Sashe 7
Dangi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karbar wayar Momy tayi, Cikin ranta tace Daddy.., taji dadin yanda Nihla tace Daddy, amma ita Anty 🤦🏻♀️, batasan meyasa Nihla take kiranta da Anty ba, kokuma har yanzu bata bata matsayin uwa bane a gareta?
Kawar da tunanin tayi aranta tadauki wayar "ki dauko Nihla kufuto mutafi"
Abinda yace da ita kenan, tace "to" tareda kashe wayar, farin ciki yakamata, ta kalli Nihla tace "Nihla tashi ki sauya hijabi mutafi, tare dake zamu wuce"
Batayi tunanin komai ba ta shiga daki ta sauya hijabin jikinta, sannan tadauki wasu kayan acikin jaka sukayi sallama da sauran yan'uwan babanta suka futo
Motoci uku suna jere akofar gidan, suka nufi daya daga ciki, hannunta yana cikin na Momy, Daddy yatashi yayiwa sauran mutanan wajan sallama, amma kokadan baiyiwa Baba magana akan Nihla ba, kawai de yace musu su suntafi, baba yakasa magana, yayi shiru yana kallansu har suka shiga Mota, akan idonsa aka tafi da Nihla, amma bai nuna komai ko akan fuskarsa ba
❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️
Sai dare suka qarasa kano, agate din gidan sukai Parking gaba dayan motocin, zubawa gate din ido tayi, shi kadai ma abin kallone
Ana bude musu gate suka shiga gidan
Anan taga Inda duniya take, Kamar gidan turawa,part hudu ne manya manya agidan, saide akwai nisa sosai a tsakanin kowanne parta, ga kuma Parking space dayake cikeda manyan motoci
Futowa sukai daga motar, kowa yanufi hanyar part dinsa, Alhaji Basiru yace "Nihla sai gobe yan'uwan ki zasuzo ki gansu kinji?"
Daga masa kai kawai tayi, Momy taja hannunta suka nufi nasu part din, suna shiga taga falon yahadu, komai ya tsaru yanda yakamata
Zama sukai dukansu afalon,Usman ya kalleta yanaso yaja hankalinta tadan sake tadena tunani yace "to yar'qauye tazo birni sai kalle kalle take, Momy wannan yarinyar fa sakina rufe mata ido wani lokacin" 🤣
Murmushi Momy tayi "eh lalle Usman bakason auren naga alama, karfa kazo kana kuka nabaka ita"
Daria sukasa gaba dayansu harda Nihla, Aliyu yace "haba Momy, kirasa wazaki bawa sai yaya Usman? Ai yayi mana tsufa Momy"
Dasauri farouq yace "eh dama ai kasan Nihla tawace, ni Momy zata bawa ko Momy?" ya qarasa maganar yana kallan Momy
Tace "duk ba Wanda Zan bawa, ni mijin yata saiya kasance Mai tsananin sonta kunji ko, bazan badata a araha ba"
Alhaji ne yashigo dauke da sallama, dukansu lokaci daya suka nutsu, yakalli Momy yace "Hajiya nina shiga daki, akula da wannan yarinyar"
Saida Momy tayi Murmushi sannan tace "to Alhaji"
Farouq yace"momy nizan wuce gida, nagaji sosai "
Aliyu yace" yes amarya tana jira "
Daria yayi yace" bakada dama yaya Aliyu, "yakalli Nihla yace" my Sister Zan gudu gida, kinsan momynki ta dade da bawa wata ni, idan kin gama hutawa sosai agidan, ki dauki wayar Momy kisaka number ta, ki kirani Muje nakaiki yawo kiga gari, sannan muyi shopping kinji ko? "
Saida tayi Murmushi Mai kyau dimple dinta suka futo sannan tace" to yaya farouq "
Usman yace" eh lalle farouq da alama wani zaiyi kishi dakai idan yadawo "🤣
Nihla bata fahimci komai ba akan maganar Usman, Momy de ta fahimta Dan haka tayi Murmushi
Aliyu ma yayi daria yace" saide ayi Yaqi, ba zamu qi kyautatawa yar qanwar mu ba, "
Yamaida kallansa ga Nihla yace" Nihla kina jina ko?, nima idan kin gama hutawa ki kirani nazo da kaina nadauke ki Muje wajan telan mata ta yayi dinki masu kyau "
Usman yace" to nikam Babu ruwana, zanyi rabiya a tsakani, kada naje nashiga ciki wataran Pilot Yaqi ragemin hanya zuwa Saudia "🤣
Momy tace" Usman baka isaba, bawani rabiya da zakayi, nagane ka, Wato wayo ko? "
Yace " Momy kinsan de halin mutumin naki ko,?amma shikkenan nima idan tagama hutawa zanzo gidan sai abinda tace tanaso da kanta insha Allah "
Momy tace" eh naji "
Daga nan sukai musu sallama kowa yatafi gidansa, Momy tana qara jin dadin yanda kan yaranta yahadu sosai, kuma tasan ba komai yasa sukewa Nihla wannan wasan ba sai don tasake dasu ne ta kuma kwantar da hankalin ta.
Kallan Momy tayi tace" Anty wai duk sunyi aure ne? "
" sunyi aure Nihla, ni kadai ce agidan yanzu, saikuma ke dakika dawo, shi Abba yadade da gama karatu harma yafara aiki, shida Aslam, basu saka ranar dawowa bane, yanzu haka Alhaji yahana afada musu wannan mutuwar amma da yanzu kin ganshi "
Tace" to Anty Allah yabasu zaman lafiya "
" Amin Nihla, tashi Muje kiyi wanka kici abinci saiki kwanta ko? "
Babu musu tatashi, kai tsaye dakin Momy suka tafi, tayi wanka sannan taci abinci, Momy tasa ta ta kwanta, ta qara mata karfin esi sannan takashe mata wutar dakin tafita zuwa wajan Daddy
❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️
Washe gari daqyar tasamu taci abinci, idan tatuna Diddi saitaji wani irin abu yatokare mata maqoshi, daqyar taci kadan ahakan ma saboda Momy ta tsareta ne
Cikin murna tashigo part din nasu da gudu tana kwalawa Momy kira "Momy! Momy!! Momy!!!"
Cikin sauri Momy ta kalli wadda tashigo part din nasu, kafin tayi mata magana yarinyar tace "Jiya Ummah tah tace Nihla tazo, Momy tana ina?"
Murmushi Momy tayi "ilham, Nihla tana dakina, jeki sameta"
Dasauri tashige dakin Momy, a lokacin Nihla tana kwance tana tunanin Diddi, sai jin mutum tayi a jikinta, Dasauri ta kalli wadda tashigo din, kyakykyawa ce sosai wadda ake kira da choculate beauty, ahankali tatashi zaune tana cewa "wash Allah, zaki karyani"
Cikin murna dayar tace "to murna nake ance kinzo, duk bamu sanki ba, kema baki sanmu ba, nide sunana ilham, dama ummah na tana cewa kina kama da yayata Aisha, me sunan Diddi, kuma yau nagani, wallahi kina kama sosai da ita"
Murmushi Nihla tayi "dama kece ilham? Ai duk Diddi tana bani labarin ku, ina Aishan take?"
"tana India, amma ta kusa dawowa, meyasa kika zauna a daki ke kadai bakya tsoron kiyi tunani?,"
Ajiyar zuciya tasaki "nayi karatu ne kuma nagaji, shine nake Dan hutawa, ya karatu?"
Fari ilham tayi da idonta "ai nayi candy, ke dukanmu munyi candy, saide tagaba insha Allah"
"nima nayi candy har na karbi result dina,"
Kafin ilham tayi magana Momy tashigo dakin tace "Nihla tunda ga ilham tazo kuje ta tayaki ki gyara dakin naki ko?"
Ilham tace "eh wallahi zomuje"
Dakin dayaji furnitures da Komai launin green suka fara gyara wa, ilham tafara wanke mata toilet, sannan suka goge kayan dakin, tareda yin moppinga, Nihla tanata yabon halin ilham cikin ranta, babu ruwanta faram faram
Dasuka gama gyara wa zama sukai anan kowa tadau wayarta suka hau Xender suna tura abubuwa
Sallama sukayi suka shigo dakin susu biyu, kana ganin su kasan gidansu daya saboda kama dasuke da juna, daya tana sanye da riga da wando dasuka kamata sosai, gata da uban hips masha Allah,dayar kuwa norml kayane a jikinta, kana ganinta kasan silent ce, me riga da wandon ce ta d'akawa Ilham duka abaya
Sannan tazauna
Ilham tace "haba Diyana, irin wannan daukan ai saiki budamin qirjina"
Zama sukayi suma akan gadon, wadda aka kira da Diyana ta kalli Nihla "haba haba Nihla, wannan hijabin fa, Kamar bakyajin zafin duniyar nan? Kinci wani uban hijabi Kamar matar liman haba be wise mana"
Murmushi nihila tayi tana kallanta, yanda taci wannan riga da wando aidole tayi fada akan hijabi 🤣
Wadda batayi maganar ba tace "Nihla sannu da zuwa kinji, kirabu da Diyana, idan kina neman mace Mai shegen son maza to Diyana ce" 🙆🏻♀️
Kallanta Diyana tayi "to Dida idan banso maza ba mata zanso?🤣
Dida tace "kide rage wallahi, ai a yimaka shedar arziki ma abu ne Mai kyau"
Tashi tayi tsaye, batama kalli yar'uwar tata datayi mata magana ba, tace "Nihla, natafi, saina sake dawowa kokuma inkin shigo, ai zaki zo ko?"
Nihla tace "Zan shigo Diyana, nagode "
Ilham ta kalleta, "sai ina kenan?"
Kai tsaye batare da tantamaba tace "wallahi unguwa zamuje nida wani cika 🙆🏻♀️, yanaso zaiyi birthday zamuje mufara shirin komai, danya takura ne ma wallahi banso zuwaba"
Nihla ta kalleta cikeda mamaki anya kuwa Diyana kalau take? 🤔
Dida tace "ke dince zakice antakuraki? Keda yawo? To idan baki bishi ba ina zakije?"
Babu alamun damuwa tacewa qanwar tata "Dida nadade kema kinsan dadade banje nigh Club ba 😳, wallahi nan nakeso naje"
Wannan karan kam Nihla daria tasaka 🤣
Al'amarin Diyana akwai kallo, kuma duk maganar datake yi hankalin ta kwance, zuciyarta daya take magana
"Ilham tace" to saikin dawo, idan Nihla zatazo Zan rakota masha fira "
Tace musu " ok" sannan tafice
Dida ta kalli Nihla tace "haka take wallahi, Karki yi mamaki 🤣, mune yaran Anty Farida, itace babba ninake binta, kuma wallahi Mom dinmu tasani amma tazuba mata ido, tana zama idan ta tsarata shikkenan sai kiji shiru"
Murmushi Nihla tayi, tace "Diyana kenan" sannan sukaci gaba sa firarsu gwanin sha'awa
❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️
Washe gari Ilham ce tasake dawowa taja Nihla zasuje ta nuna mata kowanne part na gidan, part dinsu suka fara zuwa
Hajiya Abida tana ganinta ta karbeta hannu bibiyu, tana tausayin yarinyar sosai, taso Aisha Wato Diddi, hakanne yasa ta sakawa yarta suna Aisha, kuma ganin Nihla tana kama da Aishanta saitaji dadi, sai nan nan take da ita, sun dade sannan suka futo
Ji tayi taci karo da mutum, Dasauri tadago kanta taganshi a tsaye abakin kofar part din shima zai shigo, dogo ne fari, saide bakinsa dayayi baqi, alamun yana shan wani abun🤔,yaraba gashin kansa biyu yasakawa Rabin colour Mai launin yallow, dayan gefen kuma yabarshi yanda yake, hatta Dan gemun daya tara irinna samari yan gayu shima yasaka masa kala,ga wani uban bluetooth daya toshe kunnuwansa dashi, da alama waqa yakeji, kana ganinsa kaga tantiri na gaske, ahankali tace masa "ina wuni?"
Yace "normal ne, Nihla ko?"
Tanajin irin Tambayar dayayi mata jikinta yayi sanyi, ahankali ta daga masa kai kawai
Yace "okey kihuta"
Yana fadar haka ya shige ciki 🤣
Ilham taja hannun ta suka futo ta kalleta sannan tace "wannan shine yaya fawaz, shine Babban yayanmu, dagashi sai Aisha saini, Tun suna yara yake kula abokan banza har suka koya masa shaye-shaye, babu irin qwayar da baya sha, Tun su ummah suna fada har sun gaji sunyi shiru
Kawar da tunanin tayi aranta tadauki wayar "ki dauko Nihla kufuto mutafi"
Abinda yace da ita kenan, tace "to" tareda kashe wayar, farin ciki yakamata, ta kalli Nihla tace "Nihla tashi ki sauya hijabi mutafi, tare dake zamu wuce"
Batayi tunanin komai ba ta shiga daki ta sauya hijabin jikinta, sannan tadauki wasu kayan acikin jaka sukayi sallama da sauran yan'uwan babanta suka futo
Motoci uku suna jere akofar gidan, suka nufi daya daga ciki, hannunta yana cikin na Momy, Daddy yatashi yayiwa sauran mutanan wajan sallama, amma kokadan baiyiwa Baba magana akan Nihla ba, kawai de yace musu su suntafi, baba yakasa magana, yayi shiru yana kallansu har suka shiga Mota, akan idonsa aka tafi da Nihla, amma bai nuna komai ko akan fuskarsa ba
❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️
Sai dare suka qarasa kano, agate din gidan sukai Parking gaba dayan motocin, zubawa gate din ido tayi, shi kadai ma abin kallone
Ana bude musu gate suka shiga gidan
Anan taga Inda duniya take, Kamar gidan turawa,part hudu ne manya manya agidan, saide akwai nisa sosai a tsakanin kowanne parta, ga kuma Parking space dayake cikeda manyan motoci
Futowa sukai daga motar, kowa yanufi hanyar part dinsa, Alhaji Basiru yace "Nihla sai gobe yan'uwan ki zasuzo ki gansu kinji?"
Daga masa kai kawai tayi, Momy taja hannunta suka nufi nasu part din, suna shiga taga falon yahadu, komai ya tsaru yanda yakamata
Zama sukai dukansu afalon,Usman ya kalleta yanaso yaja hankalinta tadan sake tadena tunani yace "to yar'qauye tazo birni sai kalle kalle take, Momy wannan yarinyar fa sakina rufe mata ido wani lokacin" 🤣
Murmushi Momy tayi "eh lalle Usman bakason auren naga alama, karfa kazo kana kuka nabaka ita"
Daria sukasa gaba dayansu harda Nihla, Aliyu yace "haba Momy, kirasa wazaki bawa sai yaya Usman? Ai yayi mana tsufa Momy"
Dasauri farouq yace "eh dama ai kasan Nihla tawace, ni Momy zata bawa ko Momy?" ya qarasa maganar yana kallan Momy
Tace "duk ba Wanda Zan bawa, ni mijin yata saiya kasance Mai tsananin sonta kunji ko, bazan badata a araha ba"
Alhaji ne yashigo dauke da sallama, dukansu lokaci daya suka nutsu, yakalli Momy yace "Hajiya nina shiga daki, akula da wannan yarinyar"
Saida Momy tayi Murmushi sannan tace "to Alhaji"
Farouq yace"momy nizan wuce gida, nagaji sosai "
Aliyu yace" yes amarya tana jira "
Daria yayi yace" bakada dama yaya Aliyu, "yakalli Nihla yace" my Sister Zan gudu gida, kinsan momynki ta dade da bawa wata ni, idan kin gama hutawa sosai agidan, ki dauki wayar Momy kisaka number ta, ki kirani Muje nakaiki yawo kiga gari, sannan muyi shopping kinji ko? "
Saida tayi Murmushi Mai kyau dimple dinta suka futo sannan tace" to yaya farouq "
Usman yace" eh lalle farouq da alama wani zaiyi kishi dakai idan yadawo "🤣
Nihla bata fahimci komai ba akan maganar Usman, Momy de ta fahimta Dan haka tayi Murmushi
Aliyu ma yayi daria yace" saide ayi Yaqi, ba zamu qi kyautatawa yar qanwar mu ba, "
Yamaida kallansa ga Nihla yace" Nihla kina jina ko?, nima idan kin gama hutawa ki kirani nazo da kaina nadauke ki Muje wajan telan mata ta yayi dinki masu kyau "
Usman yace" to nikam Babu ruwana, zanyi rabiya a tsakani, kada naje nashiga ciki wataran Pilot Yaqi ragemin hanya zuwa Saudia "🤣
Momy tace" Usman baka isaba, bawani rabiya da zakayi, nagane ka, Wato wayo ko? "
Yace " Momy kinsan de halin mutumin naki ko,?amma shikkenan nima idan tagama hutawa zanzo gidan sai abinda tace tanaso da kanta insha Allah "
Momy tace" eh naji "
Daga nan sukai musu sallama kowa yatafi gidansa, Momy tana qara jin dadin yanda kan yaranta yahadu sosai, kuma tasan ba komai yasa sukewa Nihla wannan wasan ba sai don tasake dasu ne ta kuma kwantar da hankalin ta.
Kallan Momy tayi tace" Anty wai duk sunyi aure ne? "
" sunyi aure Nihla, ni kadai ce agidan yanzu, saikuma ke dakika dawo, shi Abba yadade da gama karatu harma yafara aiki, shida Aslam, basu saka ranar dawowa bane, yanzu haka Alhaji yahana afada musu wannan mutuwar amma da yanzu kin ganshi "
Tace" to Anty Allah yabasu zaman lafiya "
" Amin Nihla, tashi Muje kiyi wanka kici abinci saiki kwanta ko? "
Babu musu tatashi, kai tsaye dakin Momy suka tafi, tayi wanka sannan taci abinci, Momy tasa ta ta kwanta, ta qara mata karfin esi sannan takashe mata wutar dakin tafita zuwa wajan Daddy
❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️
Washe gari daqyar tasamu taci abinci, idan tatuna Diddi saitaji wani irin abu yatokare mata maqoshi, daqyar taci kadan ahakan ma saboda Momy ta tsareta ne
Cikin murna tashigo part din nasu da gudu tana kwalawa Momy kira "Momy! Momy!! Momy!!!"
Cikin sauri Momy ta kalli wadda tashigo part din nasu, kafin tayi mata magana yarinyar tace "Jiya Ummah tah tace Nihla tazo, Momy tana ina?"
Murmushi Momy tayi "ilham, Nihla tana dakina, jeki sameta"
Dasauri tashige dakin Momy, a lokacin Nihla tana kwance tana tunanin Diddi, sai jin mutum tayi a jikinta, Dasauri ta kalli wadda tashigo din, kyakykyawa ce sosai wadda ake kira da choculate beauty, ahankali tatashi zaune tana cewa "wash Allah, zaki karyani"
Cikin murna dayar tace "to murna nake ance kinzo, duk bamu sanki ba, kema baki sanmu ba, nide sunana ilham, dama ummah na tana cewa kina kama da yayata Aisha, me sunan Diddi, kuma yau nagani, wallahi kina kama sosai da ita"
Murmushi Nihla tayi "dama kece ilham? Ai duk Diddi tana bani labarin ku, ina Aishan take?"
"tana India, amma ta kusa dawowa, meyasa kika zauna a daki ke kadai bakya tsoron kiyi tunani?,"
Ajiyar zuciya tasaki "nayi karatu ne kuma nagaji, shine nake Dan hutawa, ya karatu?"
Fari ilham tayi da idonta "ai nayi candy, ke dukanmu munyi candy, saide tagaba insha Allah"
"nima nayi candy har na karbi result dina,"
Kafin ilham tayi magana Momy tashigo dakin tace "Nihla tunda ga ilham tazo kuje ta tayaki ki gyara dakin naki ko?"
Ilham tace "eh wallahi zomuje"
Dakin dayaji furnitures da Komai launin green suka fara gyara wa, ilham tafara wanke mata toilet, sannan suka goge kayan dakin, tareda yin moppinga, Nihla tanata yabon halin ilham cikin ranta, babu ruwanta faram faram
Dasuka gama gyara wa zama sukai anan kowa tadau wayarta suka hau Xender suna tura abubuwa
Sallama sukayi suka shigo dakin susu biyu, kana ganin su kasan gidansu daya saboda kama dasuke da juna, daya tana sanye da riga da wando dasuka kamata sosai, gata da uban hips masha Allah,dayar kuwa norml kayane a jikinta, kana ganinta kasan silent ce, me riga da wandon ce ta d'akawa Ilham duka abaya
Sannan tazauna
Ilham tace "haba Diyana, irin wannan daukan ai saiki budamin qirjina"
Zama sukayi suma akan gadon, wadda aka kira da Diyana ta kalli Nihla "haba haba Nihla, wannan hijabin fa, Kamar bakyajin zafin duniyar nan? Kinci wani uban hijabi Kamar matar liman haba be wise mana"
Murmushi nihila tayi tana kallanta, yanda taci wannan riga da wando aidole tayi fada akan hijabi 🤣
Wadda batayi maganar ba tace "Nihla sannu da zuwa kinji, kirabu da Diyana, idan kina neman mace Mai shegen son maza to Diyana ce" 🙆🏻♀️
Kallanta Diyana tayi "to Dida idan banso maza ba mata zanso?🤣
Dida tace "kide rage wallahi, ai a yimaka shedar arziki ma abu ne Mai kyau"
Tashi tayi tsaye, batama kalli yar'uwar tata datayi mata magana ba, tace "Nihla, natafi, saina sake dawowa kokuma inkin shigo, ai zaki zo ko?"
Nihla tace "Zan shigo Diyana, nagode "
Ilham ta kalleta, "sai ina kenan?"
Kai tsaye batare da tantamaba tace "wallahi unguwa zamuje nida wani cika 🙆🏻♀️, yanaso zaiyi birthday zamuje mufara shirin komai, danya takura ne ma wallahi banso zuwaba"
Nihla ta kalleta cikeda mamaki anya kuwa Diyana kalau take? 🤔
Dida tace "ke dince zakice antakuraki? Keda yawo? To idan baki bishi ba ina zakije?"
Babu alamun damuwa tacewa qanwar tata "Dida nadade kema kinsan dadade banje nigh Club ba 😳, wallahi nan nakeso naje"
Wannan karan kam Nihla daria tasaka 🤣
Al'amarin Diyana akwai kallo, kuma duk maganar datake yi hankalin ta kwance, zuciyarta daya take magana
"Ilham tace" to saikin dawo, idan Nihla zatazo Zan rakota masha fira "
Tace musu " ok" sannan tafice
Dida ta kalli Nihla tace "haka take wallahi, Karki yi mamaki 🤣, mune yaran Anty Farida, itace babba ninake binta, kuma wallahi Mom dinmu tasani amma tazuba mata ido, tana zama idan ta tsarata shikkenan sai kiji shiru"
Murmushi Nihla tayi, tace "Diyana kenan" sannan sukaci gaba sa firarsu gwanin sha'awa
❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️
Washe gari Ilham ce tasake dawowa taja Nihla zasuje ta nuna mata kowanne part na gidan, part dinsu suka fara zuwa
Hajiya Abida tana ganinta ta karbeta hannu bibiyu, tana tausayin yarinyar sosai, taso Aisha Wato Diddi, hakanne yasa ta sakawa yarta suna Aisha, kuma ganin Nihla tana kama da Aishanta saitaji dadi, sai nan nan take da ita, sun dade sannan suka futo
Ji tayi taci karo da mutum, Dasauri tadago kanta taganshi a tsaye abakin kofar part din shima zai shigo, dogo ne fari, saide bakinsa dayayi baqi, alamun yana shan wani abun🤔,yaraba gashin kansa biyu yasakawa Rabin colour Mai launin yallow, dayan gefen kuma yabarshi yanda yake, hatta Dan gemun daya tara irinna samari yan gayu shima yasaka masa kala,ga wani uban bluetooth daya toshe kunnuwansa dashi, da alama waqa yakeji, kana ganinsa kaga tantiri na gaske, ahankali tace masa "ina wuni?"
Yace "normal ne, Nihla ko?"
Tanajin irin Tambayar dayayi mata jikinta yayi sanyi, ahankali ta daga masa kai kawai
Yace "okey kihuta"
Yana fadar haka ya shige ciki 🤣
Ilham taja hannun ta suka futo ta kalleta sannan tace "wannan shine yaya fawaz, shine Babban yayanmu, dagashi sai Aisha saini, Tun suna yara yake kula abokan banza har suka koya masa shaye-shaye, babu irin qwayar da baya sha, Tun su ummah suna fada har sun gaji sunyi shiru