← Book details Atsakanin Soyayya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 133

Sashe 32

Atsakanin Soyayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da sauri Dady yace "nose bleed kuma Aliyu, mekuma yakawo maka nose bleed ana zaune lpy?" yay maganan yana kai hannu zai taba hancin Aliyun da tip din yay jajir, da sauri Aliyu yarike hannun yana kawad da fuskan shi dan baiso ataba dan zafi zaiji yace "nikarka tabamin hanci am fine, ba zafi yakemin ba kuma tuntuni ya tsaya, are you just coming back now Dad? ina kaje kadade haka?" goran ruwan da Dady yagani kan table dinshi mara sanyi ya dauka tareda budewa zai sha yace "bamu gama meeting din dawuri bane, and on my way coming back kuma something happen saida na taimaka ma wata mata da yarta batada lpy na kaisu asibiti gwanin ban tausayi wlh" dan lumshe ido Aliyu yayi tareda shigewa cikin kujera more yace "am sleepy Dad" hanunshi Dady yaja yace "tobaza kaje ka kwanta ba afalo zaka kwana? Ehen Gadanga na that reminds me of something, taso kaji wata magana, tashi, tashi kaji" yadaga Aliyun da sauri yana dan murmushi, turo baki Aliyu yayi kaman zaiyi kuka yatashi zaune yakallai yace "uhmm tell me" matsowa kusa dashi Dady yayi sosai yadaura hanunshi akafada yace "daman kagane wanan aminin nan nawa Alhaji Hassan?" dan yatsine fuska Aliyu yayi yace "what about him?" murmushi Dady yayi yana kara matsowa kusada shi yace "to agidanshi mukaje meeting dazu dana fita, yarshi ce tazo tai serving dinmu, na yaba da hankalinta da natsuwan ta, kasan tareda sukayi school da kanwar ka Hajara a Dubai, sa'an Hajara ce, she's just 24 Zainab, na yaba da natsuwan ta, tama cemin gobe zatazo wajen Hajara, inaso idan tazo kusasanta ka aureta Gadanga, so karkaje ko ina inaso ku sasanta ka aureta batada matsala very quite and obedient girl, kaga yanda kakeda shegen zuciyan nan you need yar yarinya maijin magana, mara hayaniya dazata bika sau da kafa, is just the best choice Son namaka trust you Dad" dariyan iskanci Aliyu ya shiga yi irin na sangartattun yaran nan, Dady yabude baki yana kallonshi instead of yamaji haushi saima washe baki yayi arayuwan shi yanaso yaga Aliyun shi na dariya, yanaso yaganshi he's free and very happy, da kyar Aliyu ya tsayar da dariyan yace "are you for real Dad, like are you serious about this eh Babana?" da sauri Dady daya tsaya yana kallonshi kaman wani TV yana murmushi yace "yes now Boy, am serious, nafada maka she will make a best wife" dan tabe baki Aliyu yayi yadauki wayarshi yana kallo kafin ya dago kai ya kalli Dady yace "please, please Dad kaga am begging you don't start with this neman min mata stuff, am I a kid daza ka wani nemomin mata, ni nama isa aure ne?" baki Dady yarike yana kallonshi yanda yakemai maganan yana turo baki sounding serious saikuma yay murmushi yana girgiza kai yace "kace kaikama isa aure ne, sanan kace are you a kid, wat does your statement and your question makes you now?" dan murmushin rashin gaskiya Aliyu yayi baice komiba ya dauke kai hakan yasa Dady yadanyi dariya yace "stop taking the advantage of the love I have for you Aliyu, kasan dai burin kowani uba ne yaga danshi yay aure ko, I want to see my grand kids Aliyu, banso namutu banga y'ay'anka ba Aliyu" da sauri Aliyu ya kallai jin kalman mutuwan daya fito daga bakinshi dan ko kadan baiso yaji Dady ya ambaci kalman mutuwa, gyadamai kai Dady yayi ganin tarkon daya dana mai yakamashi dan finally yasami full attention nashi, hakan yasa yasake kwantar da murya yace "yes Gadanga, banso namutu banga jikokina ba, kasan shekara na nawa yanzu aduniya? Talatin da takwas ga ishirin da tara ka lissafa, inada shekaru talatin da takwas aduniya mamanka ta haifamin kai kaga yanzu shekaruna sittin da bakwai, rayuwa taja Aliyu, Aliyu tai nisa kullum kara kusantowa da kabari mukeyi, nasan bazan taba kara shekaru dari akan wanan shekarun nawa ba, idan ma nakara to komi mini za'a dingayi" dan shiru yayi yana kallon yanda maganganun shi sukasa Aliyu yay sanyi sosai, dan fuzar da iska Dady yayi yace "is alright, naji nakuma yarda bazan nemama mata ba, konima nafison kazabo mata kafadamin choice dinka, na tattaro abokanai na da yan uwa muje munema maka ita but promise me zaka fito da mata nan da one month, you are 29, a graduate, har masters kanada shi, your company na running perfectly fine wat else kake jira? Promise me zaka fito da mata kwanan nan Son" dan lumshe ido yayi yana ganin fuskar Aneesa namai murmushi kafin ahankali yabude idon ya kalli Dady, hannun Dady yakama yarike ahankali yace "I promise Dad, and karka karamin maganan mutuwa, nothing will happen to you, jikoki harsaika gaji, duk wacce zan aura triplets triplets zata dinga haifowa and every year so get ready jekokin ka will break all your bones and fibers" dariya sosai Dady yayi yace "haka nake so ai, abun nema kenan hausawa sukace wai matar direba ta haifi mota kaga ai tuki har nijar" yasake fashewa da dariya kafin yay shiru ya shafa gashin kan Aliyun yace "nagode Aliyu na, yarona maijin maganan babanshi, Allah yamaka albarka kaji" murmushi yayi yace "Ameen Dad" hanunshi da har yanzu bedawo normal ba Dady ya karba yana kallo yace "tell me the truth what happen to you dazu Aliyu, eh what happen to you? Why were you so angry dazu?"

Dan shiru yayi yana tunanin abinda yafaru dazu da sauri ya kawad da tunanin daga ranshi danji yake kaman zai sume, ahankali yace "never mind Dad, I don't wanna talk about it" dan murmushi Dady yayi ganin baiso yafada mai, amma dai yaso yaji meya sameshi yace "Alright bari naje na watsa ruwa na kwanta, kaima saida safe, jeka kwanta dan ka iya zuwa masallaci da asuba" tashi yayi yana kallon Dady saida yafita sanan yawuce bedroom dinshi singlet din jikinshi tacire dudda dazu yay wanka jiyayi yanaso yasake yi kuma koyaji dadin jikinshi, bathroom yabude ya shiga yakai almost 20min a bayin sanan yafito ya shirya tsaf cikin wani milk color pyjamas ya kashe wutan dakin yarage saura bedside lamp kadai yazo yazauna bakin gado, kasa hakura yayi yadau wayarshi ya shiga contact din Aneesa dayay saving da Boldest yana kallo, bala'in son yakirata yake at the same time kuma baiso yakirata abinda yafaru dazu na mugun bakanta mai rai, kwanciya yayi ahankali kan gadon yadaura wayan kan kirjinshi tareda fuzar da iska dan lumshe ido yayi yana tunane tunane ahaka bacci yay awon gaba dashi.
[10/03, 09:52] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_

_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤

_✍🏿M Shakur_

2️⃣2️⃣

Tana share hawayen dake zubowa daga idanunta da hijabi tana leka motar ta glass duk arude tace "hello, hello, salama alaykum, dan Allah taimaka min za'ayi, dan Allah taimako nake nema, y'ata batada lafiya tana gida unconscious, please kutaimaka ma Y'ata asibiti zaku kaimu" Ammi tai maganan tana sake share hawayen dake zubowa, kallon bodyguard din Dady yayi bayan sun gamajin maganganun da Ammi takeyi yace "wind down" saukar da glass din kasa bodyguard din yayi Ammi tayi tana tsaye wajen mazaunin driver ganin bodyguard sunci bakaken suit da bakin glass, idanu Ammi tadan zaro tabude baki zatai magana bodyguard din yamata pointing baya da hannu yace "talk to my boss" gyadamai kai Ammi tayi arude takoma tabaya, hada ido sukayi da Dady dan wutar cikin motan a kunne yake, da bayan hannu ta goge fuskarta daya kara jikewa da hawaye tace "dan Allah ka taimaka min y'ata batada lpy, tana gida nabarta ita kadai, please dan girman Allah kutaimakamin karta mutu she's my only daughter ita kadai gareni dan Allah kutaimakamin, dan Allah, dan Allah" yanda jikinta ke rawa hawaye na bulbulowa daga idanunta tana sharewa yasa Dady yaji ta bala'in bashi tausayi, he just relate to her condition he just can't imagine yaga Aliyu na ciwo yana ganin rudewan shi saiyafi nata times 8, dan ajiyan zuciya ya fuxar ya kalleta yace "ina ne gidan naku?" da sauri Ammi tamai pointing layinsu tace "wanan layin ne" dan jim Dady yayi yana tunani hakan yasa Ammi tace "wlh da gaske nake ba amanan ka zanci ba, trust me my girl is dying please, dan Allah" ajiyan zuciya Dady yasake saukewa yace "alright I trust you karkici amana, shigo cikin motan" gyadamai kai Ammi tayi bata damuba dan matsalan datake ciki yafi komi ta shiga motar Dady ya matsa dayan gefen itakuma ta zauna kusada kofa tarufo kofan, Dady ya kalli gaban motan yace "let's go" ya kalli Ammi yace "nuna musu gidan" gyadamai kai tayi ta nuna musu layinsu suka shiga har zuwa kofar gidan nasu, akai parking da sauri ta sauka daga motan ta shiga gidan da sauri tana kunna torchlight din wayan Aneesan dake hanunta, dakin Aneesan ta shiga da sauri ganin Aneesan kwance akasa tana convulsing sosai ga nose dinta na bleeding yasa tai wajen da sauri ta dago kanta tana girgizawa ta kurma uban ihu. "Aneesa, Aneesa, ke Fateema haka zakimin eh? Barina zakiyi kaman babanki eh Aneesa, please don't leave me baby girl ke kadai gareni a duniyan nan, banda iyaye banda yan uwa, u are my everything Aneesa, wayyo Allah! Jama'a" Ammi tasake kurma uban ihu not knowing what to do, bama tasan metake ba.
Chapter 32 · 0% Book details