Sashe 41
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hirar su suka ci gaba da yi can Daddy ya tambayi ina Khairyn?, Sai a lokacin Sheikh Imam ya sanar da shi cewa “Ba lallai ta farka a yau ba, saboda shaiɗanun manya ne kuma baƙaƙe, amma akwai maganin da zan baku, ruwan addu'a da kuma wasu addu'oi da za'a ke karanta mata. Idan ta farka za'a iya samun sauyin yanayi game da ita saboda rayuwar da tayi a da duk bata da hankali, don Allah a kula da maganin nan. In ta ware zamu je can garin nasu tunda sun faɗa, sai a tono bisnen a ware shi, daga nan baƙaƙen aljanun zasu bar jikin ta.”
Da “Toh Daddy ya amsa yana ajajjaɓin abun cikin ransa,”.
Sai wajajen Zuhr Daddy ya nemi Hamma Zaki, bayan sunyi sallah a masallacin dake jikin gidan Sheikh Imam ɗin Daddy yasa Hamma Zaki ya ɗauki Khairy ya kaita mota. Da ya dawo Sheikh Imam ya bashi magungunan da kuma addu'oin kamar yadda ya faɗa, ya bawa Daddy ma na Khairy sannan yayi wa Hamma Zaki tunatar wa akan kula da ambaton Allah musamman zikirorin safiya da maraice. Nan suka yi sallama suka dawo gida.
Allah Sarki granny tunda aka tafi da Khairy hankalin ta bai kwanta ba, haka Nenne da sauran mutanen gidan. Horn ɗin motar da suka ji yasa duka suka fito waje suka yi tsaye. Hamma zaki har ya miƙe zai shige part ɗin su Daddy ya dakatar da shi
“Waye kuma zai shiga da ita?”
Ba tare da sanin yadda zai kaita ba ya ɗauko ta sai part ɗin granny, sauran mutanen gidan ma duk suka biyo bayansa cike da alhinin Allah yasa Khairy ba mutuwa tayi ba.
Granny, Nenne, Mommah da kuma Mom duk saida suka zubar da hawaye, Adda Najma uwar tausayi Kam kuka take shaɓe-shaɓe. Su Ayrah dama sun wuce islamiyya.
Har yau Adda Salma a suƙure take, a cewarta itace silar komai, Mommah ma bata sake mata kuma tace duk abinda ya samu yarinyar ta kuka da kanta.
A kan gadon granny ya fire ta daga nan ya fito, magungunan sa ya ɗauka ya wuce part ɗin su.
Granny dake ta famar sharar ƙwalla tana fyace hanci sai haƙuri suke bata.
“Dole nayi kuka mana, yarinyar nan jinta nake kamar yadda nake jin maza, wallahi wani abu ya same ta bazan yafewa kaina ba. Allah Sarki Ummul Khairy”
Daddy ne yayi gyaran murya yace
“Yanzu dai ba wannan ba Hajiya, kiyi haƙuri Allah zai bata lafiya. Sannan waɗannan magungunan ta ne,”
Nan ya faɗa mata yadda za'a yi mata amfani da shi. Mom tace
“Sai naga kamar Hajiya zata takura, ko za'a kaita waje na na kula da ita”
Da sauri granny tayi caraf tace
“Aah Ramatu, barni nayi jinyar Ummul Khairy da kaina, babu wani takurawa”
Kowa sai da ya murmusa don dama da biyu mom tayi maganar.
Nan Daddy yayi musu sharhin yadda abun ya wakana, dagar da aka sha kafin kai ga wannan mataki, kuka dukkan su suke yi, granny tace
“Allah sarki shiyasa nake jin tausayin yarinyar ashe, amma wannan mata in munje can Mai Hana ni muƙe ta da ice ma sai naji dalili”
Fyace hanci tayi tace “Allah sarki ɗaya ta ”
Jikin su Nenne duk yayi sanyi. Nan Daddy ya ɗaura da yi musu nasiha akan suji tsoron Allah su kuma guji shirka, domin mafi munin zunubi itace shirka. Daga nan suka watse granny aka fara jinyar Khairy.
Ɓangaren Hamma Zaki kamar yadda Sheikh Imam yayi masa bayani haka ya fara amfani da maganin, addu'oin ma ya karanta su, tunda ya fara yake ji kamar ana sauƙe masa wani nauyi daga kansa, mugun ɓacin rai da baƙin rai da yake fuskanta tun bikin sa tuni ya fara jin sassauci.
Tunani kuma ya fara kama shi tun bayan yin addu'oin da kuma shafa magani da ruwan addu'ar. Ba abinda ya fara faɗo masa a rai sai batun auren sa, taya ma aka yi ya fara son yarinyar da ta so nuna masa raini ranar bikin girmamawa da akayi masa, wai anya shi yace yana son Auren kuwa shida ko kaɗan baya son tashin hankali?”
Ganin kansa ya fara sarawa yasa ya shiga Toilet ya watsa ruwa tare da ɗauro alwala, daga nan bacci ya ɗauke shi.
_Toh, ko ya zata kaya tsakanin Hamma zaki da Pretty?, Zai ci gaba da zama da ita?, In baku manta ba akwai fansar da iyayen Pretty ke son ɗauka, ko meye dalili?, Khairy fa? Wane irin sauyi kuke tunanin rayuwar ta zata samu?, Su inna Zaliha fa?, Duk cikin littafin ƴar Iya ne, ku ci gaba da bibiyar alƙalamin diamond bhatool_
_In har ba'a comments zan ƙara rage yawan post gaskiya, kuyi comments ni kuma nayi ta Baku update_
Comment & Share Please.
[8/21, 10:36 PM] 𝙳𝚒𝚊𝚖𝚘𝚗𝚍_𝙱𝚑𝚊𝚝𝚘𝚘𝚕💎:
🌸🍀🌸🍀🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
SHAFI NA “““69&70”””
Sai wajajen ƙarfe goma na dare Khairy ta fara mutauniyar tashi, granny da idonta ke kanta tayi maza ta ƙara matsawa kusa da ita. Shafa bayanta ta fara tana faɗin “Ummul Khairy kin tashi?” shiru babu amsa hakan yasa granny kunna bulb na ɗakin. Idanuwanta sun sauƙa ne akan fuskar Khairy da tayi Fayau da ita sai yamutsa fuskar take.
“Khairy” granny ta ƙara ƙiran sunanta a karo na biyu. Ganin ba zata amsa ba yasa granny yin shiru tana zubawa sarautar Allah ido tare da jin ɗumbun tausayin Khairyn na yawo cikin jininta. Tabbas ko maƙiyinta ne yaga irin yanayin da take ciki zai tausaya mata.
Ɓangaren Hamma Zaki sai da yayi amfani da maganin kafin ya kwanta bisa katafaren gadonsa, addu'oin bacci ya karanta sai dai baccin sam yaƙi zuwa masa in banda tunani babu abunda yake yi, wanda kaso 40 ya tafi ne akan sauyin da ya samu a cikin rayuwarsa. This sudden change yasa shi shiga cikin wani yanayi. “Ya Allah” ya furta yana ƙara juyawa akan faffaɗan gadon nashi.
Ganin tunanin yana shirin sanya shi shiga cikin wani mugun yanayi yasa ya fara tunanin maslaha ga rayuwarsa. Tabbas akwai baƙon al'amarin da ya ziyarce shi kwanakin baya, in ba haka ba me yasa zai yi aure so sudden haka?, Bashi da mai bashi amsar yasa yayi tsaki “And the worst part of it mahaukaciya ce matar tawa” ya faɗa cikin ɗacin rai. “Allah sarki yarinyar nan! Ko ta farka kuwa?, I pity the little creature”.
Miƙewa yayi yana sauƙa a kan gadon, direct part ɗin granny ya nufa. Da sallama a bakinshi ya shiga. Granny ta amsa amsa masa cikin sakin fuska lokaci ɗaya kuma fuskar damuwa ta bayyana tattare da ita “Maza kaga yarinyar nan Khairy har yanzu bata tashi ba, anya ba mutuwa ma tayi ba?, Ɗan duba min” sai da ya murmusa kafin ya dube ta yace “Granny ba dai anyi miki bayanin abinda ke damunta ba?” gyaɗa kai tayi sannan yace “To tana da rai, addu'r ki kawai take buƙata a yanzun sannan Sheikh Imam yace ake kunna karatun Alqur'ani a wurin da take”
Da sauri granny ta miƙe ta nufi wayarta ƙirar tecno mai madannai. Ƙira'ar babban ƙari'in nan Sheikh Muhammad Ayyubi ta kunna wanda tuni sautin ya karaɗe ɗakin.
Murmushi yayi cikin ransa yace “She too much care about the little creature”
Mintuna biyar suka shafe babu mai magana, mutsu-mutsunta ne ya dawo da hankalinsu gare ta.
“Ash, kaina!, Iya ta kaina zai cire” da sauri granny ta matsa kusa da ita tana faɗin “Kin tashi, sannu maza bari na kawo miki abinci”
Da ido Hamma Zaki ya nunawa granny ruwan addu'a ai kuwa tayi sauri ta ɗebo ta shafa mata a goahinta sannan ta shafe mata a sauran jikinta sai famar sannu take jera mata.
“Wollah yunwa nake ji, wai haka zan zauna” murmushi yayi yana miƙewa cikin ransa yana ayyana “Wannan da gani dama foodie ce”
Granny ce tayi feeding ɗin ta daga nan ta koma baccin ta.
Washegari Hamma Zaki yayi shirinsa na zuwa Abuja don samarwa kanshi transfer bisa umarnin iyayensa. Bayan ya isa kamar koyaushe ya tarar da gidan cikin datti kamar ba sabon gida ba. Tsaki yayi ya nufi ɗakinta don babu shakka bacci take sai kace kasa. Ai kuwa zatonsa ya tabbata.
Cikin ɓacin rai ya ɗaka mata duka “Tashi kiyi sallah”
Kamar daga sama ta jiyo muryarsa ai kuwa zubur ta miƙe, wallahi har cikin ranta tana ƙaunar Captain Alee.
Hugging nashi tayi zata kai masa peck ya ja gefe “See You, ko salla baki yi ba kina shirin taɓa ni, oya go and pray, ki Kuma same ni a bedroom ɗina” ya faɗa cike da taƙama tare da yamutsa fuska.
Baki Pretty ta sake tana ganin ikon Allah. Tsawon aurensu bai taɓa yi mata magana da irin wannan sigar ba duk da cewa tasan a jininsa ne, kai ta karkatar tana faɗin Allah yasa ba aiki na bane ya ɓaci ba”
Daga haka ta nufi toilet ta ɗauro wanka da alwala. Ko sallar bata yi bata sheƙa kwalliya kamar mai zuwa gasar kyau.
Kitchen ta nufa ta buɗe fridge tare da ɗauko sauran abincin da tayi order jiya, warming tayi sannan ta ɗauka ta wuce Bedroom ɗinsa.
Kwance ta tarar da shi yana lallatsa wayarsa ga kuma wani irin kwarjini da yayi mata. Sai ta tsinci kanta da faɗin “Good morning sweetheart” idan da wayar da yake dannawa tayi magana la'alla ta amsa mata. Kusa da shi ta zauna tana ajiye abincin bisa side drawer. Ba tare da ya tanka mata ba yaci gaba da uzurinsa. Ganin ma ba kulata zai yi ba yasa ta miƙe jiki a saɓule zata fita. Muryarsa ce ta daki dodon kunnenta “Wa ya baki izinin fita?”
Da “Toh Daddy ya amsa yana ajajjaɓin abun cikin ransa,”.
Sai wajajen Zuhr Daddy ya nemi Hamma Zaki, bayan sunyi sallah a masallacin dake jikin gidan Sheikh Imam ɗin Daddy yasa Hamma Zaki ya ɗauki Khairy ya kaita mota. Da ya dawo Sheikh Imam ya bashi magungunan da kuma addu'oin kamar yadda ya faɗa, ya bawa Daddy ma na Khairy sannan yayi wa Hamma Zaki tunatar wa akan kula da ambaton Allah musamman zikirorin safiya da maraice. Nan suka yi sallama suka dawo gida.
Allah Sarki granny tunda aka tafi da Khairy hankalin ta bai kwanta ba, haka Nenne da sauran mutanen gidan. Horn ɗin motar da suka ji yasa duka suka fito waje suka yi tsaye. Hamma zaki har ya miƙe zai shige part ɗin su Daddy ya dakatar da shi
“Waye kuma zai shiga da ita?”
Ba tare da sanin yadda zai kaita ba ya ɗauko ta sai part ɗin granny, sauran mutanen gidan ma duk suka biyo bayansa cike da alhinin Allah yasa Khairy ba mutuwa tayi ba.
Granny, Nenne, Mommah da kuma Mom duk saida suka zubar da hawaye, Adda Najma uwar tausayi Kam kuka take shaɓe-shaɓe. Su Ayrah dama sun wuce islamiyya.
Har yau Adda Salma a suƙure take, a cewarta itace silar komai, Mommah ma bata sake mata kuma tace duk abinda ya samu yarinyar ta kuka da kanta.
A kan gadon granny ya fire ta daga nan ya fito, magungunan sa ya ɗauka ya wuce part ɗin su.
Granny dake ta famar sharar ƙwalla tana fyace hanci sai haƙuri suke bata.
“Dole nayi kuka mana, yarinyar nan jinta nake kamar yadda nake jin maza, wallahi wani abu ya same ta bazan yafewa kaina ba. Allah Sarki Ummul Khairy”
Daddy ne yayi gyaran murya yace
“Yanzu dai ba wannan ba Hajiya, kiyi haƙuri Allah zai bata lafiya. Sannan waɗannan magungunan ta ne,”
Nan ya faɗa mata yadda za'a yi mata amfani da shi. Mom tace
“Sai naga kamar Hajiya zata takura, ko za'a kaita waje na na kula da ita”
Da sauri granny tayi caraf tace
“Aah Ramatu, barni nayi jinyar Ummul Khairy da kaina, babu wani takurawa”
Kowa sai da ya murmusa don dama da biyu mom tayi maganar.
Nan Daddy yayi musu sharhin yadda abun ya wakana, dagar da aka sha kafin kai ga wannan mataki, kuka dukkan su suke yi, granny tace
“Allah sarki shiyasa nake jin tausayin yarinyar ashe, amma wannan mata in munje can Mai Hana ni muƙe ta da ice ma sai naji dalili”
Fyace hanci tayi tace “Allah sarki ɗaya ta ”
Jikin su Nenne duk yayi sanyi. Nan Daddy ya ɗaura da yi musu nasiha akan suji tsoron Allah su kuma guji shirka, domin mafi munin zunubi itace shirka. Daga nan suka watse granny aka fara jinyar Khairy.
Ɓangaren Hamma Zaki kamar yadda Sheikh Imam yayi masa bayani haka ya fara amfani da maganin, addu'oin ma ya karanta su, tunda ya fara yake ji kamar ana sauƙe masa wani nauyi daga kansa, mugun ɓacin rai da baƙin rai da yake fuskanta tun bikin sa tuni ya fara jin sassauci.
Tunani kuma ya fara kama shi tun bayan yin addu'oin da kuma shafa magani da ruwan addu'ar. Ba abinda ya fara faɗo masa a rai sai batun auren sa, taya ma aka yi ya fara son yarinyar da ta so nuna masa raini ranar bikin girmamawa da akayi masa, wai anya shi yace yana son Auren kuwa shida ko kaɗan baya son tashin hankali?”
Ganin kansa ya fara sarawa yasa ya shiga Toilet ya watsa ruwa tare da ɗauro alwala, daga nan bacci ya ɗauke shi.
_Toh, ko ya zata kaya tsakanin Hamma zaki da Pretty?, Zai ci gaba da zama da ita?, In baku manta ba akwai fansar da iyayen Pretty ke son ɗauka, ko meye dalili?, Khairy fa? Wane irin sauyi kuke tunanin rayuwar ta zata samu?, Su inna Zaliha fa?, Duk cikin littafin ƴar Iya ne, ku ci gaba da bibiyar alƙalamin diamond bhatool_
_In har ba'a comments zan ƙara rage yawan post gaskiya, kuyi comments ni kuma nayi ta Baku update_
Comment & Share Please.
[8/21, 10:36 PM] 𝙳𝚒𝚊𝚖𝚘𝚗𝚍_𝙱𝚑𝚊𝚝𝚘𝚘𝚕💎:
🌸🍀🌸🍀🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
SHAFI NA “““69&70”””
Sai wajajen ƙarfe goma na dare Khairy ta fara mutauniyar tashi, granny da idonta ke kanta tayi maza ta ƙara matsawa kusa da ita. Shafa bayanta ta fara tana faɗin “Ummul Khairy kin tashi?” shiru babu amsa hakan yasa granny kunna bulb na ɗakin. Idanuwanta sun sauƙa ne akan fuskar Khairy da tayi Fayau da ita sai yamutsa fuskar take.
“Khairy” granny ta ƙara ƙiran sunanta a karo na biyu. Ganin ba zata amsa ba yasa granny yin shiru tana zubawa sarautar Allah ido tare da jin ɗumbun tausayin Khairyn na yawo cikin jininta. Tabbas ko maƙiyinta ne yaga irin yanayin da take ciki zai tausaya mata.
Ɓangaren Hamma Zaki sai da yayi amfani da maganin kafin ya kwanta bisa katafaren gadonsa, addu'oin bacci ya karanta sai dai baccin sam yaƙi zuwa masa in banda tunani babu abunda yake yi, wanda kaso 40 ya tafi ne akan sauyin da ya samu a cikin rayuwarsa. This sudden change yasa shi shiga cikin wani yanayi. “Ya Allah” ya furta yana ƙara juyawa akan faffaɗan gadon nashi.
Ganin tunanin yana shirin sanya shi shiga cikin wani mugun yanayi yasa ya fara tunanin maslaha ga rayuwarsa. Tabbas akwai baƙon al'amarin da ya ziyarce shi kwanakin baya, in ba haka ba me yasa zai yi aure so sudden haka?, Bashi da mai bashi amsar yasa yayi tsaki “And the worst part of it mahaukaciya ce matar tawa” ya faɗa cikin ɗacin rai. “Allah sarki yarinyar nan! Ko ta farka kuwa?, I pity the little creature”.
Miƙewa yayi yana sauƙa a kan gadon, direct part ɗin granny ya nufa. Da sallama a bakinshi ya shiga. Granny ta amsa amsa masa cikin sakin fuska lokaci ɗaya kuma fuskar damuwa ta bayyana tattare da ita “Maza kaga yarinyar nan Khairy har yanzu bata tashi ba, anya ba mutuwa ma tayi ba?, Ɗan duba min” sai da ya murmusa kafin ya dube ta yace “Granny ba dai anyi miki bayanin abinda ke damunta ba?” gyaɗa kai tayi sannan yace “To tana da rai, addu'r ki kawai take buƙata a yanzun sannan Sheikh Imam yace ake kunna karatun Alqur'ani a wurin da take”
Da sauri granny ta miƙe ta nufi wayarta ƙirar tecno mai madannai. Ƙira'ar babban ƙari'in nan Sheikh Muhammad Ayyubi ta kunna wanda tuni sautin ya karaɗe ɗakin.
Murmushi yayi cikin ransa yace “She too much care about the little creature”
Mintuna biyar suka shafe babu mai magana, mutsu-mutsunta ne ya dawo da hankalinsu gare ta.
“Ash, kaina!, Iya ta kaina zai cire” da sauri granny ta matsa kusa da ita tana faɗin “Kin tashi, sannu maza bari na kawo miki abinci”
Da ido Hamma Zaki ya nunawa granny ruwan addu'a ai kuwa tayi sauri ta ɗebo ta shafa mata a goahinta sannan ta shafe mata a sauran jikinta sai famar sannu take jera mata.
“Wollah yunwa nake ji, wai haka zan zauna” murmushi yayi yana miƙewa cikin ransa yana ayyana “Wannan da gani dama foodie ce”
Granny ce tayi feeding ɗin ta daga nan ta koma baccin ta.
Washegari Hamma Zaki yayi shirinsa na zuwa Abuja don samarwa kanshi transfer bisa umarnin iyayensa. Bayan ya isa kamar koyaushe ya tarar da gidan cikin datti kamar ba sabon gida ba. Tsaki yayi ya nufi ɗakinta don babu shakka bacci take sai kace kasa. Ai kuwa zatonsa ya tabbata.
Cikin ɓacin rai ya ɗaka mata duka “Tashi kiyi sallah”
Kamar daga sama ta jiyo muryarsa ai kuwa zubur ta miƙe, wallahi har cikin ranta tana ƙaunar Captain Alee.
Hugging nashi tayi zata kai masa peck ya ja gefe “See You, ko salla baki yi ba kina shirin taɓa ni, oya go and pray, ki Kuma same ni a bedroom ɗina” ya faɗa cike da taƙama tare da yamutsa fuska.
Baki Pretty ta sake tana ganin ikon Allah. Tsawon aurensu bai taɓa yi mata magana da irin wannan sigar ba duk da cewa tasan a jininsa ne, kai ta karkatar tana faɗin Allah yasa ba aiki na bane ya ɓaci ba”
Daga haka ta nufi toilet ta ɗauro wanka da alwala. Ko sallar bata yi bata sheƙa kwalliya kamar mai zuwa gasar kyau.
Kitchen ta nufa ta buɗe fridge tare da ɗauko sauran abincin da tayi order jiya, warming tayi sannan ta ɗauka ta wuce Bedroom ɗinsa.
Kwance ta tarar da shi yana lallatsa wayarsa ga kuma wani irin kwarjini da yayi mata. Sai ta tsinci kanta da faɗin “Good morning sweetheart” idan da wayar da yake dannawa tayi magana la'alla ta amsa mata. Kusa da shi ta zauna tana ajiye abincin bisa side drawer. Ba tare da ya tanka mata ba yaci gaba da uzurinsa. Ganin ma ba kulata zai yi ba yasa ta miƙe jiki a saɓule zata fita. Muryarsa ce ta daki dodon kunnenta “Wa ya baki izinin fita?”