da kunya wallahi. A gabana ina uwar mijinki kike zabura dan ɗanki kin jiyo yana kuka? Lallai Yawale ya auro mana fitsararriya, ko dama ance kinyi makarantar firamare. Amman in banda rashin neman albarka yaushe zaki yi haka a gaban Yar miji ma, ballantana har kiyi a gabana ni uwar mijinki. Kishiyarta Baba Huwaila ta amshe da cewa.
"Ke kin mance sanda Yawale ya karɓi Idi ya baki ne, wanne irin kuka da rama ne bata yi ba. Har yanzu ƙulafacin Idin take yi. Mu da sai mun haifi yara uku ana kwacewa, saika haifi na huɗune za'a barma. Haka zamu kawar da kanmu akan yarannan, har sai sun girma zasu san iyayensu na ainihi, raɓarmu ba bama bari yarannan suyu sabida kawaici irin namu na hausawa." Jin faɗowar Ƙasimu da shiɗewarshi, yasa na bar wajan a jijice, ni nama mance da su Baba Huwaila sam. A ƙasa na taddashi, hancinshi ya kuma daujewa, bakinshi sai jini yake zubarwa. Hannuna yana rawa na ɗagoshi, kujerar tsugunna na jawo na zauna a gaban kwabata, kusa da kumbunan dake ƙasa a jere hawan hawa. Nono na zura mishi, na soma shafa kanshi, sai ajjiyar zuchiya yake saukewa. Ni kuma sai hawaye nake fitarwa. Wannan wacce irin rayuwace mara ƴanci, rana zafi inuwa ƙuna. Zafi a wajan surukai, zafi a wajan miji, zafi a wajan facaloli, a hannun uban mijina kawai nake samun dama dama, sai Yayan Yawale, da ƙannen sa maza.
"Yayi tabbatacciyar maras kunya. Ni ina magana shine kika tawo kika barni a wajan ko?. Mu ada, in uwar miji na magana ma, wallahi tari wannan baki isa kiyi ba, balle ki ki tafi ki barta a tsaye tana magana, da shike iyayenki sun damƙa ragamar tarbiyyarki a hannun yahudawa marasa addini shi yasa. Amma a al'adance ke fitsararriyace ta ƙarshen zance" Da sauri na ɗago, Baba Huwaila ce riƙe da labulen ɗakina. Kasa cewa komai nayi, dana bata haƙuri zata ce na kuma yin wani babban laifin, koma tace zaginta nayi. Hawaye kawai nake zubarwa.
"Yayi kyau, sabida anyi miki faɗa, shine kika tusa yaro a gaba, kina zubar hawaye ko? To bari kiji shi kanshi Ƙasimun kina yayeshi zan karɓeshi, kiyi maza ki tashi ki koma bakin aikin girki, su A'i ai ba bayinki bane da zasu gwafe suna daka, ke kina ɗaki, kuma a gama tuwon kifi kowa bakin ci.. ." Labulen ɗakin ta saki. Wani irin kuka ne ya turniƙeni, da ƙyar na rarrashi zuchiyata nayi shiru. Ƙasimu na shinfiɗe a gadon bono. Sai naji danshin ruwa a jikina. Dana duba jikin Ƙasimu sai naga baiyi fitsari ba. Zanin na sake, na fita tsakar gida na sako alwala, amma ina cikin Sallah na kuma jin danshin ruwannan, sallamewa nayi jikina ya shiga rawa
To meye wannan, daga ina wannan ruwa? Kai bari dai in sake alwala."
Fita na kuma yi na sako alwala, a taƙaice a daddafe nayi sallah a ranar, daga jikina ruwannan yake fitowa gashi harna kuma jiƙe zanina. Kuka na rushe dani dana gane na kamu da lalurar yoyyon fitsarine, hankalina ba ƙaramin mugun tashi yayi ba.
Kuka nake rerawa mai sauti, a haka Baba Hauwa ta buɗe labule ta sameni."
"Au har yanzu kukan kike yi tabbatacciya? Zaki tashi kije ki kama musu aiki ne ko yaya, maras kunya fitararriya."
Kiyi haƙuri Baba, ganinan.
"Moin rufa mini baki, wacce bata iya shiru in babba nayi mata magana ba."
Labulen ta saki, ina jiyota tana zage_zage a tsakar gidan.
Tashi nayi na fita wajan girkin.
Amma kamun mu gama girkin, na shiga sakaki, ( bayan gida) yafi sau ashirin, fitsari nake yi sosai. Bayan mun gama girkin muka shiga rabo. Surukan gidan muka soma cirema, sai ko wacce ta ɗakko langar tuwo da miya na mijinta. Bayan mun zuzzuba musu, sai aka zuba ma yara. Muma muka zuba namu a ƙawuwar ƙwarya wacce ake kira da mazubi. Lauma biyar nayi ma tuwonnan, na tsame hannuna. A jiƙe na koma ɗakina, ina hawaye. Ƙunzugu nayi da fallen zani guda. Ina zaune ina ba Ƙasimu daya farka nono, zuchiyata sai harbawa take yi da sauri, tunanina baya jikina sam. Yawale ne ya shigo sai wani cicciza yake yi, yana ta batsewa. Langar tuwonshi na jawo mai gabanshi, da kwanon sha dana zuba mishi farau_farau a ciki.
Sannu da dawowa Yawale" A daƙile yace.
"Musina karki kuma bari su Baba suyi ƙararki akan rashin kunya da kike yi musu akan yara. Dan har yanzu ban mance fitsara da ɗiban albarkar da kika yi ba, lokacin da na tsige Idi a nono, na ba Baba ba. Kuma shima wannan kina Yayewa zan kyautar dashi, kina kuma haifa zan kuma kyautarwa. Sannan wallahi in kika sake tado mun da maganar inje Birni in dubo Idi kuma, zan iya salwantar miki da iyoyin aurenki, danni ɗiban albarkar da kike yi mun a gidannan takai intaha." Yawu na haɗiye muƙut, take jikina ya shiga kakkarwa. Dan mu matan hausawa muna tsoron saki, mace duk ƙuncin da take ciki, tana kiyaye abunda zai zamana an kai ga sakinta. Alhalin a mafi yawan lokuta sakin shine a'ala a garemu, duk da inka fita daga gidan auren naka, baka san gida wa zaka kuma faɗawa ba, tunda mazan ba tukwane bane balle ka ƙwanƙwasa ka samu gidi, amma kuma a rashin tayi ake barin arha . Ina mamakin irin wannan milkin mallakan da iyaye suke yi mana akan yaranmu, yanzu laifine dan na damu da nawa, a matsayina na Uwa? Nisawa nayi nace.
Yawale kayi haƙuri, in sha Allah ba zaka sake jin bakina akan ko wanne yarona ba. Wannan yaron kuma tuni na jima da sama zuchiyata dangana. Rayuwar shekara biyu yayi, a ƙirjina da cinyata, aka rabani dashi, daga baya ma aka kaishi almajirci na dena ganinshi baki ɗaya ma."
"Kuma in maza ɗari zaki haifa haka zasu tafi almajirci, ko kina mutuwa kina tashi ne, nj yarana bazan miƙa su hannun turawa ba, kamar yanda iyayenki su ka yi kiskuren miƙa ki, gashi a sakamakon karatun boko zaman aure, da bin miji yana shirin gagararki." kwanon tuwon ya ja ya soma kantara loma. Ni kuma sai kallonshi nake yi. Ina ina ɗigar hawaye.
Yawale." Ɗagowa yayi yace.
"Wooo haba Musina kar inci abincinne koko me kike nufi ne?. Ɗauriya na ara na yafa ma kaina, nace.
Daman gani nake kamar yoyyon fitsarine ya kamani, shine nake neman izininka, gobe zan shiga Azare inje asibiti a duba ni." Jim yayi yana kallona.
" In sha Allahu ma ba yoyyon fitsarin daya kamaki, yama akayi kika san yoyyon fitsari?"
"Yayata marigayiya Hanne, ciwon daya kasheta kenan, ita asibin binni ma Babanmu yasa aka kaita. Kuma tun la'asar nake sunturin shiga sakaki, yanzu haka maganar nan da nake yi maka, ƙunzugune a jikina" ina kaiwa nan na soma kuka.
"Ke dalla tsayar da kukannan haka, banson shirme irin naku na mata. Maganar asibiti kuma babu inda zaki wallahi. Ki shirya dai in kaiki waccan ruggar ta fulani wajan malam Sakaraɗa, ya baki magani kizo ki dafa kiyi ta sha. Ince dai babu wanda yasan halin dai da kike ciki a cikin gidannan ko?
Kai na girgiza mishi halamar eh. Sannan nace.
"Yawale kayi ma Allah ka yarda inje gida Baba ya kaini asibiti, wallahi yaya Hanne ma da maganin gargajiyar aka soma, saida ciwon ya cinyeta aka kaita asibiti dana gidan yaƙi." Tsawa ya daka mun, saida na zabura, tsabar ƙarfin tsawar.
"Tunda gidanku ne ke auranki ai dole kije gida a kai ki asibiti, wata kan kinma raina duk ƙoƙarin da nake yi a kanki ko? Maganin gargajiyar da zan karɓo miki shi ba magani bane?asibiti ko shirmen banza. Ke duk maganin gargajiyar mu ka sha, gamu gadagau da lafiyar mu, wallahi daga nan zan iya zuwa har Azare da bala'in gudu, tsabar lafiya, kuma ba'a taɓa kai zuriyar gidanmu asibiti ba, a kanki baki isa a soma ba, uwar iya. Dan haka na gargajiya zaki yi. Kice ciwon ma gado ne." Yana kaiwa nan ya wanke hannunshi, ya haye maulidi. Nafi kwatan dare a zaune a wajan ina dubka da warwara, maganganun da Yawale ya yaɓa mun sai yawo suke a kaina. Ƙunzugun jikina ya jiƙe sharab har tsungulata yake yi. Sake ƙunzugun nayi, wanda na cire kuma nasa a bokitin da nake wanke kayan ƙunzugun Ƙasimu, na tura a ƙarƙashin maulidi, na jawo matashin kai na yar a ƙasa. Na jima banyi bacci ba. Ina ganin lokacin da Yawale yake zuwa zance gidanmu a idanuna. Da irin kalamai tausasan da yake jifana dashi. Ko a gida aka ɓata mun rai, da zaran Yawale yazo zance, zai yaye mun dukkannin damuwa, saiya tabbatar ya sani farin ciki. Ashe yaudarace kawai. Yau gani a cikin halin da nake buƙatar tsantsar kulawa daga wajan Yawale, amma yayi kwanciyarshi yayi burus dani, sai munshari yake ja. Tunda na Auri Yawale muka gama cin amarcinmu salamun_salamun, ban kuma samun farin cikin daya haura mako ba. Kullum a cikin taraddadi gami da taka tsan_tsan nake, dan ɗan motsi kaɗan zakayi, saiya zama gagarumin laifi, a wajan miji, ko iyayenshi.
MRS BUKHARI
INA MIƘA GODIYA TA DA DUKKAN MASOYA WANNAN LITTAFI NAWA. HAƘIƘA YAU NAGA RUWAN SOYAYYA. NA AMSA WAYA TAFI SAU GOMA, ANA TAMBAYATA YAU BANYI POSTING BA. NAGODE DA SOYAYYA.
AKWAI WATA BAIWAR ALLAH DATA SAKA MUN SAƘO A MOTA DAGA NIGER ZUWA INDA NAKE RIVERS STATE. DUK AKAN WANNAN LITTAFI. NAGODE SOSAI. DAMA DANA BUƊE INGA.....🤣
Gawurtattu uku,zasu buɗe aji na musamman da azumi,don koyar da girke girke na musamman na azumi don kun san mu mata ƴan adone,wajen yin girki in akace baki iya girki ba to tabbas mijinki fa kullum yana kan hanyar yawon restuarent, sannan idanuwansa suna kan ƴammata saboda ya samu sarauniyar girki, kada ki bari a barki a baya don gwangwaje me gidanki.
Domin nema ƙarin bayani,sai ku tuntuɓi waɗannan numbobin👇🏻👇🏻
07068606171
08104335144
08179523215
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
Alwala nake ɗaurawa, ina zaune akan wani dutsi. Kukan Yarona Ƙasimu na jiyo, a zabure na miƙe, dan inje in ɗaukoshi, shekaran jiya_jiyannan ya faɗo akan maulidi (gado mai rumfa) ya dauje hanci. Salati na jiyo Baba Hauwa na rabtaɓawa harda tafa hannaye.
"Kai amma Musina baki da kunya wallahi. A gabana ina uwar mijinki kike zabura dan ɗanki kin jiyo yana kuka? Lallai Yawale ya auro mana fitsararriya, ko dama ance kinyi makarantar firamare. Amman in banda rashin neman albarka yaushe zaki yi haka a gaban Yar miji ma, ballantana har kiyi a gabana ni uwar mijinki. Kishiyarta Baba Huwaila ta amshe da cewa.
"Ke kin mance sanda Yawale ya karɓi Idi ya baki ne, wanne irin kuka da rama ne bata yi ba. Har yanzu ƙulafacin Idin take yi. Mu da sai mun haifi yara uku ana kwacewa, saika haifi na huɗune za'a barma. Haka zamu kawar da kanmu akan yarannan, har sai sun girma zasu san iyayensu na ainihi, raɓarmu ba bama bari yarannan suyu sabida kawaici irin namu na hausawa." Jin faɗowar Ƙasimu da shiɗewarshi, yasa na bar wajan a jijice, ni nama mance da su Baba Huwaila sam. A ƙasa na taddashi, hancinshi ya kuma daujewa, bakinshi sai jini yake zubarwa. Hannuna yana rawa na ɗagoshi, kujerar tsugunna na jawo na zauna a gaban kwabata, kusa da kumbunan dake ƙasa a jere hawan hawa. Nono na zura mishi, na soma shafa kanshi, sai ajjiyar zuchiya yake saukewa. Ni kuma sai hawaye nake fitarwa. Wannan wacce irin rayuwace mara ƴanci, rana zafi inuwa ƙuna. Zafi a wajan surukai, zafi a wajan miji, zafi a wajan facaloli, a hannun uban mijina kawai nake samun dama dama, sai Yayan Yawale, da ƙannen sa maza.
"Yayi tabbatacciyar maras kunya. Ni ina magana shine kika tawo kika barni a wajan ko?. Mu ada, in uwar miji na magana ma, wallahi tari wannan baki isa kiyi ba, balle ki ki tafi ki barta a tsaye tana magana, da shike iyayenki sun damƙa ragamar tarbiyyarki a hannun yahudawa marasa addini shi yasa. Amma a al'adance ke fitsararriyace ta ƙarshen zance" Da sauri na ɗago, Baba Huwaila ce riƙe da labulen ɗakina. Kasa cewa komai nayi, dana bata haƙuri zata ce na kuma yin wani babban laifin, koma tace zaginta nayi. Hawaye kawai nake zubarwa.
"Yayi kyau, sabida anyi miki faɗa, shine kika tusa yaro a gaba, kina zubar hawaye ko? To bari kiji shi kanshi Ƙasimun kina yayeshi zan karɓeshi, kiyi maza ki tashi ki koma bakin aikin girki, su A'i ai ba bayinki bane da zasu gwafe suna daka, ke kina ɗaki, kuma a gama tuwon kifi kowa bakin ci.. ." Labulen ɗakin ta saki. Wani irin kuka ne ya turniƙeni, da ƙyar na rarrashi zuchiyata nayi shiru. Ƙasimu na shinfiɗe a gadon bono. Sai naji danshin ruwa a jikina. Dana duba jikin Ƙasimu sai naga baiyi fitsari ba. Zanin na sake, na fita tsakar gida na sako alwala, amma ina cikin Sallah na kuma jin danshin ruwannan, sallamewa nayi jikina ya shiga rawa
To meye wannan, daga ina wannan ruwa? Kai bari dai in sake alwala."
Fita na kuma yi na sako alwala, a taƙaice a daddafe nayi sallah a ranar, daga jikina ruwannan yake fitowa gashi harna kuma jiƙe zanina. Kuka na rushe dani dana gane na kamu da lalurar yoyyon fitsarine, hankalina ba ƙaramin mugun tashi yayi ba.
Kuka nake rerawa mai sauti, a haka Baba Hauwa ta buɗe labule ta sameni."
"Au har yanzu kukan kike yi tabbatacciya? Zaki tashi kije ki kama musu aiki ne ko yaya, maras kunya fitararriya."
Kiyi haƙuri Baba, ganinan.
"Moin rufa mini baki, wacce bata iya shiru in babba nayi mata magana ba."
Labulen ta saki, ina jiyota tana zage_zage a tsakar gidan.
Tashi nayi na fita wajan girkin.
Amma kamun mu gama girkin, na shiga sakaki, ( bayan gida) yafi sau ashirin, fitsari nake yi sosai. Bayan mun gama girkin muka shiga rabo. Surukan gidan muka soma cirema, sai ko wacce ta ɗakko langar tuwo da miya na mijinta. Bayan mun zuzzuba musu, sai aka zuba ma yara. Muma muka zuba namu a ƙawuwar ƙwarya wacce ake kira da mazubi. Lauma biyar nayi ma tuwonnan, na tsame hannuna. A jiƙe na koma ɗakina, ina hawaye. Ƙunzugu nayi da fallen zani guda. Ina zaune ina ba Ƙasimu daya farka nono, zuchiyata sai harbawa take yi da sauri, tunanina baya jikina sam. Yawale ne ya shigo sai wani cicciza yake yi, yana ta batsewa. Langar tuwonshi na jawo mai gabanshi, da kwanon sha dana zuba mishi farau_farau a ciki.
Sannu da dawowa Yawale" A daƙile yace.
"Musina karki kuma bari su Baba suyi ƙararki akan rashin kunya da kike yi musu akan yara. Dan har yanzu ban mance fitsara da ɗiban albarkar da kika yi ba, lokacin da na tsige Idi a nono, na ba Baba ba. Kuma shima wannan kina Yayewa zan kyautar dashi, kina kuma haifa zan kuma kyautarwa. Sannan wallahi in kika sake tado mun da maganar inje Birni in dubo Idi kuma, zan iya salwantar miki da iyoyin aurenki, danni ɗiban albarkar da kike yi mun a gidannan takai intaha." Yawu na haɗiye muƙut, take jikina ya shiga kakkarwa. Dan mu matan hausawa muna tsoron saki, mace duk ƙuncin da take ciki, tana kiyaye abunda zai zamana an kai ga sakinta. Alhalin a mafi yawan lokuta sakin shine a'ala a garemu, duk da inka fita daga gidan auren naka, baka san gida wa zaka kuma faɗawa ba, tunda mazan ba tukwane bane balle ka ƙwanƙwasa ka samu gidi, amma kuma a rashin tayi ake barin arha . Ina mamakin irin wannan milkin mallakan da iyaye suke yi mana akan yaranmu, yanzu laifine dan na damu da nawa, a matsayina na Uwa? Nisawa nayi nace.
Yawale kayi haƙuri, in sha Allah ba zaka sake jin bakina akan ko wanne yarona ba. Wannan yaron kuma tuni na jima da sama zuchiyata dangana. Rayuwar shekara biyu yayi, a ƙirjina da cinyata, aka rabani dashi, daga baya ma aka kaishi almajirci na dena ganinshi baki ɗaya ma."
"Kuma in maza ɗari zaki haifa haka zasu tafi almajirci, ko kina mutuwa kina tashi ne, nj yarana bazan miƙa su hannun turawa ba, kamar yanda iyayenki su ka yi kiskuren miƙa ki, gashi a sakamakon karatun boko zaman aure, da bin miji yana shirin gagararki." kwanon tuwon ya ja ya soma kantara loma. Ni kuma sai kallonshi nake yi. Ina ina ɗigar hawaye.
Yawale." Ɗagowa yayi yace.
"Wooo haba Musina kar inci abincinne koko me kike nufi ne?. Ɗauriya na ara na yafa ma kaina, nace.
Daman gani nake kamar yoyyon fitsarine ya kamani, shine nake neman izininka, gobe zan shiga Azare inje asibiti a duba ni." Jim yayi yana kallona.
" In sha Allahu ma ba yoyyon fitsarin daya kamaki, yama akayi kika san yoyyon fitsari?"
"Yayata marigayiya Hanne, ciwon daya kasheta kenan, ita asibin binni ma Babanmu yasa aka kaita. Kuma tun la'asar nake sunturin shiga sakaki, yanzu haka maganar nan da nake yi maka, ƙunzugune a jikina" ina kaiwa nan na soma kuka.
"Ke dalla tsayar da kukannan haka, banson shirme irin naku na mata. Maganar asibiti kuma babu inda zaki wallahi. Ki shirya dai in kaiki waccan ruggar ta fulani wajan malam Sakaraɗa, ya baki magani kizo ki dafa kiyi ta sha. Ince dai babu wanda yasan halin dai da kike ciki a cikin gidannan ko?
Kai na girgiza mishi halamar eh. Sannan nace.
"Yawale kayi ma Allah ka yarda inje gida Baba ya kaini asibiti, wallahi yaya Hanne ma da maganin gargajiyar aka soma, saida ciwon ya cinyeta aka kaita asibiti dana gidan yaƙi." Tsawa ya daka mun, saida na zabura, tsabar ƙarfin tsawar.
"Tunda gidanku ne ke auranki ai dole kije gida a kai ki asibiti, wata kan kinma raina duk ƙoƙarin da nake yi a kanki ko? Maganin gargajiyar da zan karɓo miki shi ba magani bane?asibiti ko shirmen banza. Ke duk maganin gargajiyar mu ka sha, gamu gadagau da lafiyar mu, wallahi daga nan zan iya zuwa har Azare da bala'in gudu, tsabar lafiya, kuma ba'a taɓa kai zuriyar gidanmu asibiti ba, a kanki baki isa a soma ba, uwar iya. Dan haka na gargajiya zaki yi. Kice ciwon ma gado ne." Yana kaiwa nan ya wanke hannunshi, ya haye maulidi. Nafi kwatan dare a zaune a wajan ina dubka da warwara, maganganun da Yawale ya yaɓa mun sai yawo suke a kaina. Ƙunzugun jikina ya jiƙe sharab har tsungulata yake yi. Sake ƙunzugun nayi, wanda na cire kuma nasa a bokitin da nake wanke kayan ƙunzugun Ƙasimu, na tura a ƙarƙashin maulidi, na jawo matashin kai na yar a ƙasa. Na jima banyi bacci ba. Ina ganin lokacin da Yawale yake zuwa zance gidanmu a idanuna. Da irin kalamai tausasan da yake jifana dashi. Ko a gida aka ɓata mun rai, da zaran Yawale yazo zance, zai yaye mun dukkannin damuwa, saiya tabbatar ya sani farin ciki. Ashe yaudarace kawai. Yau gani a cikin halin da nake buƙatar tsantsar kulawa daga wajan Yawale, amma yayi kwanciyarshi yayi burus dani, sai munshari yake ja. Tunda na Auri Yawale muka gama cin amarcinmu salamun_salamun, ban kuma samun farin cikin daya haura mako ba. Kullum a cikin taraddadi gami da taka tsan_tsan nake, dan ɗan motsi kaɗan zakayi, saiya zama gagarumin laifi, a wajan miji, ko iyayenshi.
MRS BUKHARI
INA MIƘA GODIYA TA DA DUKKAN MASOYA WANNAN LITTAFI NAWA. HAƘIƘA YAU NAGA RUWAN SOYAYYA. NA AMSA WAYA TAFI SAU GOMA, ANA TAMBAYATA YAU BANYI POSTING BA. NAGODE DA SOYAYYA.
AKWAI WATA BAIWAR ALLAH DATA SAKA MUN SAƘO A MOTA DAGA NIGER ZUWA INDA NAKE RIVERS STATE. DUK AKAN WANNAN LITTAFI. NAGODE SOSAI. DAMA DANA BUƊE INGA.....🤣
Gawurtattu uku,zasu buɗe aji na musamman da azumi,don koyar da girke girke na musamman na azumi don kun san mu mata ƴan adone,wajen yin girki in akace baki iya girki ba to tabbas mijinki fa kullum yana kan hanyar yawon restuarent, sannan idanuwansa suna kan ƴammata saboda ya samu sarauniyar girki, kada ki bari a barki a baya don gwangwaje me gidanki.
Domin nema ƙarin bayani,sai ku tuntuɓi waɗannan numbobin👇🏻👇🏻
07068606171
08104335144
08179523215
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻