Sashe 39
Mata Iyayen Giji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallonsu suka dawo dashi gareni. Ruwan hawayene ke zuba a idanuna. Da sauri Idi ya iso gareni.
"Uwo ki dena zubar da hawayenki dan Allah, hawayenki suna da tsada, lokacin farin cikinkine yanzu." Murmusawa nayi nace.
"Allah yayi maka albarka. Ka kyauta sosai akan abinda ka aikata. Wannan zai zama izina ga matan da suka washi iyayen mijinsu. Har wasu matan ke kiranmu da olsa, wasu kuma suce mana hawan jini. Hadiza ke uwace, ga Ƙasimu kin haifa namiji. Ya zakiji a lokacin da ƙarfinki ya ƙare, matar Ƙasimunki tace bazata iya zama dake ba? Bana fatan ki ɗanɗani wannan irin ɗacin da kika lasa ma harshena. Ni da ɗana yau yayi girma, da arzikin da wai akeson a rabani dashi kuma? Tun yana yaro ake raba mu. A yanzu kuwa sai dai mutuwa ta raba mu. Bari in baki labarin wuyar da nasha tun daga renon cikinshi har zuwa haihuwar tashi. Tun cikin na da wats biyu, na shiga wani irin zazzafan lauyayin da ko ruwa na haɗiya, saiya dawo. Na rame na kwanjame, jinina yai ƙasa sosai a jikina. Saida aka kaini asibiti. Likita ya lissafo mana abubbuwan da zasu ƙaramun jini, danginsu alaiyawo, wake, hanta, tumatur da gurji. Na dawo gida, kullum a kwance nake wuni, har cikina ya tsufa. Naƙuda kuwa, tunda na soma ran alhamis a tsatstsaye, saida nakai ranar sati na haihu da yamma. Koda na haifeshi, kwanana uku bana gane kowa, banda jini da naita zubarwa. Sannan nazo na shayar dashi, na goyashi, yai mun kashi yaimun fitsari duk, in baida lafiya in kasa bacci, farin cikinshi shine nawa. Amman yau shine ke da bakinki kike cewa bazaki iya zama dani ba? Ai duk wani ɗan halas dole ya sakeki Hadiza" Hawayena na sharce. Hadiza ta zube a gabana ta kama ƙafafuna tace.
"Haƙiƙa na tabka babban kuskuren da bazan iya cewa meya shigeni na aikata hakan ba. Ki yafe mun Uwo, kuma nayi alƙawarin zan kula dake fiye da yanda zan kula da kaina." Dubanta ta mayar kan Idi wanda yake kusa dani.
"Kaimun afuwa, sharrin shaiɗanne wallahi, zan riƙe Uwo da daraja da kima sosai, kaimun rai in rayu tare da yarana." Idi yana hawaye yace.
"Wallahi sonki ne ya fice fut a cikin raina, banjin zan iya ci gaba da zama dake, sabida kin kushe dangina." Murmusawa nayi nace
Kayi haƙuri ka dawo da'ita ɗakinta. Banason duniya ta buga dani cikin iyayen mijin da suke takura ma surukansu. Ni ba zanyi hakan ba, anyi mini nasan zafin shi. Na umarceka daka dawo da matarka." Juyawa nayi na fice a ɗakin, na ɗaura alwala na shige ɗaki abuna." Abubbuwan farin ciki da dama sun faffaru. Hadiza kula dani take yi sosai. Harma nakan rasa da ita da Idi wa yafi kulawa danine wai." Su Alawiyya, ita ta samu gurbin aiki a asibitin juth wanda yake kasuwar taminus, Zubaida kuma ta samu gurbin karatunta a jami'ar jos. Idi ya sani a islamiyya ta matan aure mai suna UMMAHAT wacce take cikin babbar makarantar arabiyya da boko Al iman, suna da reshuna a gari_gari. Daga ajin farko na soma karatuna. Sai a lokacin nake jin wani haske na shiga rayuwata. A koda yaushe da littattafan karatu zaka ganni a hannuna.
Bayan wasu shekaru. Yarana duk sunyi Aure, Idi ya sayi gidan da suka haɗa katanga tare, an haɗeshi ya zama gida ɗaya. Su Mustapha da matanshi suna zaune a gefen. Matansu sai suka shiga gasar kyautatamun, ko wacce tanason ta samu fada a wajena, ko dan mijinta ya darajata. ( KU SANI DUK SURUKAR DATA KE WULAƘANTA UWAR MIJINTA. TAGA WANNAN UWAR BATA DA DARAJA NE A WAJAN ƊANTA. IN KUWA YA NUNA MA MATARSHI UWARSHI DA DANGINSHI ZAI IYA KOMAI DAN GANIN FARIN CIKINSU. YA ZAME MATA DOLE TA GIRMAMA UWAR MIJINNAN, DA DANGIN MIJIN. MUMA IYAYE MU KAME KAWUNANMU, DAN WATARAN MU KE WATSAR DA KANMU. MUITA SAKA MA MATAN YARANMU IDANU. IYAYE MU KULA) mun shiga jarabawrmu ta ƙarshe wacce ake kira Zariya. Wannan takadda ita zata baka lasisin shiga jami'a bangaren islamic studies. A lokacin ne Jamilu ya dawo daga ƙauye yake shaida mana Yawale ba Lafiya, yana asibitin Bauchi. Ba shiri muka yi mota biyu, muka nufi Bauchi. Dan yanzu arziki yaci uban na da, Ƙaton suto su Idi ke dashi na kayan hatsi. Shinkafar hausa, shinkafar tuwo, dawa, masara, gero, riɗi, duk suna dashi. Sun kuma dage da noma sosai, a ƙauye, sun mallaki gonakai, da ma'aikata masu yawa. Da tambaya muka isa ɗakin da Yawale yake kwance. Kumatu tana ganinmu ta sauke kanta ƙasa. Ta rame ta kuma tsofewa, ga su Saminu, da, Sauma'iyya da Zakiya duk suna asibitin. Zakiya dukta tsofe tayi zuru_zuru da'ita. Sauma'iyya kuma dukta tsotse ta tsomare, rashin Aure yayi mata illa, kamar kanta ya ɗan taɓu, dan naga tana wani abu kamar ba mai cikakken hankali ba. Yawale na zuba ma idanu a kwance babu riga, ga mamanshi ya kumbura har gefen maman ya fashe, yana zubar da ɗiwa, da jini jini. Idi yace.
"Baba Kumatu me likitan yace ne?" Tama kasa magana sam, sai Saminu ne yace.
"Mu dai tunda muka zo ba wani bayani da suka yi mana. Likitoci dai sunata zuwa suna gwada maman nashi, amman har zuwa yanzu basu ce komai ba." Jamilu yace.
"Yaya Idi muje mu samu likitocin muji daga bakinsu." Haɗe kai suka yi mazan suka fice. Wata ma'aikaciyar jinya ce, tace mu je daga waje mu jira. Fita muka yi, Alawiyya taje bayan mota ta ɗakko ƙatuwar dadduma ta shinfiɗa mana. Nace da Zubaida.
"Kuje ku ɗakko abinci a bayan motar Jamilu maza. Kumatu gafa surukanki. Wannan matar jamilu ce, wannan matar Mustafa, Ƙasimu matarshi na gida, ita da matar Yayansu, amman zasu tawo in sha Allah. Kumatu tace.
"Au yanzu yarannan ne suka zama ƴan burni haka lallai kam yara Allah yayi albarka. Ni kinga Zakiya, karayar arzikice ta samu mijin nata, aikin komai bayayi. Ita ke wankau da surfau take ciyar da kanta, da yara. Gashi ma ciwon hawan jinine da'ita. Sauma'iyya kuwa muna nan tare, har yanzu miji bai samu ba. Wannan ɗan banzan yaje ya gama rayuwar gidan kaso, ya dawo. Wallahi maganar da yake ɗebowa na da ba komai bane." Murmushi nayi nace.
"Adda'a zaki dage kiyi ta binsu dashi, Allah ya shiryesu. Ita Sauma'iyya in zamu tafi saiki bani ita, in sata a makarantar addini, wala Allah ta samu miji a birni tayi aurenta." Kumatu tayi ta kuka tana share majina.
Ɗakin likita:
MRS BUKHARI
[08/04, 19:57] Mrs Bukhari: GAWURTATTU UKU
MRS BUKHARI
LAMBA TA ASHIRIN DA TAKWAS:
JOS:
"Uwo wannan shine gidana, ga shaguna guda biyu" Farin ciki ne ya lulluɓemun zuchiyata, nace dashi.
Masha Allah, Allah ya ƙara maka buɗi da ɗaukaka"
"Ameen Uwona" Fitowa mukayi dukka, Idi na riƙe da jakar kayana. Ɗan mabuɗi yasa ya buɗe ƙofar. Yai mana iso zuwa ciki. Tsakar gidan tasha sumunti luwal_luwal gwanin sha'awa. Tabarma ya shinfiɗa mana daga inuwa, ya kawo mana ruwa.
"Uwo bari in kira Hadiza ta dawo gida, bikin ƙanwarta akeyi shine ta kwashi yaran suka koma can gidan nasu. Gobe za'a gama bikin."
A'a barta tana cikin ƴan uwanta tana jin daɗinta. Allah ya kaimu goben."
"To shikenan, zanje anjima in ƙarɓo ɗan mabuɗin madafi. Amman kafinnan bari in ɓalle ɗakinta, inason in mayar mata da kayanta wancan ɗaƙin. Sabida wanda take ciki yafi wancan ɗin girma." Yaƙi ya barni ince komai. Shi da Ƙasimu, da Mustapha sukaita jigilar fito da kayan jeren Hadiza, suna jera mata a ɗakin dake can cikin gida. Bayan sun gama kuma, ya fita ya jibgo mana naman balagu da masa, da lemon ƙwali." Ya ja Ƙasimu, da Mustapha zuwa kasuwa. Bayan kamar awa guda, ina sallah sai gasu sun shigo, da kaya kici_kici. Harda su gado da katifa. Haka akaita shiga da kaya harda kujeru masu kyau. Saida suka kintsa komai, sannan Idi yai mana iso zuwa ɗakin. Kafet malala a ɗakin ga taushi, komai sabo aka saka, ga gadona babba sosai, da sababbin zannuwan gado da bargo a ƙatuwar leda.
"Uwo nanne ɗakinku da su Alawiyya. Nan ɗin yafi dacewa dake. Can ɗin ƙananune, kuma falle falle ne guda uku. To na bata biyu, yaranta na basu ɗaya. Ki sake a nan, ga makewayi a ciki kinga kina buƙatar sirri, tunda da suruka zaki zauna."
Amman ai daka barta a ɗakinta, ni falle ɗayan ɗaƙi ya isheni, a falle ɗaya na gama rayuwar ƙauye. Tun daga ɗakin mahaifiyata, har zuwa gidan aurena". Murmusawa yayi yace.
"Nan gidan ɗankine, wanda kika sha azaba wajan rainon cikinshi da haihuwarshi. Uwo bana manta sanda nake samunki a bayan gonar mai gari, ina gani kullum sai kinyi kuka in zamu rabu. Haka sanda Baba ya koreni, ina jiyo sautin kukanki. Inna barki a ɗaki ɗaya matata na ɗaki biyu da makewayi. Tamkar ban darajaki a matsayinki na jajirtacciyar uwa ba. Uwo aljanna ba'a ƙarƙashin matata take ba. A wajanki nake neman albarka" munyi kuka sosai dani da yaran duka. Haƙiƙa Idi ya haifu ya cika ɗa." Fita suka yi da Ƙasimu suka gyara shagon waje tsab, Ƙasimu ya shigo gida. Shi kuma yace a sanar mun yaje karɓo ɗan mabuɗin madafi."
Idi:
Kai tsaye gidan surukan nashi ya shiga, sabida shi ɗane a gidan. Iyaye kaɗai ya tarar a gidan. A gaban mahaifiyar Hadiza ya tsugunna, aka gaggsisa, yai musu Allah ya sanya alkhairi tare da jaddada musu uzirin daya hanashi halartar ɗaurin aure."
"Yanzu haka ma, ita mahaifiyar tamu, na tawo da'ita da ƙannena zamu zauna tare." Mahaifiyar Hadiza tace.
"Ka kuwa kyauta, Allah yayi albarka. In suka huta, muka gama sallamar baƙi muma, zamu zo a ga juna"
"Zamu zo ma Mama, tanason tazo tayi godiya bisa karamcin da akai mata. Hadizan basa nan ko?"
"Sun tafi gidan Amarya jere, shi yasa kaga gidan ya yashe ba kowa."
"Ta bar ɗan mabuɗi a nan, ko dashi ta tafi?" Mahaifiyar Hadiza tace.
"Bari in ɗakko maka jakarta ka duba ko zaka samu" Ɗakko mai jakar tayi ya duba, ya ɗauƙa, yaima iyayen Hadiza alkhairi, tare dayi musu sallama."
"Uwo ki dena zubar da hawayenki dan Allah, hawayenki suna da tsada, lokacin farin cikinkine yanzu." Murmusawa nayi nace.
"Allah yayi maka albarka. Ka kyauta sosai akan abinda ka aikata. Wannan zai zama izina ga matan da suka washi iyayen mijinsu. Har wasu matan ke kiranmu da olsa, wasu kuma suce mana hawan jini. Hadiza ke uwace, ga Ƙasimu kin haifa namiji. Ya zakiji a lokacin da ƙarfinki ya ƙare, matar Ƙasimunki tace bazata iya zama dake ba? Bana fatan ki ɗanɗani wannan irin ɗacin da kika lasa ma harshena. Ni da ɗana yau yayi girma, da arzikin da wai akeson a rabani dashi kuma? Tun yana yaro ake raba mu. A yanzu kuwa sai dai mutuwa ta raba mu. Bari in baki labarin wuyar da nasha tun daga renon cikinshi har zuwa haihuwar tashi. Tun cikin na da wats biyu, na shiga wani irin zazzafan lauyayin da ko ruwa na haɗiya, saiya dawo. Na rame na kwanjame, jinina yai ƙasa sosai a jikina. Saida aka kaini asibiti. Likita ya lissafo mana abubbuwan da zasu ƙaramun jini, danginsu alaiyawo, wake, hanta, tumatur da gurji. Na dawo gida, kullum a kwance nake wuni, har cikina ya tsufa. Naƙuda kuwa, tunda na soma ran alhamis a tsatstsaye, saida nakai ranar sati na haihu da yamma. Koda na haifeshi, kwanana uku bana gane kowa, banda jini da naita zubarwa. Sannan nazo na shayar dashi, na goyashi, yai mun kashi yaimun fitsari duk, in baida lafiya in kasa bacci, farin cikinshi shine nawa. Amman yau shine ke da bakinki kike cewa bazaki iya zama dani ba? Ai duk wani ɗan halas dole ya sakeki Hadiza" Hawayena na sharce. Hadiza ta zube a gabana ta kama ƙafafuna tace.
"Haƙiƙa na tabka babban kuskuren da bazan iya cewa meya shigeni na aikata hakan ba. Ki yafe mun Uwo, kuma nayi alƙawarin zan kula dake fiye da yanda zan kula da kaina." Dubanta ta mayar kan Idi wanda yake kusa dani.
"Kaimun afuwa, sharrin shaiɗanne wallahi, zan riƙe Uwo da daraja da kima sosai, kaimun rai in rayu tare da yarana." Idi yana hawaye yace.
"Wallahi sonki ne ya fice fut a cikin raina, banjin zan iya ci gaba da zama dake, sabida kin kushe dangina." Murmusawa nayi nace
Kayi haƙuri ka dawo da'ita ɗakinta. Banason duniya ta buga dani cikin iyayen mijin da suke takura ma surukansu. Ni ba zanyi hakan ba, anyi mini nasan zafin shi. Na umarceka daka dawo da matarka." Juyawa nayi na fice a ɗakin, na ɗaura alwala na shige ɗaki abuna." Abubbuwan farin ciki da dama sun faffaru. Hadiza kula dani take yi sosai. Harma nakan rasa da ita da Idi wa yafi kulawa danine wai." Su Alawiyya, ita ta samu gurbin aiki a asibitin juth wanda yake kasuwar taminus, Zubaida kuma ta samu gurbin karatunta a jami'ar jos. Idi ya sani a islamiyya ta matan aure mai suna UMMAHAT wacce take cikin babbar makarantar arabiyya da boko Al iman, suna da reshuna a gari_gari. Daga ajin farko na soma karatuna. Sai a lokacin nake jin wani haske na shiga rayuwata. A koda yaushe da littattafan karatu zaka ganni a hannuna.
Bayan wasu shekaru. Yarana duk sunyi Aure, Idi ya sayi gidan da suka haɗa katanga tare, an haɗeshi ya zama gida ɗaya. Su Mustapha da matanshi suna zaune a gefen. Matansu sai suka shiga gasar kyautatamun, ko wacce tanason ta samu fada a wajena, ko dan mijinta ya darajata. ( KU SANI DUK SURUKAR DATA KE WULAƘANTA UWAR MIJINTA. TAGA WANNAN UWAR BATA DA DARAJA NE A WAJAN ƊANTA. IN KUWA YA NUNA MA MATARSHI UWARSHI DA DANGINSHI ZAI IYA KOMAI DAN GANIN FARIN CIKINSU. YA ZAME MATA DOLE TA GIRMAMA UWAR MIJINNAN, DA DANGIN MIJIN. MUMA IYAYE MU KAME KAWUNANMU, DAN WATARAN MU KE WATSAR DA KANMU. MUITA SAKA MA MATAN YARANMU IDANU. IYAYE MU KULA) mun shiga jarabawrmu ta ƙarshe wacce ake kira Zariya. Wannan takadda ita zata baka lasisin shiga jami'a bangaren islamic studies. A lokacin ne Jamilu ya dawo daga ƙauye yake shaida mana Yawale ba Lafiya, yana asibitin Bauchi. Ba shiri muka yi mota biyu, muka nufi Bauchi. Dan yanzu arziki yaci uban na da, Ƙaton suto su Idi ke dashi na kayan hatsi. Shinkafar hausa, shinkafar tuwo, dawa, masara, gero, riɗi, duk suna dashi. Sun kuma dage da noma sosai, a ƙauye, sun mallaki gonakai, da ma'aikata masu yawa. Da tambaya muka isa ɗakin da Yawale yake kwance. Kumatu tana ganinmu ta sauke kanta ƙasa. Ta rame ta kuma tsofewa, ga su Saminu, da, Sauma'iyya da Zakiya duk suna asibitin. Zakiya dukta tsofe tayi zuru_zuru da'ita. Sauma'iyya kuma dukta tsotse ta tsomare, rashin Aure yayi mata illa, kamar kanta ya ɗan taɓu, dan naga tana wani abu kamar ba mai cikakken hankali ba. Yawale na zuba ma idanu a kwance babu riga, ga mamanshi ya kumbura har gefen maman ya fashe, yana zubar da ɗiwa, da jini jini. Idi yace.
"Baba Kumatu me likitan yace ne?" Tama kasa magana sam, sai Saminu ne yace.
"Mu dai tunda muka zo ba wani bayani da suka yi mana. Likitoci dai sunata zuwa suna gwada maman nashi, amman har zuwa yanzu basu ce komai ba." Jamilu yace.
"Yaya Idi muje mu samu likitocin muji daga bakinsu." Haɗe kai suka yi mazan suka fice. Wata ma'aikaciyar jinya ce, tace mu je daga waje mu jira. Fita muka yi, Alawiyya taje bayan mota ta ɗakko ƙatuwar dadduma ta shinfiɗa mana. Nace da Zubaida.
"Kuje ku ɗakko abinci a bayan motar Jamilu maza. Kumatu gafa surukanki. Wannan matar jamilu ce, wannan matar Mustafa, Ƙasimu matarshi na gida, ita da matar Yayansu, amman zasu tawo in sha Allah. Kumatu tace.
"Au yanzu yarannan ne suka zama ƴan burni haka lallai kam yara Allah yayi albarka. Ni kinga Zakiya, karayar arzikice ta samu mijin nata, aikin komai bayayi. Ita ke wankau da surfau take ciyar da kanta, da yara. Gashi ma ciwon hawan jinine da'ita. Sauma'iyya kuwa muna nan tare, har yanzu miji bai samu ba. Wannan ɗan banzan yaje ya gama rayuwar gidan kaso, ya dawo. Wallahi maganar da yake ɗebowa na da ba komai bane." Murmushi nayi nace.
"Adda'a zaki dage kiyi ta binsu dashi, Allah ya shiryesu. Ita Sauma'iyya in zamu tafi saiki bani ita, in sata a makarantar addini, wala Allah ta samu miji a birni tayi aurenta." Kumatu tayi ta kuka tana share majina.
Ɗakin likita:
MRS BUKHARI
[08/04, 19:57] Mrs Bukhari: GAWURTATTU UKU
MRS BUKHARI
LAMBA TA ASHIRIN DA TAKWAS:
JOS:
"Uwo wannan shine gidana, ga shaguna guda biyu" Farin ciki ne ya lulluɓemun zuchiyata, nace dashi.
Masha Allah, Allah ya ƙara maka buɗi da ɗaukaka"
"Ameen Uwona" Fitowa mukayi dukka, Idi na riƙe da jakar kayana. Ɗan mabuɗi yasa ya buɗe ƙofar. Yai mana iso zuwa ciki. Tsakar gidan tasha sumunti luwal_luwal gwanin sha'awa. Tabarma ya shinfiɗa mana daga inuwa, ya kawo mana ruwa.
"Uwo bari in kira Hadiza ta dawo gida, bikin ƙanwarta akeyi shine ta kwashi yaran suka koma can gidan nasu. Gobe za'a gama bikin."
A'a barta tana cikin ƴan uwanta tana jin daɗinta. Allah ya kaimu goben."
"To shikenan, zanje anjima in ƙarɓo ɗan mabuɗin madafi. Amman kafinnan bari in ɓalle ɗakinta, inason in mayar mata da kayanta wancan ɗaƙin. Sabida wanda take ciki yafi wancan ɗin girma." Yaƙi ya barni ince komai. Shi da Ƙasimu, da Mustapha sukaita jigilar fito da kayan jeren Hadiza, suna jera mata a ɗakin dake can cikin gida. Bayan sun gama kuma, ya fita ya jibgo mana naman balagu da masa, da lemon ƙwali." Ya ja Ƙasimu, da Mustapha zuwa kasuwa. Bayan kamar awa guda, ina sallah sai gasu sun shigo, da kaya kici_kici. Harda su gado da katifa. Haka akaita shiga da kaya harda kujeru masu kyau. Saida suka kintsa komai, sannan Idi yai mana iso zuwa ɗakin. Kafet malala a ɗakin ga taushi, komai sabo aka saka, ga gadona babba sosai, da sababbin zannuwan gado da bargo a ƙatuwar leda.
"Uwo nanne ɗakinku da su Alawiyya. Nan ɗin yafi dacewa dake. Can ɗin ƙananune, kuma falle falle ne guda uku. To na bata biyu, yaranta na basu ɗaya. Ki sake a nan, ga makewayi a ciki kinga kina buƙatar sirri, tunda da suruka zaki zauna."
Amman ai daka barta a ɗakinta, ni falle ɗayan ɗaƙi ya isheni, a falle ɗaya na gama rayuwar ƙauye. Tun daga ɗakin mahaifiyata, har zuwa gidan aurena". Murmusawa yayi yace.
"Nan gidan ɗankine, wanda kika sha azaba wajan rainon cikinshi da haihuwarshi. Uwo bana manta sanda nake samunki a bayan gonar mai gari, ina gani kullum sai kinyi kuka in zamu rabu. Haka sanda Baba ya koreni, ina jiyo sautin kukanki. Inna barki a ɗaki ɗaya matata na ɗaki biyu da makewayi. Tamkar ban darajaki a matsayinki na jajirtacciyar uwa ba. Uwo aljanna ba'a ƙarƙashin matata take ba. A wajanki nake neman albarka" munyi kuka sosai dani da yaran duka. Haƙiƙa Idi ya haifu ya cika ɗa." Fita suka yi da Ƙasimu suka gyara shagon waje tsab, Ƙasimu ya shigo gida. Shi kuma yace a sanar mun yaje karɓo ɗan mabuɗin madafi."
Idi:
Kai tsaye gidan surukan nashi ya shiga, sabida shi ɗane a gidan. Iyaye kaɗai ya tarar a gidan. A gaban mahaifiyar Hadiza ya tsugunna, aka gaggsisa, yai musu Allah ya sanya alkhairi tare da jaddada musu uzirin daya hanashi halartar ɗaurin aure."
"Yanzu haka ma, ita mahaifiyar tamu, na tawo da'ita da ƙannena zamu zauna tare." Mahaifiyar Hadiza tace.
"Ka kuwa kyauta, Allah yayi albarka. In suka huta, muka gama sallamar baƙi muma, zamu zo a ga juna"
"Zamu zo ma Mama, tanason tazo tayi godiya bisa karamcin da akai mata. Hadizan basa nan ko?"
"Sun tafi gidan Amarya jere, shi yasa kaga gidan ya yashe ba kowa."
"Ta bar ɗan mabuɗi a nan, ko dashi ta tafi?" Mahaifiyar Hadiza tace.
"Bari in ɗakko maka jakarta ka duba ko zaka samu" Ɗakko mai jakar tayi ya duba, ya ɗauƙa, yaima iyayen Hadiza alkhairi, tare dayi musu sallama."