← Book details Dangi Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 59

Sashe 26

Dangi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallansa tayi, yaune karon farko data tabaji yakira sunanta, harara ta sakar masa tatashi ta nufi hanyar dakinsu, shima yatashi yabita, tana shiga dakin tarufo kofar, shikuma yakawo kansa zai shiga sai qumm tabige masa fuska

Kadan yarage Fawaz yayi hauka agidan surukai 🤣, haka yafuto jikinsa duk yayi sanya, ko kallan part dinsu baiyi ba yaja motarsa ya koma gida

❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️

Yau Tun safe hajiya Na'ila bataga futowar Diyana ba, Dan futowar datake ta yataya aiki ma yau shiru 🤣

Tace "to wannan yarinya ko lafiya?" tashi tayi ta nufi dakin nata, tana zuwa ta risketa tana kuka adaki, hajiya tace "subhanallah Diyana menene kuma yafaru?"

Cikin kuka tace "Hajiya niso nake natafi gidanmu"

Hajiya tanemi waje tazauna agefen Diyana tace "ai dole kice zaki tafi gida Diyana, tunda shi yazo ya ajiye ki baya tunanin zuwa ya dauke ki, bansan yaushe Adam yakoyi taurin kaiba, nace yazo gida ya sameni Yaqi zuwa, nakira wayarsa kuma yadena dauka ma yanzu, inde baso yake na yiwa babansu maganar ba bansan yaya zanyi ba, hada kayanki ina zuwa "

Gyada kanta tayi, sannan tadauke komai nata na dakin itama ta shirya, hajiya ce tadawo dauke da cup ahannun ta da zuma aciki, tace "ki kalli abinda Zan hada miki kigani saiki dinga yi ,"

Diyana ta gyada kanta tana goge hawaye

Hajiya tazauna tana 'bare gyadar miya da qwai agaban Diyana tanayi tana sababi🤣"ba dole maza su dinga renaku ba, yaran zamani idan anyi muku aure shikkenan saiku zauna dagaku sai i love you, bazaku tashi tsaye akan mazajenku ba, ko wacce mace tanada sirrin ta, kuma ita tasan abinda mijinta yakeso, Inda kin kamashi ahannun ki datun ranar dayace kidawo gida saiya nemeki toko sati daya bazai iyaba zaizo har Inda kike yadauke ki "

Akan idon Diyana hajiya Na'ila tagama bare gyadar miya guda goma, da dafaffan qwai guda biyu sannan tazuba acikin cup din zuman nan tabata tace" karbi ki shanye duka "

Diyana datayi kasaqe tana kallan ikon Allah takarba ta shanye, zaqin zuman yasa harda saka hannu ta lashe kofin tass🤣
Cikin ranta tana mamakin hajiya, ko da wadannan abubuwan take amfani shiyasa duk masifar ta mijinta yakasa rabuwa da ita?

('yar uwa wanna sirri ne Mai mutuqar kyau wallahi, ko gwada zaki tabbatar da magana ta, wadda bata taba yiba zata samu gyadar miya, irin me qamshin nan, bafa gyada wadda ake gyada amaro da'itaba, a a gyadar miya zaki samu guda goma, kibareta kidaka tadaku sosai, saiki bare dafaffan qwanki guda biyu, ki yaiyanka akan gyadar miyar dakika daka, saiki zuba zuma cokali biyu aciki kijuya sosai, saiki shanye gaba daya, idan kuma kin tabayi to qwai daya zaki yaiyanka Karki sake kisa guda biyu, sirri ne Mai kyau, matan aure zasuji da dinsa sosai, ki jarraba yar'uwa🙏🏻)

Hajiya ta dubeta tace "to nan gaba saiki dinga saka qwai daya, kuma biyaiya kici Gaba dayi Diyana, yinayi bari nabari,kuma saikin ja ajinki dakyau, ki nuna masa kema kinada daraja, dan abubuwan Jan hankalin nan kidinga yimasa, yar kwalliyar nan ce duk ki masa" 🤣

Diyana tace "to hajiya, insha Allah"

Daga nan hajiya tace tasaka mayafin ta sutafi, aikuwa cikin sauri Diyana tasaka suka futo, ahanya ma fada take qara mata, tana dada wayar mata da kai akan zaman aure har sukaje gidan nasa 🤣

Sabon maigadi suka gani azaune abakin get din, nan hajiya tafada masa kosu waye, aikuwa cikin ladabi yabarsu suka shiga, acikin ma saida hajiya tasake yimata fada sannan tayi mata sallama tatafi, hajiya na tafiya Diyana tatashi tahau gyaran gidan, dakinta tafara gyara wa da toilet Sanna tashige dakinsa, duk gadon nasa a hargitse, haka tahau gyaran dakin tasaka masa Air freshner, duk kayansa daya ajiye a'inda bai daceba ta gyara masa su, takardun dalibai yan jami'ah data gani Kamar ma text ne suma ta tattara masa su waje daya, sannan tafuto ta gyara falon, bata zauna ba tashige kitchen tahada masa abinci Sabon maigadi suka gani azaune abakin get din, nan hajiya tafada masa kosu waye, aikuwa cikin ladabi yabarsu suka shiga, acikin ma saida hajiya tasake yimata fada sannan tayi mata sallama tatafi, hajiya na tafiya Diyana tatashi tahau gyaran gidan, dakinta tafara gyara wa da toilet Sanna tashige dakinsa, duk gadon nasa a hargitse, haka tahau gyaran dakin tasaka masa Air freshner, duk kayansa daya ajiye a'inda bai daceba ta gyara masa su, takardun dalibai yan jami'ah data gani Kamar ma text ne suma ta tattara masa su waje daya, sannan tafuto ta gyara falon, bata zauna ba tashige kitchen tahada masa abinci
Sabon maigadi suka gani azaune abakin get din, nan hajiya tafada masa kosu waye, aikuwa cikin ladabi yabarsu suka shiga, acikin ma saida hajiya tasake yimata fada sannan tayi mata sallama tatafi, hajiya na tafiya Diyana tatashi tahau gyaran gidan, dakinta tafara gyara wa da toilet Sanna tashige dakinsa, duk gadon nasa a hargitse, haka tahau gyaran dakin tasaka masa Air freshner, duk kayansa daya ajiye a'inda bai daceba ta gyara masa su, takardun dalibai yan jami'ah data gani Kamar ma text ne suma ta tattara masa su waje daya, sannan tafuto ta gyara falon, bata zauna ba tashige kitchen tahada masa abinci, wainar shinkafa da miyar egusi da kuma lemon danyar citta, tasaka shi a fridge yana daukan sanyi

(yau Diyana anzama matar novel 🙊😀)

Wanka taje ta sheqo, ta shirya cikin wata 'yar bingilar riga, rigar batazo gwiwar taba, amma saura kadan ta qaraso gwiwar ta ,babu hannu ajikin rigar hakanne yasa lafiyaiyar fatar jikinta ta baiyana, Sanna tazo takunna tv tana sauraren karatun qur'ani

Tadauki wayarta tariqe ta, dora kafa daya kan daya tana jira yashigo taji dame yazo inyaso ayita taqare

Taurari:

D-Diyana
A-Abba
N-Nihla
G-guy (Fawaz)
I-Ilham
D-Dida
A-Aslam
Y-Yusif
A-Adam

(idan naga Comments dayawa zan'iya yin Wanda yafi wannan yawa gobe, idan ban ganiba kuma gaskiya.... 🤒)

Amnah El Yaqoub ✍️
[7/1, 12:54 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493

29&30

Tun daga bakin get maigadi ya sanar masa cewa su hajiya sunzo, yana jin haka yasan cewa may be tare suke da Diyana, Parking yayi yafuto daga cikin motar, yana nufi cikin gidan yana magana cikin zuciyarsa, shida yace taje gida saiya nemeta meyasa zata dawo masa gida, kuma yasan sarai aikin mama ne

Yana dosar kofar falon yaji qamshin girki yana tashi, yace ikon Allah, sannan yatura yashiga,falon yabi da kallo yanda ya sauya kama Kamar bashi ba, ga wani qamshi dayake tashi, hakanne yasa ya lumshe idonsa.
Tana ganin shigowarsa falon ta miqe sai rangwada takeyi, taje kusa dashi da niyya ta matsa jikinsa sosai tace "Sannu da zuwa"

Dasauri yabude idonsa, sai ganinta yayi agabansa, kafin yabata amsa tasa hannu ta karbi Briefcase dinsa, shima da niyya tahana da hannunsa wajan karbar Briefcase din, tace "kawo jakar"

Babu musu yasakar mata,yana sakin ajiyar zuciya, sarai tajishi, tajuya tayi gaba da niyya take wata irin tafiya me daukan hankali, tayi cikin dakinsa da jakar

Shikuwa Adam sai satar Kallanta yakeyi, Yaqi yadago kansa ya kalleta sosai, saide ta qasan ido yake qare mata kallo, yanzu dama maryam ta'iya wannan gyaran gidan shine bata taba yiba?

Acikin kujerun falon Yazauna, yasake lumshe idonsa yana sauraron karatun qur'anin dayake tashi, ga wannan qamshin girkin yacika masa hanci, tabbas zaiso yaji dandanonsa

Yana nan zaune tafuto daga dakin, takalleshi taga yanda ya lumshe ido, tatuno yanda ya shareta a hospital, qasa qasa tace ai saina rama ne, qarasawa tayi tazauna ahannun kujerar dayake zaune, taja hannunsa guda daya tace "ya Adam Muje kayi wanka kaci abinci"

Cikin basarwa yace "no kibarshi kawai, nagode"

Wata irin harara ta zuba masa irin ta baka isa dinnan ba, ta qara jan hannunsa har wajan breast dinta, yanajin yanda hannunsa yake gogar breast dinta cikin ransa yace Innalillah...meyake damun maryam ne, Kallanta yayi, yaga sai sake tura hannunsa take awajan yace "shikkenan sakeni zanje nayi"

Murmushi tayi tasakar masa hannun, sannan yashige dakinsa, bata bishi dakin ba tayi kitchen tana kokarin hada masa Abincin, yau kam tasa aranta saitasa ya Adam yadau charge, barema hajiya tagama yimata huduba ai batada damuwa 🤣

Bayan yayi wankan tsaf ya shirya yafuto falon anan yaga irin girkin data hada masa, kokadan besaki fuskar saba, sai wani basarwa yake, yanemi kujera Yazauna yana sauya tasha, ta kalleshi tace zakayi bayani ne, afili tace "ya Adam ga abinci, ka sauko kaci"

Batare dayace komai ba yasakko Yazauna aqasan shima, yafara kokarin zuba Abincin da kansa, cikin sauri ta riqe masa hannu tace "kabari mana, yau nice zanyi feeding dinka, Kamar yanda kamin lokacin da banda lafiya"

Yace "Am maryam dakin bar..." Dasauri katseshi, tace "shiiiii"

Nan take yayi shiru, ta matsa kusadashi tazuba masa Abincin sannan tasa spoon tafara bashi, daqyar Adam yake cin Abincin saboda gaba daya tashige jikinsa, yanajin yanda take goga masa kirjinta ajikinsa, duk yarasa yaya zaiyi da ita, shi yana ganin Ilham da Aslam suna soyaiya a asbiti ashe idan Diyana ce saide arufe ido?
Ko yaya yayi motsi saiya gogi kirjinta, gashi ita abin nata masha Allah ba kadan ba, Danya rabata da jikinsa yasa yayi dabara cikin shagaggiyar murya yace "ke bazakici bane?"

Diyana tanajin yanda yayi mata maganar tasan cewa lalle tarkon ta yakama, cikin qasa-qasa da murya tace "um um, nafison kaide kafara qoshi tukunna"

Jiyayi jijiyoyin kansa suna nema su fara aiki, haka yayi shiru yakasa cemata komai, gaba daya saiya zame mata Kamar wani dolo, haka tadinga bashi Abincin shide sai santi yake aransa, domin kuwa ba qaramin dadi yamasa ba

Saida tagama bashi, sannan taci Dan kadan, yazuba mata ido yana Kallanta yanata mamaki, gaskiya duk Wanda ba'a zauna lafiya a gidansa ba to mata basu bashi hadin kai bane, amma inde mata sun bashi hadin kai, to za'a zauna lafiya, kalli de maryam, da ya'isa yayi mata maganar girki ma, amma yanzu shine ake bashi abinci abaki, yaji dadi sosai aransa, kuma yadena fishin shi ya dade da janyewa🤣

Ajiyar zuciya yayi, yace "Maryam girkin yayi dadi sosai"

Ajiye spoon din hannunta tayi tace "da gaske ya Adam yamaka dadi?"

Jinjina kansa yayi alamun qwarai kuwa

Beyi aune ba yaji takai masa wata irin runguma, tace"thnk you ya Adam "
Chapter 26 · 0% Book details