← Book details Dangi Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 59

Sashe 52

Dangi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yasa hannu ya shafi fuskarta yace "kinyi kyau sosai,"

Tayi Murmushi kadan batare data kalleshi ba, yace "kunya ta kikeji kuma? Toki dena, tashi mana, tashi kitayani mana"

Ahankali tace "saikace wani Yaro"

"yes, ai qaramin Baby ne awajan ki"

Nanma batace komai ba, yafara kokarin tashi yana mata wasa "amarya amarya, kisaki jikinki fa" 🤣

Nihla de tana jinsa tayi shiru, tasan cewa yau me rabata da ya Abba sai Allah, yanda yake wannan rawar kafar Allah ne yasan yanda zasu kwashe dashi
Agabanta yafara cire kayan jikinsa, cikin sauri ta runtse idonta, ya kalleta yayi Murmushi, kunyar Nihla tana birgeshi sosai, yadawo dagashi sai gajeren wando yadubeta yace
"zanje nayi wanka, yakamata kema kiyi shirin kwanciya, nasan kin gaji"

Ahankali ta daga masa kanta, shikuma yafice daga dakin da kayansa

Bai wani dade ba a wankan yadawo dakin nata yana sanye da kayan bacci,dakuma jallabiya a hannunsa, a lokacin harta kwanta da kayan ta a jikinta 🤣

Wata yar qaramar dariya yasaki yace "kisakko muci abinci"

Girgiza kanta tayi tace "naqoshi"

"mene? Banason musu, sauko kawai, kuma wannan kayan najikinki aida kin ciresu, damunki zasuyi idan kina bacci" 🤣

Kokarin tasowa take daga kan gadon tace "Babu komai, bazai dameni ba"

Ajiyar zuciya yayi yace "kozakiyi alwala mufara yin sallah?"

Tace "to" sannan tayi hanyar toilet dinta dake cikin dakin, yabi bayanta dawani irin mayen kallo

Tare suka gabatar da sallah,bayan sun idar yadinga kwararo musu addu'ar zama lafiya dakuma samun zuri'ah tagari, bayan sun shafa ne yabude musu ledar dayazo da ita, kaza ce aciki babba saikuma fresh milk, shida kansa yafara bata taci taqoshi sannan shima yaci, itace takai kayan kitchen har lokacin ana zabga Ruwan sama

Dakin tadawo tarakube agefen gadon, shikuwa kwanciya yayi harda dora kansa akan fillo, yana riqe da wayarsa🤣

Yadago kansa yadubeta yayi Murmushi, yaga alama gaba dayan ta atsorace take dashi, idan kayi mata kyakykyawan tsawa zata iya zurawa da gudu 🤣

Yace "kizo ki kwanta mana"

Ahankali tahau gadon can gefe ta kwanta tareda juya masa baya, tashi yayi ya kashe wutar dakin yadawo kan gadon kusada ita ya kwanta, gabanta yafara faduwa sosai

Yace "Ruwan nan anayin sa dayawa yau, yayi albarka sosai, Allah yasa muma auren mu yayi albarka"

Tayi shiru 🤣

Yayi Murmushi yasake cewa "bakice amin ba"

Sai a lokacin tace "Amin"

Hannunsa yasa yajanyota jikinsa Ahankali, yace "meyake damunkine, naga kin takura kanki"

Girgiza kanta tayi alamun Babu komai, kafin yayi magana aka fara walkiya sosai, sai cida tabiyo baya, har hakan yatsoratar da'ita, cikin sauri tashige jikinsa

Shikuwa Babu musu yasakata acikin faffadan qirjinsa, cikin kunnanta yaradama ta, meyasa ne kike tsoron cida Tun kina qarama? "

Cikin rawar murya tace" Babu komai "

Shiru yayi, yasaka hannunsa ya zagaye ta dasu, jiyake Kamar ya maida ta cikin jikinsa, yace" to kiyi baccinki, babu abinda Zan miki "

Wata irin ajiyar zuciya tasauke har yana mamakin irin yanda take tsoron sa haka, shikuma dama bashida niyyar yimata komai, gara tasake dashi sosai yanda zaifi jin dadi, amma kana ganin tsoron ka a'idon mace qarara haka tayaya zaka nemeta

Addu'ah yayi musu sannan yayi shiru yana tunani, wai yau Nihla ce suke kwance amatsayin ma'aurata

Jin numfashin ta nasauka a qirjinsa yasa yagane cewa tayi bacci, amma shi sam yakasa baccin, yana jin lokacin da aka gama ruwa, har karfe biyu da rabi idonsa biyu

Sai motsi yakeyi yana matse kafafunsa, ahankali yasaka hannu yazuge mata zif din rigarta, ya cire rigar gaba daya, a lokacin ta farka, tsoro yakamata, nan da nan tafara hawaye, bai saurareta ba ya cire mata siket din jikinta, daga ita sai breziya da under wear a jikinta, ahankali yadora bakinsa dede wuyanta yana kissing dinta, yayinda hannunsa yasauka akan qirjinta nan da nan ya rikice, babu bata lokaci ya cire breziya din yana shafa matasu, muryar sa harta fara sauyawa yace "ki.. Kiyi shiru.."

Kafin ma yaga tabashi amsa yadora bakinsa akan qirjinta yanasha, Dafarko wani irin dadi tafara ji saboda yanda yakeyi Ahankali, amma da al'amari yaci gaba da wakana saita fara kuka Ahankali

kukanta ne yaqara volume, daqyar ya'iya Dagowa yace "kiyi shiru mana"

gashi yariqe breast dinta a hannunsa yana matsawa

Cikin kuka tace "ni zafi nakeji"

Numfashin sa gaba daya ya sauya, daqyar ya'iya cewa "toshknn nadena, kiyi shiru kinji"

Ahankali ta daga kanta, daqyar suka samu suka rintsa gaba dayansu shida ita
Amma matsananciyar sha'awa kam yana cikin ta

❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️

Da asuba kam, kasa hada ido tayi dashi,shikuwa gogan daqyar yake aiwatar da Komai, Dan gaba daya jiyayi ma dama yasani bai tabata jiyan, saida yayi wanka sannan yatafi masallaci sallah

Kafin yadawo gida kuwa Nihla harta koma ta kwanta, shima Babu musu ya kwanta, sai a lokacin yasamu bacci Mai dadi ya daukeshi
Tarigashi tashi dasafe, tashiga toilet tayi wanka,taci kwalliya cikin riga da siket na leshi, ta gyara Inda yakamata ta gyara sannan tafuto falo tazauna tana tunanin abinda yayi mata adaren jiya, abin de in Ahankali ne akwai dadi, amma yanda ya Abba yadage yanayi abin ba sauqi, amma ta tabbatar ya Abba yana sonta, ita kanta tasan cewa ya tausaya mata jiya

Har karfe goma tayi tana falon azaune, har lokacin Abba bai tashi ba, dirin motar da taji yasa ta kalli bakin kofar, amma batasan kowaye yazoba, Rafi'ah ce tazo bakin falon ta tsaya tana sallama, Nihla tace "ki shigo mana"

Tashigo falon hannunta dauke da flask din abinci, tace "kinsan gidan amare gara munayi muna doka sallama"

Nihla tace "Allah ya shirye ki Rafi'ah, yagida"

Flask din ta ajiye tace "ga abinci nan inji Momy, yana ganki afalo azaune, nida nake cewa qilama kina cikin bargo kina kuka"

Harararta tayi tace "har wani, kukan me, ni rainona ya Abba yake"

Rafi'ah tace "um kaga masoya, tare nake da ya Yusuf fa, shine yakawo ni"

Adede lokacin yafuto daga dakin ya shirya cikin qananun kaya yayi kyau sosai, maganar Rafi'ah tasauka a kunnansa, yace "meyasa bai shigo ba to"

Rafi'ah ta gaida shi, ya amsa mata yace "kije ki shigo dashi mana"

Rafi'ah tace "tab, ya Yusuf din, saida nace yashigo Yaqi yarda"

Abba yace "to mu bari mubishi," ya juya ya kalli Nihla batare dayace mata komai ba, nan take ta gane nufin sa,maganin kar ayi kar afara, danhaka tanemo hijabin ta tasaka sannan suka futo 🤣

Yana cikin motar ya hango su sun futo su ukun, yabude motar yafuto, tareda bawa Abba hannu suka gaisa, Nihla tace "ya Yusuf ina kwana"

"Alhamdulillah qanwata, ya amarci"

Murmushi tayi masa tace "nayi ta kiran wayarka baka picking meyasa?"

Murmushi yayi yace "a inasan abinda yasa kike kiran, babu komai, Allah yasa hakane yafi alkhaairi, amma yanzu nide kitayani kafa fada ta awajan madam Rafi'ah"

Kunya takama Rafi'ah, tajuya cikin motar da gudu tashige, gaba dayansu sukai murmushi sannan sukai musu sallama suka tafi

Ciki suka koma Nihla tazuba musu Abincin suka faraci, Nihla tayi mamakin duk kishin yaya Abba amma bai nunawa ya Yusuf fa, taji dadin hakan sosai, shikuwa sai Kallanta yake qasa qasa, can ta tsinci maganarsa yana cewa "ke dama rayuwa ce bansaniba"

Kallansa tayi tace "ragwantar me nayi"

"gashinan jiya daga fara abu kika kamamin kuka" 🤣

Spoon din hannunta tasaki tareda rufe idonta, yace "idan kin gama kunyar, Muje nafara koya miki motar ki"

Tace "ya Abba A'ina, bade acikin gidaba"

"ai unguwar nan Babu mutane sosai, mufita kawai"

Lokaci daya tafara murna tace "to ya Abba"

Suna gamawa kuwa, suka futo, motar tata suka shiga Wanda dama already ankawo mata ita gidan, sai kwarara gudu yake Kamar yasamu Babban titi, wannan shine karon farko daya taba yini driving da kansa shida ita
Cikin sauri ta kalleshi tace "ya Abba bafa acikin jirgi muke ba"

Murmushi yayi yace "yawwa, nanma yayi," yatsaya, sannan ya kalleta yace "Futo" 🤣, babu musu tafuto shikuma ya koma Inda take da Yazauna

Fara gwada mata yayi, cikin nutsuwa, tana jinsa tana kuma fahimtar abinda yake fada mata
Yabata umarnin ta gwada practical, gaba daya tsoro ya kamata, daqyar tafara driving din Ahankali, can nesa dasu suka hango wani mutum yana tafiya, amma Nihla data taka wata uwar giya, sai ganin mutumin sukai gab dasu, qiris yarage tayi ciki dashi 🙆🏻‍♀️

Daqayar da temakon Abba aka taka giya, sannan motar ta tsaya, tsoro yakamata, gabanta sai faduwa yake

Tuni ta dora kanta akan sitiyarin motar, Abba yafuto yabawa mutumin hakuri sannan yadawo cikin motar yaga yanda haki Kamar Wanda tayi gudu ya tuntsire da dariya
Dagowa tayi ta kalleshi, yaushe rabonda ya Abba yayi wannan dariyar? tace"wallahi na haqura, abarshi kawai "

Daqyar yadena dariyar yace" a a, manyan direbobi "🤣

Cikin shagwaba tace" Allah kadena min dariya "

Yace" to shknn naji, futo kigani "

Babu musu tafuto daga cikin motar, shima yafuto yadawo driving sit Yazauna, ya miqa mata hannunsa yace "Taho"

Babu musu ta dora hannunta akan masa, babu bata lokaci yadora ta akan cinyarsa, sannan Yarufe motar yace "kina kallan yanda nake yi"

Nihla tayi shiru, tana kallansa, motsin dayake da jikinsa wajan riqe sitiyarin motar da kuma saka giya yasa itama datake zaune akan cinyarsa take motsi, hakan kuwa ba qaramin shiga yanayi ya haddasa masa ba, ahankali ya dakata da driving din yasaka hannu yariqe wais dinta, yadora kansa ajikinta, muryarsa harta fara canjawa yace "kina ganin yanda nake yi ko?"

Nihla Tajuyo ta kalleshi taga yanda gaba daya yanayin sa ya sauya, jikinta yayi sanyi, cikin ranta tace nikam naga koyon Mota 🤣
Afili kuma tace "ina gani"

Shiru yayi, yafara tura hancinsa jikinta yana shaqar qamshin dake tashi ajikinta, ahankali yafara yin sama da hannunsa harya sauka akan qirjinta
Cikin shagwaba Nihla tace "ya Abba awaje mukefa"

Daqyar yadago kansa sannan yabude motar, yace "to zagaya kishigo mutafi gida"

"to ya Abba koyon motar fa?"

Kai tsaye yace "kibari sai nanda wata shida"

Cikin sauri tace "wata shida"

"eh, sai nanda wata shida, zagayo mutafi"

Babu musu tafita takoma daya bangaren sannan yaja motar suka koma gida cikin salama

❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️

Washe gari yaje yasiyo mata qananun kaya, afalo yaganta tana waya, ya ajiye jakar kayan Yazauna agefenta, sai yaji tana cewa "Babu komai Anty Nadiya, ai nasan dama akwai dalilin dayasa baki zoba"
Chapter 52 · 0% Book details