Sashe 6
Dangi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zuwa wannan lokacin Abba yayi candy, Har Alhaji Abubakar yafitar dasu qasar Germany karatu shida Aslam, Dan gidan Alhaji Baqir, tunda yalura hankalin yaron ya karkata akan jirgi 🤣, shiyasa yadage yanaso yacika wa dansa burinsa na ganin yazama cikakken pilot
Yayinda Aslam hankalinsa yafi karkata kan harkar kasuwanci
Bayan shekara biyu Allah yayiwa hajiya rasuwa, mutuwar tataba kowa, wannan family sun shiga damuwa sosai, kowa kaga fuskarsa zaka ganshi dauke da damuwa, Su Abba sunso suzo, amma Alhaji Baqir mahaifin Aslam yahanasu zuwa, yace kawai suyi mata addu'ah, Momy ce takira Diddi tafada mata, a lokacin Nihla tana makaranta, bata jira dawowar ta ba tatafi, shikuma Ibrahim Mai hakuri yace bazai iyu su tafi dukansu subar Nihla ba, idan tadawo ranar uku shi sai yaje
Kowa yaganta a family din yasan ta rame, shi kansa yayan nata daya ganta, saida jikinsa yayi sanyi, gaba daya ta sauya Kamar ba itaba
Bayan angama sutura suka koma part din su Momy, anan takejin labarin tafiyar Abba da Aslam karatu germany, duk yaran gidan sunzo sun gaishe ta, Aisha ce kawai bata ganiba, anan Momy take fada mata cewa tana India tana karatu agidan wani abokin Alhaji, saboda ita tadage bazatai karatu anan ba 🤣
Murmushi kawai Diddi tayi, tace "Allah ya kyauta," suna wannan firar Alhaji yashigo, shima zama yayi, Diddi tasake gaida shi, a mamakinta saitaga ya amsa mata cikin sakin fuska, yana murmushi yace "meyasa baki Taho da mamana ba, Tun tana qarama ban sake ganinta ba"
Diddi tace "Nihla tana makaranta yaya, yanzu ma batasan nataho ba, ashe su Abba suntafi germany"
"wallahi su Abba suntafi, shekarar su biyu kenan, sunaso suzo gida ma nahanasu, nace su bari sai sun gama komai tukunna, aide kuna zaune lafiya ko?"
Mamaki yagama kashe Diddi, tace "yaya lafiya kalau,"
"to alhmdlh, idan kin koma sai kiyi harama hajjin bana dake za'a tafi insha Allah, daga nan sai Rahma tarakaki Dubai kisiyo kayaiyaki kifara business ko"
Saboda murna Diddi harda kukan ta, takasa cewa komai, ahankali shima yatashi ya shige ciki, yanaji kukan ta yana taba ransa, to yaya zaiyi tunda auren de bazata rabu dashi ba, gashi harda Rabon yarinya a tsakani, gara yayi hakuri yaja qanwarsa jikinsa
❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️
After 8 year's
Da gudu tashigo gidansu cikin murna tace "Diddiyyy"
Sannan tafada jikinta ta rungumeta
"Nihla ke kadai ma zaki karyani kihuta"
"to Diddi ai ina murna ne, kinga result din nawa"
Karba Diddi tayi cikeda murna tace "a a masha Allah, Allah yamiki albarka Nihla, Allah ya albarkaci ilminki, neco tayi kyau waec tayi kyau, saura jamb insha Allah"
Fari tayi da idonta tace"Diddi, wannan karan da kinaso, da bakyaso Diddi sainaje kano, inaso naga su Anty "
" A a Nihla kede kice kinaso kiga Abba, to ai Abban bai dawoba, saide kije kiga su Antyn Kamar yanda kika min qarya daga farko "🤣
Ajiyar zuciya tasauke, ta cire dogon hijabin jikinta, kanta Babu dankwali qananun kalbar da akayi mata tazubo agadon bayanta, ta zubawa waje daya ido tana kallo batare data cewa Diddi komai ba
Kallanta Diddin tayi cikin murmushi" to yanmatan Diddi, me kuma ake tunani? "
" Diddi, Yaya Abba yana germany har yanzu bai dawoba, Yaya yusif yatafi china shima Yaqi yadawo, duk qawayena basa nan, basusan nayi Candy ba, dama suna nan Diddi, shi yaya Yusif naje umma tabani number sa amma kullum na kirashi bata shiga, saura yaya Abba Dan Allah Diddi kicewa Anty taturo miki number sa na kirashi "
Diddi tace" a a babu ruwana, keda kikace zakije kanon da kanki? Idan kinje sai Antyn tabaki "
" shikkenan Diddi, idan naje Zan dauki wayarta da kaina na dauki number sa na kirashi "
Diddi tace" keni kin dameni da zancen wannan mutanan naki 😂, tashi kije kisiyomin maganin zazzabi, zazzabi nakeji "
"to Diddi"
Kudin tadauka agefenta tafice daga gidan
Gidansu Nihla kenan, Diddi ta manyan ta, bakinta manne da haqorin makkah, Nihla taqara girma, kyanta yana nan sai abinda yaqaru, tazama budurwa, idan ka kalleta saika sake kallonta, surutun ta yana nan yanda yake
Maganin takawo mata tasha, da yamma tagyara gidan tsaf, tayi wanka ta shirya cikin riga da siket, hips dinta yafuto acikinsu siket din sosai, 'yan madedetan breast dinta ma haka, dukda basu cika girma sosai ba, amma kana kallansu zaka tabbatar a tsaye suke sosai
Kusada Diddi tadawo tazauna tace "Diddi ko zazzabin ne? Naga kinyi shiru kina tunani"
Ajiyar zuciya tasauke tace "tashi kidaukomin wayata inkira yaya na,"
Saida tayi daria sannan tadauko mata wayar tana cewa "hajiya Diddi kinaji da wannan yayan naki,kuma ni Diddi banga alamun ma yanada Fara'ah ba wallahi"
"zakici ubanki Nihla, yayan nawa kike fadawa haka?"
Shiru Nihla tayi tana daria, Diddi takira yayan nata, bugu yadauka "Aisha kina lafiya ko"
"lafiya kalau yaya, Ya wajansu Abba kuwa? Sai yaushe zasu dawo ne yaya?"
Cikin mamaki yace "Abba sun kusa dawowa, amma Lafiya Aisha?"
"lafiya kalau yaya, kawai na matsu yadawo ne naganshi,"
Saida yayi Murmushi Wanda saika dade kafin ka ganshi yayi sannan yace "Zai dawo insha Allah, idan zai dawo ai zanturo driver yazo yadauke ki insha Allah"
"to yaya Allah yakaimu, Tokai yaushe zakazo yaya?"
Cikin mamaki yace "Aisha wai kalau kike kuwa?"
Saida tayi Murmushi tace "yaya lafiya ta kalau fa, kawai inaso naganka ne"
Jikinsa ne yayi sanyi, me yarinyar nan take nufi ne? Anya kalau take kuwa? Haka yake ta fada cikin ransa afili sai yace mata "inde nine Zan shirya gobe nazo kiganni Aisha, shikkenan?"
"eh yaya shikkenan, ka gaida Anty Rahma, ga Nihla ma tana gaishe ka,"
Yace "toki shafa min kanta" sannan ya kashe wayar, Diddi kuwa maganarsa dariya tabata, wai ashafa masa kanta Kamar wata 'yar yarinya
Da magrib baba yadawo daga kasuwa, suna zaune sunata fira, zazzabin datake ji ma Babu yatafi, sallama akayi akofar gidan, baba yace su shigo, samari ne guda uku suka shigo da kaya niqi-niqi ahannu, kwalin taliya da macaroni sai doya Mai yawa, sukace Alhaji isma'eeil mahaifin Yusif ne yace akawo musu yayi zakkah ne
Godia sukayi musu, baba yanata yabon kirkin mutumin, duk unguwar kowa yana yana yabonsa
Har dare yayi suna zaune suna fira, sannan sukaje suka kwanta, Diddi yau a dakin Nihla ta kwanta, Nihla ta dade dayin bacci, ahankali Diddi ta matsa kusada ita ta rungumeta a jikinta, sannan tayi musu addu'ah itama ta kwanta
Da asuba Nihla ce tafara tashi, kallan Diddi tayi agefenta tace "Diddi asuba tayi"
Bata jira amsarta ba tatashi taje tayi alwala tazo tatada sallah, harta idar Diddi bata tashi ba
Addu'ah tashafa, takama kafarta tace "Diddi asubafa tayi"
Taji shiru, hijabin jikinta ta cire tace "a a Diddi lafiya kuwa?"
Takoma kanta tana tashin ta, amma Diddi ko motsi batayi ba, gabanta ne yayi muguwar faduwa, tafara ja da baya Ahankali, harta futo tsakar gidansu, adede lokacin baba yadawo daga masallaci hannunsa dauke da carbi yanaja
Cikin tashin hankali tafara nuna masa d'akin da hannun ta, tace "Baba Diddi!"
Yace "Diddi kuma? Me yasameta? Ko zazzabin ne?"
Bata iya bashi amsaba, duk jikinta rawa yake kawai tana nuna masa dakin da hannu, Dasauri yashiga, itama ta doru abayansa
Yana zuwa yasa hannu ya tallafo Diddi jikinsa yace
"Aisha!"
Yaji shiru, gabansa ne yafadi yaduddubata, lokaci daya jikinsa yayi sanyi baisan lokacin daya zauna ba
"Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Aisha, haba Aisha, meyasa zaki tafi kibamu, me.. Yas..sa Aisha" ya qarasa maganar yana kuka wiwi, sake rungumeta yayi yana fadin "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, yanzu Aisha dama tafiya zakiyi kibarmu?"
Cikeda tashin hankali tafara girgiza kanta "A a baba, Diddi bata mutuba, lafiya fa muka kwanta, baba Diddi na bata mutu ba kadena cewa tamutu baba"
Cikin kuka Kamar ba babanta ba yadago kansa ya kalleta yace "Nihla Aisha tamutu, Aisha tatafi ta barmu"😭
(sannu sannu bata hana zuwa saide adade ba'a jeba, dafatan kun gane)
Amnah El Yaqoub ✍️
[6/16, 11:52 PM] El Yaqoub: ❣️ DANGI 'DAYA❣️
{Romance & Friendship luv}
Writing by Amnah El Yaqoub
Like my page On facebook 👇🏻
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/
9&10
Kuka take sosai Kamar ranta zai fita, wai gawar Diddi ce a gabanta Akwance haka, akan idonta makotansu da wasu daga cikin yan'uwan babanta sukayi mata wanka, bata taba tunanin zataci gaba da rayuwa batare da Diddi ba, babu me iya bata hakuri saboda kowa yasan yanda tashaqu da mahaifiyarta, gara abarta tayi kukan ko zataji sassauci
Dole saida aka jinkirta jana'izarta har saida yan kano suka qaraso, dirin motar da sukaji ne ya tabbatar musu da cewa sun qaraso, gaba dayansu sunzo yara da manya, Momy tana kuka tashigo gidan, duk hankalin mutane ya koma kanta, cikin dakin tashige, tana ganin Diddi Akwance anrufeta da farin mayafi tasake sakin kuka tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Allah yaji qanki Aisha"
Nihla ta kalla datake zaune agefe idonta ya kumbura gashi sunyi jajir, Dasauri ta rungumeta, tana bubbuga bayanta "Nihla kidena kuka kinji, kidena kuka bakiyi rashin uwaba, kina damu kinji yata, kidena kuka"
Duk dakin saida suka sakasu kuka, Alhaji ne yashigo Wato yayan Diddi taredasu Alhaji Baqir gaba dayansu, tsugunnawa yayi agaban gawar, yasaka hannu yabude fuskarta, duk jajircewa irinta Alhaji, saida yayi kuka, yasaka dayan hannunsa Yarufe fuskarsa yana kuka sosai, yakasa magana, yadade yana tsugunne a gabanta, Alhaji Baqir da Alhaji Basiru suka jashi, suka fita dashi, sannan sukayi mata addu'ah, aka qarasa shirya ta, ana daukanta za'a fita da ita waje domin sallah Nihla tasaka kuka ta qanqame Momy tace "Anty zasu tafi da ita"
Kasa magana Momy tayi,domin itama wani irin d'aci takeji aranta
Babu yanda suka iya, haka aka sallaci Diddi aka kaita gidanta na gaskiya, saide muce idan tamu tazo Allah yasa mucika da imani
Ranar da akai sadakar uku data bakwai, da yamma lis yan kano sukai shirin tafiya gida, Momy tana zaune da carbi ahannun ta, wayarta ce tayi qara, wayar tana ajiye kusada Nihla, daukar wayar tayi taga ansa Daddyn Abba hakan ya tabbatar da cewa yayan Diddi ne yake kira, meqa mata wayar tayi tace "Anty Daddy yana kiranki"
Yayinda Aslam hankalinsa yafi karkata kan harkar kasuwanci
Bayan shekara biyu Allah yayiwa hajiya rasuwa, mutuwar tataba kowa, wannan family sun shiga damuwa sosai, kowa kaga fuskarsa zaka ganshi dauke da damuwa, Su Abba sunso suzo, amma Alhaji Baqir mahaifin Aslam yahanasu zuwa, yace kawai suyi mata addu'ah, Momy ce takira Diddi tafada mata, a lokacin Nihla tana makaranta, bata jira dawowar ta ba tatafi, shikuma Ibrahim Mai hakuri yace bazai iyu su tafi dukansu subar Nihla ba, idan tadawo ranar uku shi sai yaje
Kowa yaganta a family din yasan ta rame, shi kansa yayan nata daya ganta, saida jikinsa yayi sanyi, gaba daya ta sauya Kamar ba itaba
Bayan angama sutura suka koma part din su Momy, anan takejin labarin tafiyar Abba da Aslam karatu germany, duk yaran gidan sunzo sun gaishe ta, Aisha ce kawai bata ganiba, anan Momy take fada mata cewa tana India tana karatu agidan wani abokin Alhaji, saboda ita tadage bazatai karatu anan ba 🤣
Murmushi kawai Diddi tayi, tace "Allah ya kyauta," suna wannan firar Alhaji yashigo, shima zama yayi, Diddi tasake gaida shi, a mamakinta saitaga ya amsa mata cikin sakin fuska, yana murmushi yace "meyasa baki Taho da mamana ba, Tun tana qarama ban sake ganinta ba"
Diddi tace "Nihla tana makaranta yaya, yanzu ma batasan nataho ba, ashe su Abba suntafi germany"
"wallahi su Abba suntafi, shekarar su biyu kenan, sunaso suzo gida ma nahanasu, nace su bari sai sun gama komai tukunna, aide kuna zaune lafiya ko?"
Mamaki yagama kashe Diddi, tace "yaya lafiya kalau,"
"to alhmdlh, idan kin koma sai kiyi harama hajjin bana dake za'a tafi insha Allah, daga nan sai Rahma tarakaki Dubai kisiyo kayaiyaki kifara business ko"
Saboda murna Diddi harda kukan ta, takasa cewa komai, ahankali shima yatashi ya shige ciki, yanaji kukan ta yana taba ransa, to yaya zaiyi tunda auren de bazata rabu dashi ba, gashi harda Rabon yarinya a tsakani, gara yayi hakuri yaja qanwarsa jikinsa
❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️
After 8 year's
Da gudu tashigo gidansu cikin murna tace "Diddiyyy"
Sannan tafada jikinta ta rungumeta
"Nihla ke kadai ma zaki karyani kihuta"
"to Diddi ai ina murna ne, kinga result din nawa"
Karba Diddi tayi cikeda murna tace "a a masha Allah, Allah yamiki albarka Nihla, Allah ya albarkaci ilminki, neco tayi kyau waec tayi kyau, saura jamb insha Allah"
Fari tayi da idonta tace"Diddi, wannan karan da kinaso, da bakyaso Diddi sainaje kano, inaso naga su Anty "
" A a Nihla kede kice kinaso kiga Abba, to ai Abban bai dawoba, saide kije kiga su Antyn Kamar yanda kika min qarya daga farko "🤣
Ajiyar zuciya tasauke, ta cire dogon hijabin jikinta, kanta Babu dankwali qananun kalbar da akayi mata tazubo agadon bayanta, ta zubawa waje daya ido tana kallo batare data cewa Diddi komai ba
Kallanta Diddin tayi cikin murmushi" to yanmatan Diddi, me kuma ake tunani? "
" Diddi, Yaya Abba yana germany har yanzu bai dawoba, Yaya yusif yatafi china shima Yaqi yadawo, duk qawayena basa nan, basusan nayi Candy ba, dama suna nan Diddi, shi yaya Yusif naje umma tabani number sa amma kullum na kirashi bata shiga, saura yaya Abba Dan Allah Diddi kicewa Anty taturo miki number sa na kirashi "
Diddi tace" a a babu ruwana, keda kikace zakije kanon da kanki? Idan kinje sai Antyn tabaki "
" shikkenan Diddi, idan naje Zan dauki wayarta da kaina na dauki number sa na kirashi "
Diddi tace" keni kin dameni da zancen wannan mutanan naki 😂, tashi kije kisiyomin maganin zazzabi, zazzabi nakeji "
"to Diddi"
Kudin tadauka agefenta tafice daga gidan
Gidansu Nihla kenan, Diddi ta manyan ta, bakinta manne da haqorin makkah, Nihla taqara girma, kyanta yana nan sai abinda yaqaru, tazama budurwa, idan ka kalleta saika sake kallonta, surutun ta yana nan yanda yake
Maganin takawo mata tasha, da yamma tagyara gidan tsaf, tayi wanka ta shirya cikin riga da siket, hips dinta yafuto acikinsu siket din sosai, 'yan madedetan breast dinta ma haka, dukda basu cika girma sosai ba, amma kana kallansu zaka tabbatar a tsaye suke sosai
Kusada Diddi tadawo tazauna tace "Diddi ko zazzabin ne? Naga kinyi shiru kina tunani"
Ajiyar zuciya tasauke tace "tashi kidaukomin wayata inkira yaya na,"
Saida tayi daria sannan tadauko mata wayar tana cewa "hajiya Diddi kinaji da wannan yayan naki,kuma ni Diddi banga alamun ma yanada Fara'ah ba wallahi"
"zakici ubanki Nihla, yayan nawa kike fadawa haka?"
Shiru Nihla tayi tana daria, Diddi takira yayan nata, bugu yadauka "Aisha kina lafiya ko"
"lafiya kalau yaya, Ya wajansu Abba kuwa? Sai yaushe zasu dawo ne yaya?"
Cikin mamaki yace "Abba sun kusa dawowa, amma Lafiya Aisha?"
"lafiya kalau yaya, kawai na matsu yadawo ne naganshi,"
Saida yayi Murmushi Wanda saika dade kafin ka ganshi yayi sannan yace "Zai dawo insha Allah, idan zai dawo ai zanturo driver yazo yadauke ki insha Allah"
"to yaya Allah yakaimu, Tokai yaushe zakazo yaya?"
Cikin mamaki yace "Aisha wai kalau kike kuwa?"
Saida tayi Murmushi tace "yaya lafiya ta kalau fa, kawai inaso naganka ne"
Jikinsa ne yayi sanyi, me yarinyar nan take nufi ne? Anya kalau take kuwa? Haka yake ta fada cikin ransa afili sai yace mata "inde nine Zan shirya gobe nazo kiganni Aisha, shikkenan?"
"eh yaya shikkenan, ka gaida Anty Rahma, ga Nihla ma tana gaishe ka,"
Yace "toki shafa min kanta" sannan ya kashe wayar, Diddi kuwa maganarsa dariya tabata, wai ashafa masa kanta Kamar wata 'yar yarinya
Da magrib baba yadawo daga kasuwa, suna zaune sunata fira, zazzabin datake ji ma Babu yatafi, sallama akayi akofar gidan, baba yace su shigo, samari ne guda uku suka shigo da kaya niqi-niqi ahannu, kwalin taliya da macaroni sai doya Mai yawa, sukace Alhaji isma'eeil mahaifin Yusif ne yace akawo musu yayi zakkah ne
Godia sukayi musu, baba yanata yabon kirkin mutumin, duk unguwar kowa yana yana yabonsa
Har dare yayi suna zaune suna fira, sannan sukaje suka kwanta, Diddi yau a dakin Nihla ta kwanta, Nihla ta dade dayin bacci, ahankali Diddi ta matsa kusada ita ta rungumeta a jikinta, sannan tayi musu addu'ah itama ta kwanta
Da asuba Nihla ce tafara tashi, kallan Diddi tayi agefenta tace "Diddi asuba tayi"
Bata jira amsarta ba tatashi taje tayi alwala tazo tatada sallah, harta idar Diddi bata tashi ba
Addu'ah tashafa, takama kafarta tace "Diddi asubafa tayi"
Taji shiru, hijabin jikinta ta cire tace "a a Diddi lafiya kuwa?"
Takoma kanta tana tashin ta, amma Diddi ko motsi batayi ba, gabanta ne yayi muguwar faduwa, tafara ja da baya Ahankali, harta futo tsakar gidansu, adede lokacin baba yadawo daga masallaci hannunsa dauke da carbi yanaja
Cikin tashin hankali tafara nuna masa d'akin da hannun ta, tace "Baba Diddi!"
Yace "Diddi kuma? Me yasameta? Ko zazzabin ne?"
Bata iya bashi amsaba, duk jikinta rawa yake kawai tana nuna masa dakin da hannu, Dasauri yashiga, itama ta doru abayansa
Yana zuwa yasa hannu ya tallafo Diddi jikinsa yace
"Aisha!"
Yaji shiru, gabansa ne yafadi yaduddubata, lokaci daya jikinsa yayi sanyi baisan lokacin daya zauna ba
"Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Aisha, haba Aisha, meyasa zaki tafi kibamu, me.. Yas..sa Aisha" ya qarasa maganar yana kuka wiwi, sake rungumeta yayi yana fadin "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, yanzu Aisha dama tafiya zakiyi kibarmu?"
Cikeda tashin hankali tafara girgiza kanta "A a baba, Diddi bata mutuba, lafiya fa muka kwanta, baba Diddi na bata mutu ba kadena cewa tamutu baba"
Cikin kuka Kamar ba babanta ba yadago kansa ya kalleta yace "Nihla Aisha tamutu, Aisha tatafi ta barmu"😭
(sannu sannu bata hana zuwa saide adade ba'a jeba, dafatan kun gane)
Amnah El Yaqoub ✍️
[6/16, 11:52 PM] El Yaqoub: ❣️ DANGI 'DAYA❣️
{Romance & Friendship luv}
Writing by Amnah El Yaqoub
Like my page On facebook 👇🏻
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/
9&10
Kuka take sosai Kamar ranta zai fita, wai gawar Diddi ce a gabanta Akwance haka, akan idonta makotansu da wasu daga cikin yan'uwan babanta sukayi mata wanka, bata taba tunanin zataci gaba da rayuwa batare da Diddi ba, babu me iya bata hakuri saboda kowa yasan yanda tashaqu da mahaifiyarta, gara abarta tayi kukan ko zataji sassauci
Dole saida aka jinkirta jana'izarta har saida yan kano suka qaraso, dirin motar da sukaji ne ya tabbatar musu da cewa sun qaraso, gaba dayansu sunzo yara da manya, Momy tana kuka tashigo gidan, duk hankalin mutane ya koma kanta, cikin dakin tashige, tana ganin Diddi Akwance anrufeta da farin mayafi tasake sakin kuka tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Allah yaji qanki Aisha"
Nihla ta kalla datake zaune agefe idonta ya kumbura gashi sunyi jajir, Dasauri ta rungumeta, tana bubbuga bayanta "Nihla kidena kuka kinji, kidena kuka bakiyi rashin uwaba, kina damu kinji yata, kidena kuka"
Duk dakin saida suka sakasu kuka, Alhaji ne yashigo Wato yayan Diddi taredasu Alhaji Baqir gaba dayansu, tsugunnawa yayi agaban gawar, yasaka hannu yabude fuskarta, duk jajircewa irinta Alhaji, saida yayi kuka, yasaka dayan hannunsa Yarufe fuskarsa yana kuka sosai, yakasa magana, yadade yana tsugunne a gabanta, Alhaji Baqir da Alhaji Basiru suka jashi, suka fita dashi, sannan sukayi mata addu'ah, aka qarasa shirya ta, ana daukanta za'a fita da ita waje domin sallah Nihla tasaka kuka ta qanqame Momy tace "Anty zasu tafi da ita"
Kasa magana Momy tayi,domin itama wani irin d'aci takeji aranta
Babu yanda suka iya, haka aka sallaci Diddi aka kaita gidanta na gaskiya, saide muce idan tamu tazo Allah yasa mucika da imani
Ranar da akai sadakar uku data bakwai, da yamma lis yan kano sukai shirin tafiya gida, Momy tana zaune da carbi ahannun ta, wayarta ce tayi qara, wayar tana ajiye kusada Nihla, daukar wayar tayi taga ansa Daddyn Abba hakan ya tabbatar da cewa yayan Diddi ne yake kira, meqa mata wayar tayi tace "Anty Daddy yana kiranki"