← Book details Dangi Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 59

Sashe 46

Dangi Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Momy kanta tsaye tace "goron saka ranar qanwar ka ne, na saka ranar auren Nihla ne"

Wani dummm! Yafara ji akansa, gabansa yafara faduwa, numfashinsa yafara yin sama, daqyar ya'iya cewa "Momy saka rana kuma?"

Momy data fara tsorata da yanayin sa yace "emana, menene?"

Hannu yasa yadafe kansa dake masa mugun ciwo, qirjinsa ya riqe numfashi yana neman gagararsa, ahankali yadora dayan hannunsa akan qirjinsa, Idanunsa suka fara rufewa, yafara ganin duhu-duhu har suka rufe gaba daya yadena gani dajin komai, nan take ya sulale awajan yafadi

Cikin sauri Momy tayi kansa tana fadin "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un.... Abba!"

Girgiza shi tafara yi amma Babu alamar numfashi awajan Abba, gaba daya Momy ta rikice sai jijjigashi take, hasbunallah wani'imal wakil... Abinda take guje musu kenan dama, nan take hawaye ya balle mata

Ta kalli Nihla cikin kuka tace" yi sauri ki kira Daddynku mutafi asbiti"

Da gudu tajuya zuwa dakin Daddy yana zaune yana duba jarida, ganin yanda tashigo dakin hankali tashe yasa yatashi tsaye da sauri yace "lafiya?"

"Daddy kazo inji Momy"

Cikin sauri yafuto itama Nihla ta biyo bayansa, yana qarasa wa wajanda Abba ke kwance ya tsugunna yana taba fuskarsa yace "meyasa meshi ne Rahma?"

Cikin kuka tace "Alhaji kaga abinda nake fadama ko? Kaga irinta ko? Babu abinda aka masa, kawai dagajin ansa ranar Nihla shine yayanke jiki yafadi"

Daddy yace "subhanallah... Kamamin shi Muje asbiti"

Daqyar suka dagashi, suka tafi asbiti baki dayansu, sai adala kawai aka bari agidan

Zuwan su asbiti keda wuya likitoci suka karbe shi cikin gaggawa, suka shiga bashi temakon gaggawa, Daddy da Momy kam kasa zama sukai, sai Nihla ce take bawa Momy hakuri akan tadena kukan datake amma ina! Hawaye Yaqi tsayawa a idanun Momy

Sun kusa awa daya da zuwa asibitin sannan likitocin suka futo, cikin sauri suka nufesu suna tambaya

Babban cikin su yace "kuyi hakuri Alhaji, ku kwantar da hankalin ku, amma Dan Allah ku kiyaye fadar abinda zai dinga tsorata mutum lokaci daya, yanzu haka danku yaji abinda ya tsorata shi ne sosai, shiyasa yasuma, kuma dama bugun numfashin sa ba normal yake fitaba sakamakon ciwon da zuciyar sa take son kamuwa dashi "

Daga Momy har Daddy hada baki sukai wajan fadin
" ciwon zuciya Doc.?

Kai tsaye yace "qwarai kuwa, amma tunda kunzo asbiti insha Allah zamuyi kokarin ganin yasamu lafiya, yanzu za'a futo dashi a sauya masa daki"

daga haka ya juya yabasu waje

Momy kasa magana tayi daga nan, kawai de tana goge hawayen idonta, kuma har zuwa yanzu kokadan batajin haushin Nihla, fatanta daya, Allah yabawa danta lafiya

Daddy yakira Alhaji Basiru da Alhaji Baqir ya sanar dasu abinda yake faruwa, nan take suma suka Garzayo asbitin
Cikin lokaci qanqani jinyar Abba tacika family din Mazawaje

❣️❣️❣️ ❣️❣️❣️

Aslam yafi kowa shiga cikin tashin hankali, musanman daya tambayi Momy menene yake faruwa tafada masa komai bata boye masa ba, haka Yazauna yana tunanin mafita
Nihla ya hango tareda Ilham azaune agefe, tana riqeda lil Abba a hannunta

Ahankali yataka yaje wajansu Yazauna, yadubi Nihla tareda miqa mata wayarsa yace "qanwata temakamin da number Angon namu mana"

Murmushi tayi kadan, ta karbi wayar tasa tasaka masa number ya Yusuf aciki, sannan tabashi, ya karba yayi godia

Wayarta ce tahau qara, tana dubawa taga ya Yusuf ne, tadauka

Ilham da Aslam suka kalleta, cikin zazzakar muryarta yace "hello ya Yusuf , yakake yagida"

"lafiya amarya ta, nashigo kano fa, zanzo naganki inaso naji shirye shiryen dakika tsara, saina wuce daga nan"

"Ayya ya Yusuf ai bana gida, munzo asbiti ne, saide nayima kwatancen wajan saimu hadu anan, kaga sai Muje gidama nahadama wani abin kaci"

Be tambayeta waye baida lafiya ba yace "toki turomin adress din Inda kike yanzu"

Sunan asbitin kawai tafada masa yace yana kusa, tace to zata futo waje bakin titi Inda zai ganta

Wayar ta kashe tadubi Ilham tace "zanje waje nadubo ya Yusuf "

Ilham tace "to shikkenan"

Ahankali ta miqe tafuto, Aslam ya kalli Ilham yace "kibita mana, kidan bata shawara ko zata saurareki"

Kallan mijin nata tayi, duk yashiga damuwa, tarasa wacce irin soyaiya sukewa tsakanin su shida ya Abba, tace "to" sannan ta biyo bayan Nihla

Daga murya tayi ta kirata, Nihla ta tsaya ta, sannan ta qaraso sukaci gaba da tafiya
Ilham tace "ya Aslam ne yace nazo naraka ki"

Nihla tace "Allah sarki, kinga salihin miji, wallahi idan ya Abba ne bazai bar matar saba"

Murmushi tayi tace "nikam Nihla nabaki shawara mana"

"inajinki" cewar Nihla

Shiru Ilham tayi, saida suka qaraso bakin titi suna jiran ya Yusuf ya qaraso sannan tace "Nihla Dan Allah meyasa bazaki tausaya wa ya Abba ki aure shiba?"

Cikin sauri ta dago kanta ta kalli Ilham tace "aure fa kikace Ilham"

Hannunta Ilham takama hannunta ta riqe tace "eh, aure nace Nihla, to menene aciki idan kin aure shi? Nihla wacce irin zuciya gareki?yaushe kika koma haka? Mutumin nan yayi miki laifi kuma yabaki hakuri, babu wanda baya aikata kuskure acikin Rayuwar sa Nihla, saide na wani yafi na wani,kidinga tunawa ya Abba dan'uwana ne da'aka bar wasiyya cewa kuyi aure, Nihla ubangijin daya haliccemu ma muna aikata masa laifi muroqeshi gafara yayafe mana, haba Nihla, yanzu ashe bazaki iya tausayawa yaron Momy ba? Bazaki iya ceto yaron Daddy daga halin da yake ciki ba? Nihla wannan shine sakayyar dazaki nunawa Momy kenan? matar da tasoki Tun kina qarama kina gaban mahaifiyarki? Duk cikin yaran Momy Babu Wanda ya qyamaceki Nihla, kowa kokari yake yaga yafaranta ranki, Momy tana qaunar ki Nihla, Inda wata uwarce da tuni ta sauya miki, suna qaunar dansu fa, soyaiyar dasuke miki ce tasa bazasu iya nuna miki komai ba, idan kina tuna laifin dayayi miki bazaki taba yafe masaba, kuma bashi zaki dubaba, a a, iyayen sa zaki duba, kinji de abinda likita yace, zuciyarsa tana gab da kamuwa da ciwo, kuma komai yana hannun ki, idan kinso zaki iya ceto Rayuwar Dan mutanan dasuke kaunarki Kamar yarsu ta cikin su, idan kuma kinso zaki iya barin sa, amma kiyi tunani akai "
Tana gama fada mata tayi shiru tareda sakin hannunta

Zuciyarta fal da tunanin maganganun Ilham, tabbas maganar ta Babu ta yarwa aciki, Momy uwace abar alfahri ako'ina, to amma baban ta fa? Tayaya zata iya nusar dashi? Tayaya zata fuskanci ya Yusuf da wannan maganar? adede lokacin yaqaraso wajansu, suka gaisa cikin kulawa, ahankali suka qarasa cikin asbitin
Ya kalleta yace" yanaga jikinki yayi sanyi ne? Waye baida lafiya? "

Murmushi tayi tace" lafiya ta kalau ya Yusuf , ya Abba ne baida lafiya, dukanmu ma muna ciki, ko zaka qarasa ku gaisa da Momy duk suma suna ciki "

Yace" why not "

Ahankali suka qaraso cikin asbitin, cikeda kulawa Yusuf ya gaisa da kowa, sosai Momy ta ware suka gaisa dashi Kamar Babu abinda yake damunta

Suma su Daddy sun yaba da halin sa sosai, kowa dayake wajan yayaba da tarbiyarsa, babu laifi yanada nutsuwa

Likita ne yazo yace zasu iya shiga su ganshi yanzu, gaba dayansu kuwa suka nufi dakin

Yana kwance hancinsa sanye da oxygen, ga kuma na'ura agefen kansa tana aiki, dakuma wadda take nuna yanayin hawa da Saukar numfashin sa

Cikin sauri Momy ta qarasa wajansa, ta dora kanta agefen gadon tasaki wani irin kuka, tama kasa magana sai kuka datake sosai

Hajiya Farida ce tazo ta janye ta tana bata baki, gaba daya dakin Babu Wanda bai tausayawa Abba ba, ajikin hajiya Faridanma bata dena kukan ba, tari yafara Ahankali, duk hankalinsu saiya dawo kansa, Tun yana tari Ahankali harya dawo yanayi sosai, Aliyu yayi sauri yakira likita, likitan na zuwa yace Dan Allah su fita daga dakin, gaba dayansu suka futo

Aslam yaja Yusuf gefe suna magana, wadda Babu Wanda yasan akan me suke tattaunawa saboda sunyi nesa da mutane

Saida suka gama magana sannan Yusuf yakira Nihla, suka tafi zata rakashi wajan motarsa, har tana mamakin wacce iri magana ya Aslam yayi masa? Kuma menene dalilin karbar number sa awajan ta?
Har gaban motarsa sukaje yashiga Yazauna amma bai rufe motar ba, ta kalleshi tace " banji kace komai ba, akan maganar da mukai waya"

Memakon yabata amsa sai yace "Wancen gayen yacemin sunansa Aslam, yayi min magana akan ki, yace ma ya karbi number ta awajan ki zai kirani kuma sai akai sa'ah nazo, yafadamin saboda ke Abba yake rashin lafiya, kece maganin damuwar sa, yayi min bayani sosai akan hakan, kuma na gamsu da bayanin sa, Nihla why not muhaqura ki auri Abba?"

Mutara zuwa gobe insha Allah 🙏🏻

Sharhi please

Amnah El Yaqoub ✍🏻[7/12, 9:57 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493

51&52

Lokaci daya idanunta suka cicciko da qwallah, ta dubeshi muryarta na rawa tace "ya Yusuf... Mekake fada hakane? Meyasa zaka qini saboda shi?"

"ba saboda shi nafadi wannan maganar ba Nihla, kinsani ina son ki, tunda kina qarama, Tun bansan menene so ba nake tare dake acikin zuciyata, halin da suke ciki shida iyayen sa zaki duba, mutanan nan sun karbeni hannu bibbiyu Babu Wanda ya nunamin komai ko akan fuska, sunada karamci Nihla "

" yanzu me kake nufi kenan?"

" ki auri Abba Nihla"
Batare daya shiryaba hawaye yazubo masa yasaka hannu ya goge cikin sauri sannan Yarufe motar tareda dora kansa akan sitiyarin motar yana kuka

Kallansa tayi tasaki wani irin kuka tareda juyawa ciki aguje tana kuka

Usman dake zaune gefensu Daddy yace "yanzu Daddy ai sai a fadawa su baba Ibrahim adaga wannan aure na Nihla, mu dangin mahaifiyarta bamu shirya ba, saboda Abba bashida lafiya"

Alhaji Baqir yayi Murmushi yace "naga alama de Usman bakason wannan auren ko"

Kansa ya sosa yace "A a kawu, danaga wai hankali ba'a kwance yakeba"

Murmushi yasake yi, amma Daddy de yayi shiru baice komai ba, zuwa yanzu kam kodan ceto Rayuwar dansa yakamata yaje su Gana shida Ibrahim Mai hakuri, yakamata su shirya suje su sameshi

Cikin kuka tashigo wajansu, gaba daya hankalinsu yadawo kanta, Nihla kuwa bata zarce ko'inaba sai wajan Momy, fadawa tayi jikinta tana kuka sosai, Momy tace "me yake faruwa Nihla?keda waye?"
Chapter 46 · 0% Book details