Sashe 13
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka suka ƙarasa islamiyya kowa bai jin daɗin ranshi...su ma da basu da appointment da shi sun maida hankali saboda tsaro.
Mom da tun ɗazu take jiran shi ya dawo suyi dinner shiru shiyasa tace ma Sarah tazo tayi nata.
Ƙarar wayar shi ne yasa ya fara juyi alamun baccin bai ishe shi ba. Laluɓo wayar yayi yana picking ido rufe tare da kara ta a kunnen shi.
“Hello Buddy, muna kan hanya ni da Sameer da Faruq.”
Cikin Muryar bacci Yaya Zaki yace
“Alright sai kun zo”
Jin alamun bacci yake yasa Yaya Yusuf ƙara cewa
“Buddy, Are u asleep”
“Uhm kawai Hamma Zaki ya iya furtawa”
“Please wake up now, ka ma yi sallah ne?”.
Cikin baccin da ya fara sakin shi yace a'a I'm about to”
“Oyah tashi manah, it's almost past four”
Sallama suka yi Hamma Zaki yayi hanging call ɗin.
Wanka yayi daga nan yayi sallah, yana idarwa ko gama kimtsawa bai yi ba wayar shi ta fara ringing.
“Buddy, we're here...ka zo ka shigar da mu”
“Idan gidan baƙon ka ne ka zauna a yadda kake bayan ka nuna wa sauran hanya.” daga haka yayi hanging call ɗin yana tsaki.
Sun jima tare da su Yaya Yusuf, Barr. Sameer, da kuma Dr. Faruq. Sai wajajen maghrib suka fice tare zuwa masjid daga can suka wuce.
[5/1, 1:16 PM] 💎Diamond Bhatool💎:
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
__Fictional story with life full of childhood, entertainment, revenge, betrayal and heart touching love __
SHAFI NA ‘‘‘‘‘21&22’’’’’
Sai bayan ya dawo daga masallaci su Fauzah suka zo yi mishi Barka da dawowa tare da sauran yaran gidan.
A lokacin yana zaune a sofa dake parlourn, ɗauke da sallama a bakin su suka shigo. Ƙasa-ƙasa ya amsa sallamar tasu ba tare da ya ɗago ya kalle su ba sai ma hankalin sa da ya mayar ga system ɗin dake gaban shi.
Ƙasan lallausan carpet ɗin dake shimfiɗe a parlourn suka tsuguna yayin da Hamma Zaki bai ma nuna ya sa su ba neh.
Fauzah ce tayi ƙarfin halin faɗin.
“Ina yini Yaya ka iso lafiya?”
Banza yayi da ita ammah hakan bai sa sauran buɗe baki su maimaita abun da ta faɗa ɗin ba saboda sarai sun san halinsa, tsab in suka yi shiru suna jiran amsar yace zai hukunta su. Dukkan su miƙewa suka yi a sukwane zasu wuce suka ji gyaran Muryar shi. Nan suka dawo suka zube kamar bayi a gaban sarki.
“Wa ya baki izinin tafiya?”
Rarraba idanu suka fara wannan ta kalli wannan sai su sunkuyar da kai ƙasa.
“Kayi haƙuri Yaya Zaki”
Ayrah ta faɗa a tsorace. Wani irin kallo da yake bin su da shi yasa suka ƙara shiga taitayin su.
“Yaya ko?, Haven't I warned u several times ku daina ce min Yaya?, Idan bazaku kira Ni da yadda yare yace a faɗa ba U better keep ur dirty mouths shut, ohk?”
Duk wannan jawabin yana yin sa ne cikin harshen fulatanci, nan da nan na ƙara jin ya fi burge Ni fiye da da.
Kawunan su suka ɗaga tare da faɗin
“Toh Hammah Zaki”
Banza yayi da su can yace
“Better”.
Sun share fiye da mintuna 30 a zaune ba tare da yace su tafi ba su kuma suna tsoron tafiya ya hukunta su. Duk zaman nasu gashi ya takura shi can ya ɗago yana musu alama da hannu da su tafi.
Tsam suka miƙe suka wuce banda Najma da Yesmeen da suke durƙushe still.
Lokacin su da suka ga yana ƙurewa yada Najma yin ta maza tace
“Hamma Zaki ɗazu ka ce mu zo mu same ka Ni da Yesmeen”
Har sai da ta cire ran tankawar shi taji yace.
“Kuna ji na koh? Ke Yesmeen bana son rashin kunya kina ji?”
Kai ta ɗaga sannan can ya ci gaba “Idan kika ƙara yi wa wanda ya fiki Allah ya isa to ranar Ni da ke a gidan nan.”
Kamar wanda aka sa dole ya ɗanyi shiru na wasu mintuna dan ba ƙaramar jarumta yayi ba, har kan shi ya fara sarawa.
“Ke kuma Najma banda cin zali kina ji na?, Idan anyi miki abu ki kai ƙara ba ki ɗau hukunci a hannun ki ba, ohk?”
Kai suka kaɗa suna faɗin “Eh”
Daga haka ya musu alama da su wuce.
Ya jima zaune a parlourn yana aiki a nutse cikin system nashi, har lokacin da Sarah ta leƙo ta gan shi.
Komawa tayi tare da sheƙa wanka ta sanya wasu nighties masu bayyana jiki, sai da ta fesa turare mai uban yawa ta fito. Tray ɗin abinci ta haɗa masa tayi sama sai ɗakin shi.
Lokacin da ta shiga ya fito daga wanka daga shi sai bathrobe sai kuma towel ɗin da yake goge sumar shi. Kallon da ya aika mata yasa tana ajiye tray ɗin ta fita da sauri. Shi kuwa Hamma Zaki duk ranshi ya gama ɓaci, shin wai duk mata haka suke ne?, Basu da kamun kai gabaɗaya?, If yes to su sani shi babu budget ɗin aure ma a rayuwar shi. Bai taɓa ko da hasashen kan shi a matsayin wanda zai yi aure ba.
(Nace ayi dai mu gani, in tusa zata hura wuta).
Ko bayan dawowar Daddy da bai tarar da shi a parlour tare da Mom ɗin shi ba yasa yayi tunanin ko bacci yayi tunda ba wani hutawa yayi ba.
★★★★★★★★★★★
*ƳAR IYA POV*
Wasa wasa sati guda kenan Ƴar Iya bata shiga sabgar kowa ba haka babu mai shiga tata saboda tsoro. Aunty Ajiram kaɗai ke samun magantuwa da ita cikin sauƙi kuma Alhamdulillah su Ƴar Iya cikin satin nan an iya ABCD zuwa Z wanda duk ƙwarin guiwar ta same ta ne daga Aunty Ajiram. Wasu lokutan takan ƙarfafa mata guiwa da rayuwar birni tuni Ƴar Iya an fara dagewa da karatu.
Malaman ma sukan yi mata uzuri duk iya shegen da zata yi basa tanka mata, idan kuma aka samu matsala sai su nemo Aunty Ajiram.
Dawowar su daga classroom kenan zasu je dining, Ƴar Iya babu abinda ke damun ta irin rashin cin abinci isasshe, sai a wani zuba mata abincin da ko baki baya wuce mata bare ya ƙarasa wuya har ya shiga ciki. (A faɗar ta kenan).
Bayan an zuba musu sun cinye taji bata ƙoshi ba ai kuwa ta ɗauki bowl nata ta koma wurin matar da ke serving nasu.
Ba tare da tace komai ba ta miƙa bowl ɗin da nufin a ƙara mata.
Abun ya ɗaurewa mai raba abincin kai don ita a tsawon aikin ta a nan almost 12-13years Bata taɓa zuba abinci wani ya dawo da sunan ƙari ba. Kallon mamaki take bin Ƴaƴan Iya da shi ko ina dalili gashi da gani sabuwar ɗaliba ce don bata san ta ba.
Students da basu bar dining ba tsayawa suka yi suna ganin ikon Allah, don kuwa so suke suga wannan drama ta Mama Jebu da Angel 👼 (Sunan da suka bata kenan don wannan basa mata kallon mutum cikakkiya).
Basu san ya aka yi ba kawai suka jiyo Muryar ta tana faɗin
“Kinga bigi-bigi bombom ki ƙara min bai ishe Ni ba”
Dariya students ɗin suka yi jin sunan da Angel ta ƙira Mama Jebu da shi, ai kuwa sunan ya dace da ita. Mama Jebu irin matan nan ne manya manya masu ƙirar maza, gata da ƙaton ɗuwawu don kuwa da ƙyar take tafiya kawai ƙarfin hali ne da neman halal ya danne ta har take iya wannan aikin na raba abinci wa ƴan makaranta.
Kallon banza Mama Jebu ta aiko mata tana faɗin “Ke amma sabuwar ɗaliba ce naga sai wani karambani kike yi?”
Ƴar Iya bata kula ta ba saboda Aunty Ajiram na gwaɓar ta kan ta koyi haƙuri thatz why ta ƙara miƙa bowl ɗin ta gaban Mama Jebu.
“Jiran ki nake bigi-bigi bombom”
Ai kuwa sai a lokacin Mama Jebu taji sunan da sabuwar ɗalibar ta ƙira ta da shi. A hasale ta zagayo daga gaban tukunyar tayi kan Ƴar Iya. Ƴar Iya da bata yi tsammani ba kawai taji dundu a bayan ta. Babu shiri ta janyo robar yaji da ta gani a gefen tukunyar, bata tsaya ɓata lokaci ba ta ɗiba ta watso wa Mama Jebu a ido.
Ihu Mama Jebu ta saka
“Wayyo Allah na na shiga uku, jama'a ku kawo ɗauki wayyoh wayyoh na shiga uku wayyoh ido na shikenan don Allah jama'a a taimaka min”
Ja da baya Ƴar Iya ta yi ganin Mama Jebu na ihu tana sowa, ga kuma lalume-lalume da take yi ganin ta taɓo wani.
Dariya sauran students suka fara wasu na madallah musamman foodies irin Ƴar Iya yayin da wasu ke jin tausayin ta amma babu damar taimaka mata, su je garin taimako Ƴar Iya ta dawo kan su?, A'a babu ruwan su.
Ana cikin haka wata student ta lallaɓa ta tafi clinic don samowa Mama Jebu ɗauki. Ƴar Iya kuwa kujera ta samu tana babbaka dariyar ta. Bata yi aune ba taji Muryar Aunty Ajiram na doka mata ƙira.
“A'ishatu A'isha”
Bata amsa ba sai ta lallaɓa bayan Mama Jebu da ke rausa ihu jikin ta sharƙaf da gumi da hawaye har da majina. ta ɓuya, ƙara damƙo wani yajin tayi a hannun ta, a hankali ta fara ware zanin Mama Jebu ta watsa mata tare da arta a na kare.
Bayan clinician ɗin yazo da ƙyar aka samu manya manyan students dake senior class suka tallafawa Mama Jebu aka wuce da ita clinic.
Taimakon gaggawa aka bata amma ina ta kasa buɗe idanuwan ta.
Duk wannan tsiya da Ƴar Iya ta tsula babu wanda yayi gigin kai ƙarar ta saboda tsoron abun da zai je ya dawo.
Washegari da yamma dai da ƙyar idon Mama Jebu ya buɗe, duk ta bi ta faɗa har abun tausayi. Bayan ta ji sauƙi clinician ɗin ya tambaye ta meh ya faru da idon nata, garin yaya ta zuba yaji haka a ciki.
Bayanin abinda ya faru tsakanin ta da sabuwar ɗaliba ta bashi tare da roƙon shi don Allah ya taya ta neman fada wurin Principal a samu a koru ɗalibar nan in ba haka ba zata iya kashe mutum wallahi.
Mom da tun ɗazu take jiran shi ya dawo suyi dinner shiru shiyasa tace ma Sarah tazo tayi nata.
Ƙarar wayar shi ne yasa ya fara juyi alamun baccin bai ishe shi ba. Laluɓo wayar yayi yana picking ido rufe tare da kara ta a kunnen shi.
“Hello Buddy, muna kan hanya ni da Sameer da Faruq.”
Cikin Muryar bacci Yaya Zaki yace
“Alright sai kun zo”
Jin alamun bacci yake yasa Yaya Yusuf ƙara cewa
“Buddy, Are u asleep”
“Uhm kawai Hamma Zaki ya iya furtawa”
“Please wake up now, ka ma yi sallah ne?”.
Cikin baccin da ya fara sakin shi yace a'a I'm about to”
“Oyah tashi manah, it's almost past four”
Sallama suka yi Hamma Zaki yayi hanging call ɗin.
Wanka yayi daga nan yayi sallah, yana idarwa ko gama kimtsawa bai yi ba wayar shi ta fara ringing.
“Buddy, we're here...ka zo ka shigar da mu”
“Idan gidan baƙon ka ne ka zauna a yadda kake bayan ka nuna wa sauran hanya.” daga haka yayi hanging call ɗin yana tsaki.
Sun jima tare da su Yaya Yusuf, Barr. Sameer, da kuma Dr. Faruq. Sai wajajen maghrib suka fice tare zuwa masjid daga can suka wuce.
[5/1, 1:16 PM] 💎Diamond Bhatool💎:
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
__Fictional story with life full of childhood, entertainment, revenge, betrayal and heart touching love __
SHAFI NA ‘‘‘‘‘21&22’’’’’
Sai bayan ya dawo daga masallaci su Fauzah suka zo yi mishi Barka da dawowa tare da sauran yaran gidan.
A lokacin yana zaune a sofa dake parlourn, ɗauke da sallama a bakin su suka shigo. Ƙasa-ƙasa ya amsa sallamar tasu ba tare da ya ɗago ya kalle su ba sai ma hankalin sa da ya mayar ga system ɗin dake gaban shi.
Ƙasan lallausan carpet ɗin dake shimfiɗe a parlourn suka tsuguna yayin da Hamma Zaki bai ma nuna ya sa su ba neh.
Fauzah ce tayi ƙarfin halin faɗin.
“Ina yini Yaya ka iso lafiya?”
Banza yayi da ita ammah hakan bai sa sauran buɗe baki su maimaita abun da ta faɗa ɗin ba saboda sarai sun san halinsa, tsab in suka yi shiru suna jiran amsar yace zai hukunta su. Dukkan su miƙewa suka yi a sukwane zasu wuce suka ji gyaran Muryar shi. Nan suka dawo suka zube kamar bayi a gaban sarki.
“Wa ya baki izinin tafiya?”
Rarraba idanu suka fara wannan ta kalli wannan sai su sunkuyar da kai ƙasa.
“Kayi haƙuri Yaya Zaki”
Ayrah ta faɗa a tsorace. Wani irin kallo da yake bin su da shi yasa suka ƙara shiga taitayin su.
“Yaya ko?, Haven't I warned u several times ku daina ce min Yaya?, Idan bazaku kira Ni da yadda yare yace a faɗa ba U better keep ur dirty mouths shut, ohk?”
Duk wannan jawabin yana yin sa ne cikin harshen fulatanci, nan da nan na ƙara jin ya fi burge Ni fiye da da.
Kawunan su suka ɗaga tare da faɗin
“Toh Hammah Zaki”
Banza yayi da su can yace
“Better”.
Sun share fiye da mintuna 30 a zaune ba tare da yace su tafi ba su kuma suna tsoron tafiya ya hukunta su. Duk zaman nasu gashi ya takura shi can ya ɗago yana musu alama da hannu da su tafi.
Tsam suka miƙe suka wuce banda Najma da Yesmeen da suke durƙushe still.
Lokacin su da suka ga yana ƙurewa yada Najma yin ta maza tace
“Hamma Zaki ɗazu ka ce mu zo mu same ka Ni da Yesmeen”
Har sai da ta cire ran tankawar shi taji yace.
“Kuna ji na koh? Ke Yesmeen bana son rashin kunya kina ji?”
Kai ta ɗaga sannan can ya ci gaba “Idan kika ƙara yi wa wanda ya fiki Allah ya isa to ranar Ni da ke a gidan nan.”
Kamar wanda aka sa dole ya ɗanyi shiru na wasu mintuna dan ba ƙaramar jarumta yayi ba, har kan shi ya fara sarawa.
“Ke kuma Najma banda cin zali kina ji na?, Idan anyi miki abu ki kai ƙara ba ki ɗau hukunci a hannun ki ba, ohk?”
Kai suka kaɗa suna faɗin “Eh”
Daga haka ya musu alama da su wuce.
Ya jima zaune a parlourn yana aiki a nutse cikin system nashi, har lokacin da Sarah ta leƙo ta gan shi.
Komawa tayi tare da sheƙa wanka ta sanya wasu nighties masu bayyana jiki, sai da ta fesa turare mai uban yawa ta fito. Tray ɗin abinci ta haɗa masa tayi sama sai ɗakin shi.
Lokacin da ta shiga ya fito daga wanka daga shi sai bathrobe sai kuma towel ɗin da yake goge sumar shi. Kallon da ya aika mata yasa tana ajiye tray ɗin ta fita da sauri. Shi kuwa Hamma Zaki duk ranshi ya gama ɓaci, shin wai duk mata haka suke ne?, Basu da kamun kai gabaɗaya?, If yes to su sani shi babu budget ɗin aure ma a rayuwar shi. Bai taɓa ko da hasashen kan shi a matsayin wanda zai yi aure ba.
(Nace ayi dai mu gani, in tusa zata hura wuta).
Ko bayan dawowar Daddy da bai tarar da shi a parlour tare da Mom ɗin shi ba yasa yayi tunanin ko bacci yayi tunda ba wani hutawa yayi ba.
★★★★★★★★★★★
*ƳAR IYA POV*
Wasa wasa sati guda kenan Ƴar Iya bata shiga sabgar kowa ba haka babu mai shiga tata saboda tsoro. Aunty Ajiram kaɗai ke samun magantuwa da ita cikin sauƙi kuma Alhamdulillah su Ƴar Iya cikin satin nan an iya ABCD zuwa Z wanda duk ƙwarin guiwar ta same ta ne daga Aunty Ajiram. Wasu lokutan takan ƙarfafa mata guiwa da rayuwar birni tuni Ƴar Iya an fara dagewa da karatu.
Malaman ma sukan yi mata uzuri duk iya shegen da zata yi basa tanka mata, idan kuma aka samu matsala sai su nemo Aunty Ajiram.
Dawowar su daga classroom kenan zasu je dining, Ƴar Iya babu abinda ke damun ta irin rashin cin abinci isasshe, sai a wani zuba mata abincin da ko baki baya wuce mata bare ya ƙarasa wuya har ya shiga ciki. (A faɗar ta kenan).
Bayan an zuba musu sun cinye taji bata ƙoshi ba ai kuwa ta ɗauki bowl nata ta koma wurin matar da ke serving nasu.
Ba tare da tace komai ba ta miƙa bowl ɗin da nufin a ƙara mata.
Abun ya ɗaurewa mai raba abincin kai don ita a tsawon aikin ta a nan almost 12-13years Bata taɓa zuba abinci wani ya dawo da sunan ƙari ba. Kallon mamaki take bin Ƴaƴan Iya da shi ko ina dalili gashi da gani sabuwar ɗaliba ce don bata san ta ba.
Students da basu bar dining ba tsayawa suka yi suna ganin ikon Allah, don kuwa so suke suga wannan drama ta Mama Jebu da Angel 👼 (Sunan da suka bata kenan don wannan basa mata kallon mutum cikakkiya).
Basu san ya aka yi ba kawai suka jiyo Muryar ta tana faɗin
“Kinga bigi-bigi bombom ki ƙara min bai ishe Ni ba”
Dariya students ɗin suka yi jin sunan da Angel ta ƙira Mama Jebu da shi, ai kuwa sunan ya dace da ita. Mama Jebu irin matan nan ne manya manya masu ƙirar maza, gata da ƙaton ɗuwawu don kuwa da ƙyar take tafiya kawai ƙarfin hali ne da neman halal ya danne ta har take iya wannan aikin na raba abinci wa ƴan makaranta.
Kallon banza Mama Jebu ta aiko mata tana faɗin “Ke amma sabuwar ɗaliba ce naga sai wani karambani kike yi?”
Ƴar Iya bata kula ta ba saboda Aunty Ajiram na gwaɓar ta kan ta koyi haƙuri thatz why ta ƙara miƙa bowl ɗin ta gaban Mama Jebu.
“Jiran ki nake bigi-bigi bombom”
Ai kuwa sai a lokacin Mama Jebu taji sunan da sabuwar ɗalibar ta ƙira ta da shi. A hasale ta zagayo daga gaban tukunyar tayi kan Ƴar Iya. Ƴar Iya da bata yi tsammani ba kawai taji dundu a bayan ta. Babu shiri ta janyo robar yaji da ta gani a gefen tukunyar, bata tsaya ɓata lokaci ba ta ɗiba ta watso wa Mama Jebu a ido.
Ihu Mama Jebu ta saka
“Wayyo Allah na na shiga uku, jama'a ku kawo ɗauki wayyoh wayyoh na shiga uku wayyoh ido na shikenan don Allah jama'a a taimaka min”
Ja da baya Ƴar Iya ta yi ganin Mama Jebu na ihu tana sowa, ga kuma lalume-lalume da take yi ganin ta taɓo wani.
Dariya sauran students suka fara wasu na madallah musamman foodies irin Ƴar Iya yayin da wasu ke jin tausayin ta amma babu damar taimaka mata, su je garin taimako Ƴar Iya ta dawo kan su?, A'a babu ruwan su.
Ana cikin haka wata student ta lallaɓa ta tafi clinic don samowa Mama Jebu ɗauki. Ƴar Iya kuwa kujera ta samu tana babbaka dariyar ta. Bata yi aune ba taji Muryar Aunty Ajiram na doka mata ƙira.
“A'ishatu A'isha”
Bata amsa ba sai ta lallaɓa bayan Mama Jebu da ke rausa ihu jikin ta sharƙaf da gumi da hawaye har da majina. ta ɓuya, ƙara damƙo wani yajin tayi a hannun ta, a hankali ta fara ware zanin Mama Jebu ta watsa mata tare da arta a na kare.
Bayan clinician ɗin yazo da ƙyar aka samu manya manyan students dake senior class suka tallafawa Mama Jebu aka wuce da ita clinic.
Taimakon gaggawa aka bata amma ina ta kasa buɗe idanuwan ta.
Duk wannan tsiya da Ƴar Iya ta tsula babu wanda yayi gigin kai ƙarar ta saboda tsoron abun da zai je ya dawo.
Washegari da yamma dai da ƙyar idon Mama Jebu ya buɗe, duk ta bi ta faɗa har abun tausayi. Bayan ta ji sauƙi clinician ɗin ya tambaye ta meh ya faru da idon nata, garin yaya ta zuba yaji haka a ciki.
Bayanin abinda ya faru tsakanin ta da sabuwar ɗaliba ta bashi tare da roƙon shi don Allah ya taya ta neman fada wurin Principal a samu a koru ɗalibar nan in ba haka ba zata iya kashe mutum wallahi.