← Book details Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 49

Sashe 23

Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zama suka yi tare a taburmar Saratu ta gaishe da Ƴar Iya ita kuma ta amsa. Daga nan ta miƙa hannu ta jawo daron kayan sana'ar ta........

COMMENT & SHARE PLEASE!

[5/18, 10:47 AM] 💎Diamond Bhatool💎:

🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀

_NA_

*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*

__Fictional story with life full of childhood, entertainment, revenge, betrayal and heart touching love __

SHAFI NA ‘‘‘‘“36&37”””

Zama suka yi tare a taburmar Saratu ta gaishe da Ƴar Iya ita kuma ta amsa. Daga nan ta miƙa hannu ta jawo daron kayan sana'ar ta.
Da mamaki Saratu ke kallon Ƴar Iya ganin dai dagaske take. Murmusawa Ƴar Iya tayi tace
“To Saratu Amaryar Arɗo...ga ƴar iya tazo neman halalin ta, kuyi mata ciniki.”
Riƙe haɓa Saratu tayi tace
“Toh Hajiya Ƴar Iya ai dole ayi maki ciniki, meyeh wannan ɗin?” ta tambaya tare da ɗaukar ƙulli ɗaya tana ƙarewa abun kallo, ganin bata gane meyeh ba yasa ta kaiwa hanci.

Hannun ta Ƴar Iya ta buge tare da wafce ƙullin tana aika mata harara.
“Ungo wannan” ta miƙa mata ƙullin
“Maganin mata ne sadidan da kike gani, Aljanu ne suka bani sirrin wannan maganin da nace musu ina son fara samun halal ɗinah”
Tsurewa Saratu tayi jin an ce Aljanu tare da damƙe ƙullin a hannun ta.
Ganin yanayin da Saratu ta shiga yasa Ƴar Iya kwantar da murya ƙasa sannan tace:
“Kina ji na ko Amaryar Arɗo?” gyaɗa kai saratu tayi
“Kinga wannan ƙullin ba wa kowa zan sayarwa ba saboda tsadar sa, kinga ke na zaɓo har gida na aiko miki, saboda haka ki gwada amfanin sa kiga in baiyi ba a biya ki kuɗin ki. Ba tare da ta fahimci me Ƴar Iya ke cewa ba saboda tsananin mamakin taya ma za'a ce yarinyar nan har tasan wani abu aure, balle kuma gyaran shi....toh zai iya yiyuwa tunda Aljanu gareta ammah abun akwai ɗaure head ace yarinyar da yanzu ne ma ta fara fitar da ƙirgen dangi.

“Baki tambaya nawa ake saidawa ba kuma kin riƙe a hannun ki”
“Yi haƙuri duk farin ciki ya mantar da ni” Ƴar Iya cikin ranta tace “Ke kika sani ai nidai kuɗi kawai nike so” a fili kuma tace “Babu tsada ₦500 ce. Gwalo ido Saratu tayi tace “Ɗaribiyar fa kika ce Ƴar Iya?”
“Eh haka nace in baki siya ne ai sai ki faɗa bana son rainin wayo” ta faɗa a ɗan hasale .
Marairaice fuska Saratu tayi sannan tace
“Kinga kuɗin ne ba'a samu sosai ina ma laifin jaka ɗaya?”
Kallon baki da wayo Ƴar Iya tayi wa Saratu kafin tace
“Bani abu na in Baki siya a haka, ƴar rainin wayo naga idan maganin yayi amfani ko million Kika tambayi Arɗo ba haka ki zai yi ba”
Ɗan tunani kaɗan Saratu tayi ta gyaɗa kanta “Shikenan yanzu yaushe ne ranar biya?”
Ƴar Iya tace “Da an kawo sabon kaya ko gobe ne to zaki bani kuɗi na”
“Shikenan”
Daga haka Ƴar Iya ta miƙe tare da ɗaura daron ta aka ta fice.

Ɓangaren Salamatu ta shige tana roɗa sallama
“Salamu Alekum, ina mutan gidan ne kam?”
Salamatu dake madafa ta kammala kwashe tuwo cikin ƙwarya ta amsa sallamar tana washe baki.
“Wa Alekumussalamu, maraba da Ƴar Iya tamu, yau ke ce a gidan nan”
“Eh nice amma neman halal ya kawoni, kinga miƙo min taburma In Zauna”
Taburmar kaba salamatu ta shimfiɗa wa Ƴar Iya ita ma ta zauna. Hakan ya sa Ƴar Iya sauƙe daron ta tare da zama gefen salamatu.
“To salamatu tallan maganin mata na kawo wanda na gaji sirrin daga wurin Aljanun soyayya, sabila da haka ban san ko zaki saya ba”
“Toh maganin mata kuma Ƴar Iya, meyeh shi?” ta faɗa tana zare idanuwa.
Harara ta wullo mata tana aika mata kallon baki da wayo
“Wallahi sai kin siya salamatu na riga na faɗa miki, sarai kin sani Ni zaki yiwa tsiya?, To bari kiji nimah nan na san kina buƙatar maganin, kaji shegiya burgujejiya kamar shanuwa.” ta ƙarasa tana aika mata kallon raini. Cikin kiɗima Salamatu tace
“Yi haƙuti Ƴar Iya ai ban ce ba zan saya ba, dole na siya kam.”
“Ah to karma ki siya nikam bani da hurobulom ai, kece zaki neme Ni da kaina tunda kishiyar ki ma ta saya, idan Arɗo ya koraki gida nan zaki zo har bukka ta a gidan iya”
“Shikenan dai Ƴar Iya, nawa ce kuɗin?”
“₦500 ce babu yawa!”
“Ɗari biyar!”
“Eh a haka kishiyar ki ma ta siya ai, in baki siya ba ma kece a ruwa, a to”
“Na ma siya ai, bari na ɗauko kuɗin ko cikin na abincin gobe ne”
Murmushi Ƴar Iya tayi kafin tace “To yi sauri ina son shiga cikin garin ne”
Fitowa tayi riƙe da ₦500 sannan ta miƙawa Ƴar Iya, daga nan ta ja daron ta ta fice.

Gida uku ta ƙara shiga ganin sun bata kuɗi a hannu yasa ta dawo gida abun ta tana murna ita ma yanzu zata yi kuɗi daga nan kuma zata koma birni.

★★★★★★★★★★★

*SHAREEF POV*

Bisa grass carpet dake a garden ɗin ya zauna saboda ɓacin rai. Da ya rufe ido babu abunda yake gani sai wannan ƙazamar halittar da ta taɓa hannun sa. Tuno da koɗaɗdiyar fuskar ta mai ibi da a Aljanu yayi, ga kuma wani attachment da tayi kitso tuni zuciyar shi ta fara tashi amai ya taso mishi, da ƙyar Hamma Zaki ya miƙe ya wuce sink ɗin dake cikin garden ɗin, amai yayi sosai kafin ya wanke bakin sa ya fito saboda lokacin sallah yayi. Daga cikin abinda ya tsana yaga mace ta sanya bai wuce attachment ba, ya tsani abun gabaɗaya ma shi ƙyama abun ke bashi.

A daddafe ya miƙe ya ƙarasa ciki, part ɗin Nenne ya wuce ba tare da kowa ya san yana can ɗin ba saboda duk suna can part ɗin Mom ana ajajjaɓin ko ina Hamma Zakin ya shiga. Da ƙyar yayi sallar a zaune ma saboda yadda kanshi ke ƙara juyawa.

Yana idarwa ya samu gado ya kwanta tare da lumshe idanuwan shi. Yanayin gabaɗaya is not stable for him. He just wanna forget that devil creature and yayi alƙawarin wulaƙanta ta idan ya warware daga takaicin da ta ƙunzuga mishi a gaban ƙannen shi.

(Bata da ma hankali, bata san waye Hamma Zaki ba, mutumin da kyawawan mata waɗanda ba na ƙasar ba wasu ma ƴaƴan sarakuna suke nuna zalamar su kan shi baya damuwa da su, ko kallon arziƙi baya bari su amsa daga wurin shi. Ballantana ita...toh ai ko Sarah da take baindiya bai bawa fuska bare kuma nunar rana. Afwan Aunty pretty gaskiya mike faɗa miki)

Allah sarki Mom da ƙyar aka lallashe ta ta haƙura ta zauna. Gaba ɗaya hankalin ta duk ya fice daga jikin ta jin ance ya dawo ammah kuma gashi su sun rasa shi, tsoron ta ma kada ace ya illata kansa.

Hajiya Granny ma sai Nenne ke aikin rarrashin ta saboda kuka take bilhaƙƙi.
“Shikenan uban me rai suka yiwa ɗan jikan nawa, yo Ni dama can Shagalin bai kwanta a raina ba gashi wata tsinanniyar ta wargaza wa jika na farin ciki. Wallahi ko ɗiyar waye sai muyi Shari'a da ubanta akan jika na”
Cikin kwantar da kai Nenne tace “Kiyi haƙuri Granny, Ina da tabbacin duk inda Shareef yake yana cikin aminci, kin san Allah bazai cutar da wanda baya cutar kowa ba saboda haka kiyi haƙuri nasan zai dawo”
Cikin shessheƙan kuka Granny tace
“Toh Allah yasa”

A nan part ɗin Mom dukkan su suka yi sallar maghrib daga iyaye mata zuwa ƴaƴayen, iyaye mazan kuma sun fice don neman mafita.

Wani matsiyacin bacci ne ya ɗauke shi a kan gadon cikin wannan yanayi. Ƙiran sallar Ishã ya sa ya farka, miƙa yayi ɗauke da addu'ar bacci a bakin sa. Ganin duhu ya tabbatar masa da Ishã tayi. Tuna cewa babu wanda yasan yana nan yasa ya yi yunƙurin miƙewa don yasan iyayen shi na cikin tashin hankali.

Miƙewa yayi ya fara takawa a hankali, da ya fito parlourn yaga babu kowa ciki ya tabbatar ma kanshi suna can ana neman shi, da sauri ya fice daga part ɗin Nenne zuwa part ɗin Mom.

Kamar ance su juyo dukan su duka waiwayo ai kuwa ganin shi ɗin ke shigowa ya sa duk suka miƙe tare da nufar sa. Kukan Mom keyi tace “Son where have u been?, Duk nan ka sa mun shiga tashin hankali”
Murmushin yaƙe yayi yace
“Calm down everyone Ina can garden ne” daga haka kowa ya koma tare da miƙewa da niyyar yin sallar Ishã in sunyi sai suyi dinner daga nan kowa ya wuce part ɗin su.
Mom kuwa sai da ta ƙira su Daddy ta sanar da su cewa an samu son ɗin nasu tukun tayi sallah.

Bayan sunyi sallah duka suka hallara a dining area, a nutse aka fara ci yayin da baka jin sautin komai sai ƙarar cokala. Ana gama dinner kowa ya watse zuwa nashi ɓangaren.

Hajiya Sarah na gama cin abincin ta ta wuce bedroom nata tare da ɗauko wayar ta. Instagram ta fara hawa tare da posting pictures ɗin da suka yi ita da sauran family wurin taron, few seconds aka fara liking, COMMENTS kuwa ba'a magana. Wasu na tambayar mijin ta ne ko dai?. Wasu kuma har sun ajiye zancen mijin ta ne, hala shi yasa ma baya kula kowacce mace tunda ya samu wannan indian girl ɗin.

Cikin daren kuwa babu abinda ya kai pictures masu trending a Media, Instagram, Facebook, Twitter, YouTube, duk ta ko'ina zancen ake. Wasu na can suna publishing sati faɗin su kan Sarah da kuma Hamma Zaki, yayin da wasu ke ƙara santin haɗa jini da wannan kyawawan family masu nagarta.

Around 10:00pm wayar Sarah tayi ringing, picking tayi tana murmurshi tare da kara wayar a kunnen ta.
“Hello” aka faɗa daga ɗaya ɓangaren
“Hi” ta faɗa cikin sanyi murya.
“Princess how're u doing?, Kin koma gida lafiya?”
“Alhamdulillah”
“Masha Allah, kiyi saving digits na, we'll talk tomorrow”
“Ok bye”
Murmushi Mai sauti yayi sannan yace “Ok good night and sweet dreams”
Daga haka suka katse kiran.
Chapter 23 · 0% Book details