Sashe 4
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idan Aishatu ta fita maƙwabta babu abun da take sai ɓarna, tun suna shiru har abun ya fara isar su suka fara kai ƙarar ta. Iya da a lokacin ke daure mata gindi sai tace sharri akayi wa ɗiyar ta , hakan ne yasa jama'ar gari suka kafa ƙahon zuƙa kan Ƴar Iya bayan tattarawar sirri da suka yi. Sun riga sun yanke hukuncin hukunta Ƴar Iya a duk lokacin da ta musu ba dai-dai ba sai dai abun da basu sani ba tafi ƙarfin su baki ɗaya.
Wata rana lokacin Ƴar Iya bata wuce shekaru shida ba a haife, ta fita yawon ta da ta saba ne kwatsam ta bi ta layin wani marowacin mutumi. Dai-dai zuwan ta ƙofar gidan mutumin ya fito da langar sa cike da waina. Tunda taga wainar nan kuwa hankalin ta ya tashi, hakan yasa tabi bayan mutumin ko ɗaya ya bata.
Bayan ya zauna a shimfiɗar tabarma irin ta kaba ɗin nan ta iso, ido ta zuba mishi amma abun ka da marowaci bai gane ba. Ganin bashi da niyyar bata yasa ta faki idon sa ta jawo langar ai kuwa ta arta a na kare yayin da take cin Masar shi kuma mutumin bai daina bin ta ba.
Sai da ta cinye tsaf ta daina wanda mutumin gashi abun tausayi ya jigata, ganin hakan yasa ta wulla masa langar ai kuwa rasss sai a kanshi. Tuni ya fashe jini sai zuba yake.
Da ƙyar aka tsayar da jinin a chemist tukunna ya dawo. Wannan dalilin ne yasa mutumin harzuƙa har ya yanke hukuncin kai ƙara fadar Arɗo. Bayan ya faɗawa Arɗo abun da ya faru ne sai Arɗo ya aika a ƙira masa Baffi. Kamar ta sani kuwa lokacin suna zaune a tabarma ta tasa tukunyar ɗumamen safe a gaba sai ci take kamar jaka, ana sallama kuwa ta fita akace tace ana sallama da mai gidan a fada....
Tana isarwa Baffi saƙo ta shiga bukkar Iya, bata jima ba ta fito still hannun ta kwaɓe da ɓakar miyar kuka da ta shafe ko ina na jikin hannun.
Baffi na fita bai tsaya ko ina ba sai a fada, mutanen da ya gani maƙil a fadar ne yasa ya shiga tashin hankali na wani lokaci, lokaci guda da ya tuna da jikar sa Ƴar Iya nan ya gano hala ta aikata wani laifin ne.
Bayan gaisuwa irin ta mutunci da suka yi da Mai martaba kamar kullum.
Mai martaba yayi gyaran murya yace:
“Toh Mallam Musa tunda Allah yayi ka iso da wuri kai tsaye zamu fara abun da ya tara mu”
Cikin sanyin jiki Baffi ya kaɗa kai.
“Toh Malam Musa, kamar yadda kaga na aika a ƙira ka ba wani abu bane ya faru sai wannan abun da JIKAR ka ta wajen Iya ta aikata”
Yana kai nan ya tsaya tare da yiwa dogarai alamar su shigo da mutumin nan. Baki buɗe Baffi ke kallon sa don kuwa abokin sa ne Ishiyaku. Ganin kansa ɗaure da bandage da kuma plaster yasa Baffi maida hankali don jin me Arɗo zai ce.
“Toh Mallam Musa, kamar yadda kaga Mallam Ishiyaku kansa naɗe da kayan ciwo, ba komai ne ya faru da shi ba sai karon da suka yi da jikar ka wacce ta kusa hallaka shi bayan sace masa waina a daro da tayi”
Kasa magana ma Baffi yayi yayinda kunya tabi ta lulluɓe shi, tuni ya sunkuyar da kan sa ƙasa.
Mai martaba ya ƙara gyaran murya yace
“Mallam Musa muna sauraron ka, kayi shiru”
Cikin ƙarfin hali da takaici Baffi yace
“Don Allah Mai martaba ayi wa Ƴar Iya haƙuri in Sha Allah in na koma gida Zan hukunta ta, yaran yanzu ne ka haifa baka haifi halin su ba, don Allah ayi mata afuwa.
Tuni mutanen wurin suka kaure da hayaniya wani yana faɗin
“Wallahi ba zata saɓu ba, ko dai a ɗauko yarinyar nan a hukunta ta ko kuma wallahi mu bi har gida mu nakasa ta.” yayin da wasu ke ganin hakan ba dai-dai bane.
Wani Matashi ɗan azagwai ne ya miƙe yace:
“Wallahi ko yanzu a zo a hukunta ta ko mu mu hukunta ta, yarinya ƙarama duk ta addabi jama'a, Aradu Arɗo in ba'a hukunta taba toh mu zamu bi mu hukunta ta”
Tsawa Arɗo ya buga nan da nan aka yi shiru ana sauraron sa.
“Toh mun ji ƙorafi daga wurin mahaifin mai laifi, Mallam Ishiyaku ya kake ganin za'a yi? Ka haƙura ko kuma sai an ɗauko yarinyar?”
Na gefen shi ne ya zuga shi hakan yasa yace sai dai a ƙira yarinyar.
Arɗo yace “Shikenan ammah miye hukuncin yarinyar?”
Hayaniya ta kacame wasu na faɗin a biya kuɗin raunin da tayi kuma a bata aikin noma da yiwa matan Arɗo aike sannan kullum ayi mata bulala uku da safe. Wasu masu tausayin kuma cewa suke ayi mata haƙuri yarinya ce...cikin zafafan mutanen ne wani ya kalli mai cewa ayi haƙuri yarinya ce yace
“Kutumar uba, toh wallahi yarinyar nan tafi mahaukacin kare haɗari”
Ganin ba zasu yi shiru ba kuma sun tayar da rigima ne Arɗo ya daka tsawa kafin yai gyaran murya.
“Ya isa haka” ya faɗa yana mayar da kallon sa kan Baffi.
“Toh Mallam Musa, kai yanzu me kake ganin za'a yi?”
Bai kai ga bada amsa ba suka ji Muryar yarinya ƙarama wacce bakin ta ma bai gama fita ba tace
“Toh ai ba shi yayi laifin ba nice”
Shiru ne ya wanzu yayin da kowa kallon sa ya koma kan Ƴar Iya da ta tsaya a gaban su ƙyam ko tsoro babu a tattare da ita, nan da nan wasu suka sha jinin jikin su yayin da wasu kuma suke miƙewa tare da yunƙurin kamo ta....
Mu haɗu gobe don jin cigaban yarintar Ƴar Iya!
Ko kuna tunanin zata bari su hukunta ta kamar yadda suke ikirarin hakan?
Duk AMSOSHIN ku na jiran ku, sai mun haɗu.
Ku yi sharing sannan kuyi comments.🥰
*DIAMOND BHATOOL ce!*
[4/27, 5:57 PM] 💎Diamond Bhatool💎:
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
__Fictional story with life full of childhood, entertainment, revenge, betrayal and heart touching love __
SHAFI NA ‘‘‘‘‘7&8’’’’’
Shiru ne ya wanzu yayin da kowa kallon sa ya koma kan Ƴar Iya da ta tsaya a gaban su ƙyam ko tsoro babu a tattare da ita, nan da nan wasu suka sha jinin jikin su yayin da wasu kuma suke miƙewa tare da yunƙurin kamo ta....
Kan uba, yadda zaratan matasa da magidanta ke yunƙurin kawo ma ƙaramar yarinya hari ammah ko gizau bata yi ba yasa masu hankali daga cikin su faɗawa duniyar mamaki.. Sai da taga rabin su sun yo kanta ta zaro silifas ɗin ta guda biyu ta fara buga musu ɗaya bayan ɗaya.
Duk wanda aka bugawa sai kaga ya ja baya ya koma gefe yana shafa kansa, ganin suna watsewa yasa ta gyara tsayuwar ta tana kallon yadda jini ke ɓulɓulowa daga kawunan su wanda hakan ba ƙaramin burge ta yayi ba.
“Hhhhhhh....dama na faɗa muku ai, shegu manyan banja kawai ku a dole jaku ci jalin yalinya kalama ko?, Toh in kun faca” ta ƙarasa tana sakin dariyar mugunta.
Ba tare da ɓata lokaci ba suka fara zamewa ɗaya bayan ɗaya suna wucewa gida saboda jinin da yake zubowa.
Shi kanshi Arɗo ya tsorata da lamarin wannan yarinya, an daɗe ana kawo ƙarar ta yakan ce suyi haƙuri yarinya ce ammah yau ta riga ta goge masa hadda. Idanuwan Ƴar Iya dake yawo kan Arɗo da Baffi da su kaɗai suka rage don tuni dogarai ma suka cika bujen su da iska.
“Baffi ka tashi mu tafi Iya na can tana jiran ka, kai ma Alɗo kana biye wa makalyatan mutanen nan sai na maka naka” ta faɗa tana kallon Baffi.
Da ido Arɗo yayi wa Baffi izinin tafiya don ya sare da al'amarin wannan aljanar yarinya. Bayan sun yi ƴar tafiya Baffi ya ɗan dakata yana Kallo Jikar tashi. Ganin ya tsaya yasa ta juyo tana kallon shi.
“Baffi mu tafi manah”
“A'ah Ƴar Iyan ta sai kin faɗa min me kika yiwa Shayibu kuma da me kika jiwa mutane ciwo”
Dariyar da ta ɗaurewa Baffi kai Ƴar Iya tayi sannan ta maida kallon ta kanshi. Nan ta bashi labarin abun da ya haɗa ta da Ishiyaku, nan Baffi yayi mata faɗa sanann yace.
“Toh da me kika ji musu ciwo kuma”
A hankali ta ciro silifas ɗin ta daga ƙafar ta ta nuna mishi ƙasan su. Wasu Allurai ne a cake sun fi hamsin a cikin kowanne. Abun ya ɗaurewa Baffi kai ganin irin waɗannan allurai a ƙasan takalmin kuma abun mamaki takalmin na ƙafarta ammah ita basu cake ta ba in fact ko leƙowa basu yi ba.
A haka suka wuce gida zuciyar Baffi babu daɗi ga kuma abun da ya ajiye a ranshi na gano dalilin wanann ɗabi'u na Jikar tashi.
Bayan sun je gida bai faɗawa Iya komai ba ammah ya ƙuduri aniyar bincike akan jikar ta sa, haka ranar dai sukuku Baffi yayi ta har dare. Nan tunani ya hana shi sukuni ƙarshe ya fice daga bukkar. Wuri ya samu yana tunanin mafita ga Ƴar Iya daga ƙarshe ya yanke shawar fara ɗaura mata karatun Alqur'ani tunda shi Qur'ani haske ne kuma waraka ga kowacce jinya.
Washegari kuwa Baffi yayi ɗamarar koyar da Ƴar Iya. Bayan gari ya waye ya ƙwalla kiran ta daga bukkar shi jin shiru yasa ya ƙwalla kiran Iya. A nan take sanar da shi Ƴar Iya ta fice sassafe.
Cike da takaici ya koma ya kwanta, sai wajajen Azahar Ƴar Iya ta dawo saboda yunwar da ta koro ta, abincin da yarinyar ke ci kuwa ko samari masu aikin noma biyu iyaka.
Bayan taci abinci Baffi ya tsayar ta ya fara mata karatu sai dai abun haushi ko bismillah ta kasa haddacewa.
Haka Baffi yayi ta ɗawainiya da ita don ganin ta koyi karatu ammah ina ƙwaƙwalwar bata ja, babu abun da ta iya sai neman tsokala.
Wata rana lokacin Ƴar Iya bata wuce shekaru shida ba a haife, ta fita yawon ta da ta saba ne kwatsam ta bi ta layin wani marowacin mutumi. Dai-dai zuwan ta ƙofar gidan mutumin ya fito da langar sa cike da waina. Tunda taga wainar nan kuwa hankalin ta ya tashi, hakan yasa tabi bayan mutumin ko ɗaya ya bata.
Bayan ya zauna a shimfiɗar tabarma irin ta kaba ɗin nan ta iso, ido ta zuba mishi amma abun ka da marowaci bai gane ba. Ganin bashi da niyyar bata yasa ta faki idon sa ta jawo langar ai kuwa ta arta a na kare yayin da take cin Masar shi kuma mutumin bai daina bin ta ba.
Sai da ta cinye tsaf ta daina wanda mutumin gashi abun tausayi ya jigata, ganin hakan yasa ta wulla masa langar ai kuwa rasss sai a kanshi. Tuni ya fashe jini sai zuba yake.
Da ƙyar aka tsayar da jinin a chemist tukunna ya dawo. Wannan dalilin ne yasa mutumin harzuƙa har ya yanke hukuncin kai ƙara fadar Arɗo. Bayan ya faɗawa Arɗo abun da ya faru ne sai Arɗo ya aika a ƙira masa Baffi. Kamar ta sani kuwa lokacin suna zaune a tabarma ta tasa tukunyar ɗumamen safe a gaba sai ci take kamar jaka, ana sallama kuwa ta fita akace tace ana sallama da mai gidan a fada....
Tana isarwa Baffi saƙo ta shiga bukkar Iya, bata jima ba ta fito still hannun ta kwaɓe da ɓakar miyar kuka da ta shafe ko ina na jikin hannun.
Baffi na fita bai tsaya ko ina ba sai a fada, mutanen da ya gani maƙil a fadar ne yasa ya shiga tashin hankali na wani lokaci, lokaci guda da ya tuna da jikar sa Ƴar Iya nan ya gano hala ta aikata wani laifin ne.
Bayan gaisuwa irin ta mutunci da suka yi da Mai martaba kamar kullum.
Mai martaba yayi gyaran murya yace:
“Toh Mallam Musa tunda Allah yayi ka iso da wuri kai tsaye zamu fara abun da ya tara mu”
Cikin sanyin jiki Baffi ya kaɗa kai.
“Toh Malam Musa, kamar yadda kaga na aika a ƙira ka ba wani abu bane ya faru sai wannan abun da JIKAR ka ta wajen Iya ta aikata”
Yana kai nan ya tsaya tare da yiwa dogarai alamar su shigo da mutumin nan. Baki buɗe Baffi ke kallon sa don kuwa abokin sa ne Ishiyaku. Ganin kansa ɗaure da bandage da kuma plaster yasa Baffi maida hankali don jin me Arɗo zai ce.
“Toh Mallam Musa, kamar yadda kaga Mallam Ishiyaku kansa naɗe da kayan ciwo, ba komai ne ya faru da shi ba sai karon da suka yi da jikar ka wacce ta kusa hallaka shi bayan sace masa waina a daro da tayi”
Kasa magana ma Baffi yayi yayinda kunya tabi ta lulluɓe shi, tuni ya sunkuyar da kan sa ƙasa.
Mai martaba ya ƙara gyaran murya yace
“Mallam Musa muna sauraron ka, kayi shiru”
Cikin ƙarfin hali da takaici Baffi yace
“Don Allah Mai martaba ayi wa Ƴar Iya haƙuri in Sha Allah in na koma gida Zan hukunta ta, yaran yanzu ne ka haifa baka haifi halin su ba, don Allah ayi mata afuwa.
Tuni mutanen wurin suka kaure da hayaniya wani yana faɗin
“Wallahi ba zata saɓu ba, ko dai a ɗauko yarinyar nan a hukunta ta ko kuma wallahi mu bi har gida mu nakasa ta.” yayin da wasu ke ganin hakan ba dai-dai bane.
Wani Matashi ɗan azagwai ne ya miƙe yace:
“Wallahi ko yanzu a zo a hukunta ta ko mu mu hukunta ta, yarinya ƙarama duk ta addabi jama'a, Aradu Arɗo in ba'a hukunta taba toh mu zamu bi mu hukunta ta”
Tsawa Arɗo ya buga nan da nan aka yi shiru ana sauraron sa.
“Toh mun ji ƙorafi daga wurin mahaifin mai laifi, Mallam Ishiyaku ya kake ganin za'a yi? Ka haƙura ko kuma sai an ɗauko yarinyar?”
Na gefen shi ne ya zuga shi hakan yasa yace sai dai a ƙira yarinyar.
Arɗo yace “Shikenan ammah miye hukuncin yarinyar?”
Hayaniya ta kacame wasu na faɗin a biya kuɗin raunin da tayi kuma a bata aikin noma da yiwa matan Arɗo aike sannan kullum ayi mata bulala uku da safe. Wasu masu tausayin kuma cewa suke ayi mata haƙuri yarinya ce...cikin zafafan mutanen ne wani ya kalli mai cewa ayi haƙuri yarinya ce yace
“Kutumar uba, toh wallahi yarinyar nan tafi mahaukacin kare haɗari”
Ganin ba zasu yi shiru ba kuma sun tayar da rigima ne Arɗo ya daka tsawa kafin yai gyaran murya.
“Ya isa haka” ya faɗa yana mayar da kallon sa kan Baffi.
“Toh Mallam Musa, kai yanzu me kake ganin za'a yi?”
Bai kai ga bada amsa ba suka ji Muryar yarinya ƙarama wacce bakin ta ma bai gama fita ba tace
“Toh ai ba shi yayi laifin ba nice”
Shiru ne ya wanzu yayin da kowa kallon sa ya koma kan Ƴar Iya da ta tsaya a gaban su ƙyam ko tsoro babu a tattare da ita, nan da nan wasu suka sha jinin jikin su yayin da wasu kuma suke miƙewa tare da yunƙurin kamo ta....
Mu haɗu gobe don jin cigaban yarintar Ƴar Iya!
Ko kuna tunanin zata bari su hukunta ta kamar yadda suke ikirarin hakan?
Duk AMSOSHIN ku na jiran ku, sai mun haɗu.
Ku yi sharing sannan kuyi comments.🥰
*DIAMOND BHATOOL ce!*
[4/27, 5:57 PM] 💎Diamond Bhatool💎:
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
__Fictional story with life full of childhood, entertainment, revenge, betrayal and heart touching love __
SHAFI NA ‘‘‘‘‘7&8’’’’’
Shiru ne ya wanzu yayin da kowa kallon sa ya koma kan Ƴar Iya da ta tsaya a gaban su ƙyam ko tsoro babu a tattare da ita, nan da nan wasu suka sha jinin jikin su yayin da wasu kuma suke miƙewa tare da yunƙurin kamo ta....
Kan uba, yadda zaratan matasa da magidanta ke yunƙurin kawo ma ƙaramar yarinya hari ammah ko gizau bata yi ba yasa masu hankali daga cikin su faɗawa duniyar mamaki.. Sai da taga rabin su sun yo kanta ta zaro silifas ɗin ta guda biyu ta fara buga musu ɗaya bayan ɗaya.
Duk wanda aka bugawa sai kaga ya ja baya ya koma gefe yana shafa kansa, ganin suna watsewa yasa ta gyara tsayuwar ta tana kallon yadda jini ke ɓulɓulowa daga kawunan su wanda hakan ba ƙaramin burge ta yayi ba.
“Hhhhhhh....dama na faɗa muku ai, shegu manyan banja kawai ku a dole jaku ci jalin yalinya kalama ko?, Toh in kun faca” ta ƙarasa tana sakin dariyar mugunta.
Ba tare da ɓata lokaci ba suka fara zamewa ɗaya bayan ɗaya suna wucewa gida saboda jinin da yake zubowa.
Shi kanshi Arɗo ya tsorata da lamarin wannan yarinya, an daɗe ana kawo ƙarar ta yakan ce suyi haƙuri yarinya ce ammah yau ta riga ta goge masa hadda. Idanuwan Ƴar Iya dake yawo kan Arɗo da Baffi da su kaɗai suka rage don tuni dogarai ma suka cika bujen su da iska.
“Baffi ka tashi mu tafi Iya na can tana jiran ka, kai ma Alɗo kana biye wa makalyatan mutanen nan sai na maka naka” ta faɗa tana kallon Baffi.
Da ido Arɗo yayi wa Baffi izinin tafiya don ya sare da al'amarin wannan aljanar yarinya. Bayan sun yi ƴar tafiya Baffi ya ɗan dakata yana Kallo Jikar tashi. Ganin ya tsaya yasa ta juyo tana kallon shi.
“Baffi mu tafi manah”
“A'ah Ƴar Iyan ta sai kin faɗa min me kika yiwa Shayibu kuma da me kika jiwa mutane ciwo”
Dariyar da ta ɗaurewa Baffi kai Ƴar Iya tayi sannan ta maida kallon ta kanshi. Nan ta bashi labarin abun da ya haɗa ta da Ishiyaku, nan Baffi yayi mata faɗa sanann yace.
“Toh da me kika ji musu ciwo kuma”
A hankali ta ciro silifas ɗin ta daga ƙafar ta ta nuna mishi ƙasan su. Wasu Allurai ne a cake sun fi hamsin a cikin kowanne. Abun ya ɗaurewa Baffi kai ganin irin waɗannan allurai a ƙasan takalmin kuma abun mamaki takalmin na ƙafarta ammah ita basu cake ta ba in fact ko leƙowa basu yi ba.
A haka suka wuce gida zuciyar Baffi babu daɗi ga kuma abun da ya ajiye a ranshi na gano dalilin wanann ɗabi'u na Jikar tashi.
Bayan sun je gida bai faɗawa Iya komai ba ammah ya ƙuduri aniyar bincike akan jikar ta sa, haka ranar dai sukuku Baffi yayi ta har dare. Nan tunani ya hana shi sukuni ƙarshe ya fice daga bukkar. Wuri ya samu yana tunanin mafita ga Ƴar Iya daga ƙarshe ya yanke shawar fara ɗaura mata karatun Alqur'ani tunda shi Qur'ani haske ne kuma waraka ga kowacce jinya.
Washegari kuwa Baffi yayi ɗamarar koyar da Ƴar Iya. Bayan gari ya waye ya ƙwalla kiran ta daga bukkar shi jin shiru yasa ya ƙwalla kiran Iya. A nan take sanar da shi Ƴar Iya ta fice sassafe.
Cike da takaici ya koma ya kwanta, sai wajajen Azahar Ƴar Iya ta dawo saboda yunwar da ta koro ta, abincin da yarinyar ke ci kuwa ko samari masu aikin noma biyu iyaka.
Bayan taci abinci Baffi ya tsayar ta ya fara mata karatu sai dai abun haushi ko bismillah ta kasa haddacewa.
Haka Baffi yayi ta ɗawainiya da ita don ganin ta koyi karatu ammah ina ƙwaƙwalwar bata ja, babu abun da ta iya sai neman tsokala.