Sashe 39
Atsakanin Soyayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Addu'a yagama tofama Aneesan dake bacci ya juyo ya kalli Ammi yace "ai yanzu hankalin ki ya kwanta ko Maman Fateema? Yarinya babu wuyan duniya dabaki bata, yau tana kasuwa, gobe tana gidan chan yin lalle, wanchan garin yin lalle, ketai aiki takawo miki kudi, kaganta tana shagon chan tana shagon nan, babu kalan Iskan duniyan nan da yarinyar nan bata shaka, ba baki barin yarinya tahuta ya za'ayi bazatai rashin lafiya be eh? An gayamiki ita injin ce?" da sauri Kawu Sani yace "ya isa Yaya yanzu ba lokacin fada bane muna asibiti" cikin fushi Baffa yace "sai anyi fadan, ka barni nafada mata gaskiya tazaci tsoronta akeji, ni uban yarinyar nanne" ya nuna Aneesa dake kwance kan gado yace "ni mahaifin tane, duk duniyan nan a yanzu babu wanda keda iko da ita kaman ni, koko idan aka barki da ita zaki iya aurar da ita ne iyye?" ya tambayi Ammi cikin fushi, yace "tabani yarinya natafi da ita kaduna ta shiga cikin yan uwanta su Rukkaya, da Asiya, da Maimunatu amma taki koko ance miki idan natafi da Aneesan cutar da ita zan dinga yi ne kokina ganin zan zauna nabude ido ina gani ana cutar da Aneesa agida nai shiru ne? Ballema nasan inhar ina raye babu wanda ya isa ya cutar da ita" dan shiru yayi yana kallon Ammi data saukar da kanta kasa yace "wlh kawai banson na tauye miki hakki ne, amma inhar baki shirya kula da yarinyar nan da hannu bibbiyu ba karbanta zanyi kome zai faru yafaru kina jina" dan murmushi Ammi tayi aranta tace "maza kenan su kullum gani suke baka kula da yara da kyau" kujera Baffan yaja yazauna shikuma Kawu Sani yazauna abakin gadon, dago kai Ammi tayi ta kallesu dan murmushi tayi koba komi Baffa tsoho ne kuma yayan baban yarta ce dole tabashi hakkin shi tasan ya isa da ita bawai bai isa bane kawai bataso ya karbe mata abu daya datake gani taji dadi ne aduniya, ahankali tace "kayakuri Baffa, kuyakuri dan Allah, zan kara kiyayewa" shiru yayi baice mata komiba ahankali tace "akwai abinci Baffa nazuba muku" girgiza kai yayi tareda saukar da ajiyan zuciya yace "kibari muyi magriba tukunna, inane ofishin likitan muje maganshi musan nawa zamu biya?" "kana fita ka mike gun zakaga ofishin" kallon sani Baffa yayi yace "kaimuje sabida kome aka rubuta ka karantomin naji" tashi yayi suka wuce suka fita koda sukaje wajen likita cemusu yayi wanda yakawo su jiya asibitin yabiya kudin komi addu'a suka dingamai su Baffa, Dr yace karma suji komi anjima zaizo zasu ganshi saisumai godiya atare duk suka wuce masallaci danyin sallan magriba.
Shigowa sukayi dakin harda likita har lokacin bacci take, Baffa yace "likita wanan baccin baccin lafiya ne daiko" dan murmushi Dr yayi yana zuba wani allura a drip din yace "eh na lafiya ne, wanan ruwan da ake karama ta shike sata wanan baccin shizai sa magun gunan subi jikinta" "to masha Allah" bude kofan da akayi yasa daukan su harda Ammi duk suka juyo suna kallon kofan, Dady ne sanye da manyan kayan dake jikinshi tunna safe sai bodyguard dinshi daya dake biye da shi yariko manya manyan ledoji bin kowa na dakin Dady yay da kallo kafin yakara so ya babbasu hannu suka gaggaisa ya kalli Ammi dake gaban gadon yace "yamai jiki bacci takene" gyadamai kai Ammi tayi ta kalli su Baffa tace "Baffa kutaya mu godiya shiya kawomu asibiti shiya taimaka mana" ta kalli Dady tace "Alhaji ga kawun nin Aneesa daga kaduna suka zo yau" kafin ma Dady yay magana Baffa yakara bashi hannu suka gaisa yace "angode, angode, angode, munji duk abinda kamana daga bakin likita, ubangiji Allah yasaka da alkairi bamu da abin biyanka saidai muna rokon Allahu Subhanahu Wata'ala ya sakamaka da alkhairi" murmushi Dady yayi yace "kudena godemin dan Allah inda ace d'ana baida lafiya koyana neman taimako na tabbatar zaku taimaka mishi kuma ai koba hakaba?" da sauri Baffa yace "maganan ka gaskiya, zamu taimaka mai, ai shi d'a dakake gani nakowa ne, Allah dai ya shirya mana su sanan ya raya mana zuri'a yakare yakuma tsare mana su" atare duk sukace Ameen, Dady ya kalli Ammi yace "tom saida safe, agaidamin da y'ata inta tashi" dan murmushi Ammi tayi tace "Allah yasaka da alkhairi mun gode da dawainiya" Dady ya kalli Baffa da Kawu sani yace "bismillah Alhaji" da sauri Baffa yace "to, to, to, bismillah muje" bude kofa Dady yayi yafita Baffa da kawu sani suka bishi a baya har zuwa wajen asibiti, wani eatry Dady ya shiga suna biye da shi suka zauna kan table, Dady yace "meza akawo mana Alhaji" hannu Baffa yadaga yace "masha Allah akoshe muke, mungode" murmushi Dady yayi still yasa aka kawo musu drinks sanan ya gyara zama yace "masha Allah inamai tsananin farin cikin ganinku ayau, da farko dai sunana Alhaji Muhammad Ibrahim Darham, ina aiki amatsayin senate president of Nigeria, matana uku sanan yarana ashirin, namiji daya gareni wacce matata tafarko wacce Allah yama rasuwane ta haifamin shi" atare Baffa da kawu sukace "Allah yamata rahama" "Ameen, Aliyu sunan yaron saikuma sauran yarana mata, bazan muku karyaba Jiyan nan nafara ganin mahaifiyar Aneesa wuraren sha biyun dare wanda nafi yarda kaddara ce yahada mu dan bancika yin dare a anguwan hakaba na taimaka mata mukakai Aneesa asibiti, Alhaji" yakira Baffa ahankali, amsawa Baffa yayi yace "na'am Alhaji Muhammad" dan murmushi yayi yace "muba yara bane munriga mun manyanta munyi kwana biyun, tun ajiyan dana fahimci kaman mahaifin Aneesan yarasu ne naji mahaifiyarta ta kwanta min arai ainun inata tunanin yanda zan bullowa al'amarin sai gashi kicibus Allah yahadani daku yau kaga yanda Allah ke abunshi ko" yafada yana murmushi yace "da izinin ku amatsayin ku na yan uwan mahaifin marigayin mijinta nakeso inhar kun yarda inason mahaifiyar Aneesa so na aure, auren sunna, kuma karkuji komi Aneesa nariga na dauke ta amatsayin ya inada yara mata guda goma sha tara karata cikin yarana su zama ashirin abin alfahari ne agareni, wanan ce daman maganan danake so namuku da fatan banyi laifi ba bankuma yi karambani ba" washe baki Baffa yayi murmushi fal fuskarshi yace "masha Allah, masha Allah, Alhaji Muhammad ina cikin tsananin farin ciki da wanan batu naka badan komi ba dan shi auren nan dakake ganinshi rahama ne sanan rufin asirin y'a mace ne, tun Fateema na yar shekara biyu mahaifi ta yarasu amma mahaifiyarta taki yarda tai aure, bazan boye makaba banji dadin yanda take rayuwa daga ita sai Aneesan, banji dadi sabida Aneesa yanzu ta tasa wata rana dole tai aure idan tai aure haka takeso ta cigaba da zaman kadaici? Aisai wani ciwo yakamata, abinda za'ayi shine zan sameta da maganan nan yau yau dinan kome tace zan sanar dakai gobe dan zanso ayi auren kafin nakoma kaduna to anriga an girma me za'a wani daga biki kaman bikin yara? To kagani dazaran ta yarda ana sallaman Fateema daga asibiti gobe ko jibi zamuje masallaci adaura auren, zaman su gida su kadai hadari ne gwara yanzu dazaran tadawo karkashin ka saika killace ta nima hankalina zaifi kwanciya nasan cewa na sauke nauyi na lura sanan nakula da iyalin kanina nabada matar shi aure gun kamilin namiji, sanan abu na karshe dazan fadama Alhaji Muhammad shine nayaba da hankalin ka dakuma mutuncin ka yasa kaga na amsa maka maganan nan siteret, dan haka karike amana, karike su amana, kai babba ne, kanada yara mata ka rike Aneesa da mahaifiyarta amana, idan Aneesa na rashin ji kotama badaidaiba ka kirani ni dinan zanzo har gida na lallasa maka ita, ina kuma rokon Allah daya sanya alheri da albarka ciki, mahaifiyar Aneesa kuwa karka damu zamu shawo kanta" murmushi sosai Dady yayi kaman anmai kyautan Aljanna yace "nagode Alhaji, in sha Allah bazaku taba samuna dacin amana ba" murmushi kowa yayi suka mimike bayan Dady ya biya kudin suka fito daga wajen Dady yamusu sallama yatafi.
_*duk wacce takaranta min littafi batare data biyaba, Allah ya isa, idan kinason book dinan chat me up 07012181461*
[14/03, 19:27] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_
_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤
_✍🏿M Shakur_
2️⃣7️⃣
Shigowa sukayi dakin harda likita har lokacin bacci take, Baffa yace "likita wanan baccin baccin lafiya ne daiko" dan murmushi Dr yayi yana zuba wani allura a drip din yace "eh na lafiya ne, wanan ruwan da ake karama ta shike sata wanan baccin shizai sa magun gunan subi jikinta" "to masha Allah" bude kofan da akayi yasa daukan su harda Ammi duk suka juyo suna kallon kofan, Dady ne sanye da manyan kayan dake jikinshi tunna safe sai bodyguard dinshi daya dake biye da shi yariko manya manyan ledoji bin kowa na dakin Dady yay da kallo kafin yakara so ya babbasu hannu suka gaggaisa ya kalli Ammi dake gaban gadon yace "yamai jiki bacci takene" gyadamai kai Ammi tayi ta kalli su Baffa tace "Baffa kutaya mu godiya shiya kawomu asibiti shiya taimaka mana" ta kalli Dady tace "Alhaji ga kawun nin Aneesa daga kaduna suka zo yau" kafin ma Dady yay magana Baffa yakara bashi hannu suka gaisa yace "angode, angode, angode, munji duk abinda kamana daga bakin likita, ubangiji Allah yasaka da alkairi bamu da abin biyanka saidai muna rokon Allahu Subhanahu Wata'ala ya sakamaka da alkhairi" murmushi Dady yayi yace "kudena godemin dan Allah inda ace d'ana baida lafiya koyana neman taimako na tabbatar zaku taimaka mishi kuma ai koba hakaba?" da sauri Baffa yace "maganan ka gaskiya, zamu taimaka mai, ai shi d'a dakake gani nakowa ne, Allah dai ya shirya mana su sanan ya raya mana zuri'a yakare yakuma tsare mana su" atare duk sukace Ameen, Dady ya kalli Ammi yace "tom saida safe, agaidamin da y'ata inta tashi" dan murmushi Ammi tayi tace "Allah yasaka da alkhairi mun gode da dawainiya" Dady ya kalli Baffa da Kawu sani yace "bismillah Alhaji" da sauri Baffa yace "to, to, to, bismillah muje" bude kofa Dady yayi yafita Baffa da kawu sani suka bishi a baya har zuwa wajen asibiti, wani eatry Dady ya shiga suna biye da shi suka zauna kan table, Dady yace "meza akawo mana Alhaji" hannu Baffa yadaga yace "masha Allah akoshe muke, mungode" murmushi Dady yayi still yasa aka kawo musu drinks sanan ya gyara zama yace "masha Allah inamai tsananin farin cikin ganinku ayau, da farko dai sunana Alhaji Muhammad Ibrahim Darham, ina aiki amatsayin senate president of Nigeria, matana uku sanan yarana ashirin, namiji daya gareni wacce matata tafarko wacce Allah yama rasuwane ta haifamin shi" atare Baffa da kawu sukace "Allah yamata rahama" "Ameen, Aliyu sunan yaron saikuma sauran yarana mata, bazan muku karyaba Jiyan nan nafara ganin mahaifiyar Aneesa wuraren sha biyun dare wanda nafi yarda kaddara ce yahada mu dan bancika yin dare a anguwan hakaba na taimaka mata mukakai Aneesa asibiti, Alhaji" yakira Baffa ahankali, amsawa Baffa yayi yace "na'am Alhaji Muhammad" dan murmushi yayi yace "muba yara bane munriga mun manyanta munyi kwana biyun, tun ajiyan dana fahimci kaman mahaifin Aneesan yarasu ne naji mahaifiyarta ta kwanta min arai ainun inata tunanin yanda zan bullowa al'amarin sai gashi kicibus Allah yahadani daku yau kaga yanda Allah ke abunshi ko" yafada yana murmushi yace "da izinin ku amatsayin ku na yan uwan mahaifin marigayin mijinta nakeso inhar kun yarda inason mahaifiyar Aneesa so na aure, auren sunna, kuma karkuji komi Aneesa nariga na dauke ta amatsayin ya inada yara mata guda goma sha tara karata cikin yarana su zama ashirin abin alfahari ne agareni, wanan ce daman maganan danake so namuku da fatan banyi laifi ba bankuma yi karambani ba" washe baki Baffa yayi murmushi fal fuskarshi yace "masha Allah, masha Allah, Alhaji Muhammad ina cikin tsananin farin ciki da wanan batu naka badan komi ba dan shi auren nan dakake ganinshi rahama ne sanan rufin asirin y'a mace ne, tun Fateema na yar shekara biyu mahaifi ta yarasu amma mahaifiyarta taki yarda tai aure, bazan boye makaba banji dadin yanda take rayuwa daga ita sai Aneesan, banji dadi sabida Aneesa yanzu ta tasa wata rana dole tai aure idan tai aure haka takeso ta cigaba da zaman kadaici? Aisai wani ciwo yakamata, abinda za'ayi shine zan sameta da maganan nan yau yau dinan kome tace zan sanar dakai gobe dan zanso ayi auren kafin nakoma kaduna to anriga an girma me za'a wani daga biki kaman bikin yara? To kagani dazaran ta yarda ana sallaman Fateema daga asibiti gobe ko jibi zamuje masallaci adaura auren, zaman su gida su kadai hadari ne gwara yanzu dazaran tadawo karkashin ka saika killace ta nima hankalina zaifi kwanciya nasan cewa na sauke nauyi na lura sanan nakula da iyalin kanina nabada matar shi aure gun kamilin namiji, sanan abu na karshe dazan fadama Alhaji Muhammad shine nayaba da hankalin ka dakuma mutuncin ka yasa kaga na amsa maka maganan nan siteret, dan haka karike amana, karike su amana, kai babba ne, kanada yara mata ka rike Aneesa da mahaifiyarta amana, idan Aneesa na rashin ji kotama badaidaiba ka kirani ni dinan zanzo har gida na lallasa maka ita, ina kuma rokon Allah daya sanya alheri da albarka ciki, mahaifiyar Aneesa kuwa karka damu zamu shawo kanta" murmushi sosai Dady yayi kaman anmai kyautan Aljanna yace "nagode Alhaji, in sha Allah bazaku taba samuna dacin amana ba" murmushi kowa yayi suka mimike bayan Dady ya biya kudin suka fito daga wajen Dady yamusu sallama yatafi.
_*duk wacce takaranta min littafi batare data biyaba, Allah ya isa, idan kinason book dinan chat me up 07012181461*
[14/03, 19:27] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_
_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤
_✍🏿M Shakur_
2️⃣7️⃣