Sashe 22
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai tsaye gidan Arɗo ta wuce, daga baƙin ƙofa Babu wanda ya kulata haka itama bata kula kowa ba. Tana shiga ta wuce ɓangaren Saratu amaryar Arɗo tare da janyo turmi. Saratu da ke ɓangaren madafan ta jiyo alamun ana taɓa turmi. Daga wurin da take ta ƙwala ihu “Waye a nan?”
Ƴar Iya ta amsa da “Ubanki ne!, Daka zanyi”. Saratu na jin Muryar Ƴar Iya ta lallaɓa ta wuce can ɓangaren Innani ba tare da ta kuma cewa komai ba.
Tass ta daga ciyawar nan har ta zama gari, daga nan ta juye ta zuba kashin shanun.....shima dai kamar ciyawa sai da ya koma gari, haka ta zuba kashin awakin nan da nan shima ya zama gari.
Kai ta ɗan jijjiga alamar ne zata yi next, can kuwa tayi murmushi na samo solution. Haɗe abubuwan da ta daka tayi cikin turmin tare da gauraya. Cikin ikon Allah ta kammala nan kuwa dakan nan ya bada colour mai kyau kamar dai ba kashi ne da ciyawa ba.
Kaɗan ta lakuto a hannun ta tare kaiwa hanci tana shinshina kamar mayya. Zaro ido tayi Jin warin still na nan.
“Kutumelesin uban can” ta faɗa tare da ƙara dandalowa tana ƙara kai hanci
“Aradu warin sa har yanzu na nan, to uban me zan saka ya daina warin”
Lokaci ɗaya ta saki murmushi....
Juye abunda ta daka tayi tare da ficewa daga gidan Arɗo don neman abun da zai kashe warin. Gonar Baba Haro ta wuce tare da. Tsinto ganyen mangwaro, ganyen kashu busassu ta koma gidan Arɗo.
Suma sai da ta daka su sannan ta haɗe su baki ɗaya. Kamar yadda tayi ɗazu Yanzu ma Sai da ta shinshina haɗin nata, jin warin ya ragu sosai yanzu sai ma ƙamshi ƙamshin ganye yake yasa tayi dariya.
Har ta saka hannu Zata kwashe tace “A'ah, akwai ciyawar lemon tsami a bayan ɗakin Arɗo bari na ƙara sai ƙamshin yayi yawa”
Tsam taje tare da ciro ɗanyar lemon grass da ƙamshin ta ke fita lokaci guda.
Da yake a jiƙe take tuni ta fara haɗe garin maganin waje ɗaya, sai da ta tabbatar ya daku da kyau ta janyo ludayi tare da ɓanɓaro haɗin kayan sana'ar ta. Ba tare da tayiwa kowa magana ba ta wuce tana ƴar waƙarta har gidan Iya.
A kan rumfar yayi da kara da aka yi don rufe madafa ta ajiye. Tana ajiyewa ta juyo, bata kai ga fara tafiya ba ta kama baki tare da faɗin:
“Na fan gulmar Iya, tana gani sai ta tambaya, mtss” ta ƙarasa da sakin wani dogon tsaki tare da janyo daron ta ta wuce da shi bukkar ta.
Wani baccin wahala ne yayi gaba da Ƴar Iya ko dan guje-gujen da tayi a lambun Baba Haro, ga yawon neman kayan haɗin ta.
Ba ita ta tashi ba sai da yamma, miƙa tayi tana hamma, ba tare da ta rufe baki ba ta miƙe ta zagaya baya don kama ruwa. Ko tsarki bata samu damar yi ba ta fice da guduuuuuu.
Kasuwa ta shiga yayin da wasu ke miƙa gaisuwar su saboda tsoron kada ta ci zalin kayayyakin su. Ganin mutumin Salisu mai burodi tuni ta saki murmushi. Har da wani sunkunyar da kai kafin ta shige rumfar.
“Ah Salisu kana nan abun ka!”
Murmushin da bai kai zuciya ba yayi yace
“Eh wallahi, aka ce mana kin je birni ke kam, yaushe kika dawo rai”
Ƴar Iya tace
“Ai nayi kwana biyu da dawowa nan ɗin ne ban fiye shigowa ba”
“Ayya sannu da dawowa” ya faɗa tare da miƙa mata burodi biyu cikin leda. Murmushi tayi ta ce
“Nagode Salisu, kamar ka san yunwa ce ta kawo ni”
Mamaki duk ya cika Salisu jin mutuniyar tashi da godiya, abun da tunda suke bai taɓa jin tayi ba. Maganar ta ne ta dawo dashi hankalin sa
“To Salisu na tafi, sai na kewayo”
Ta faɗa tana wucewa
“To toh toh” shima ya faɗa a ɗan firgice.
Tana barin wurin Salisu ta ƙara kutsa kai cikin kasuwar. Can da ta gaji da kewaya wa ta fito tare da komawa gida. Gwaten shinkafa da wake Iya tayi musu, daron da ake saka mata ta janyo ba tare da wanke hannu ba ta fara ci hannu baka hannu ƙwarya kamar wacce bata taɓa ci ba, few minutes ta haɗa cinyewa tare da janyo burodin ta, tas ta cinye tana yin gatsa .
Shaf ta manta fa ashe bata da abun ƙulla kayan neman halal ɗin ta. Ai kuwa a zabure ta miƙe ta fice a guje, tana isa kasuwa ta shiga shagon Baban Balki. Ganin yana salla kuma ga ledodi nan a baje fara da baƙa kan teburin shagon ai kuwa ta wawusa tare da cikawa bujen ta iska.
Tana komawa gida ta fara ƙulla abun da nimah kaina ban san me take nufi da shi ba. Tana murmurshi har ta kammala ƙullawa. Lokacin har an fara ƙiraye-ƙirayen Ishã saboda haka ta adana abun ta. Daga nan ta fice dandali ba tare da bi takan A'i ba.
Ba ita ta dawo ba sai da taga dare ta ɗan yi nisa, a hanyar ta ta dawowa ta tsinci wuƙa. Kar kuso kuga murna a gun Ƴar Iya kamar wacce ta samu abun arziƙi. Rungume wuƙar tayi a ƙirjin ta sannan tace
“Kai yau dai da shegiyar Sa'a na tashi Aradu, wuƙa sabuwa haka” ta faɗa tana ƙarema wuƙar kallo “Kai daga gani wuƙar nan zata yi kaifi aradu” dariya mai sauti tayi sannan tace “Da gaske mutanen ƙauyen nan so suke na fara samun halaliya ta!!! Toh ai shikenan nikam bani da wata matsala zan yi sana'a da ita” daga haka ta caka wuƙar a kunkumin ta tana tafiya tana ƙwambo irin dai yadda masu yawo da. Wuƙar nan suke yi cike da taƙama.
Cike da farin ciki ta wuce abunta har ta isa gida. Tana shiga ta ƙara jawo daron ta ta buɗe tare da irgawa don kada taje fitar ta Iya ta sace Mata. Tas ta lissafa tare da yankewa kayan sana'ar ta kuɗi. Daga nan ta ɗale gadon ta mai ɗauke da katifar yayi Nan ta faɗa duniyar bacci. Babu jimawa sautin gwartin ta ya karaɗe ɗakin.
(Nace Allah hokku sa'a Ƴar Iya”)
Ba ita ta tashi ba sai wuraren ƙarfe goma na agogo. Hankali kwance tayi miƙa tare da tashi, yawun baccin da ya bushe a fuskar tata ta ɗan ɗebi guntun ruwan dake ƙasan buta ta goge sannan ta cika bujen ta da iska.
Ba ita ta dawo ba sai wuraren sha ɗaya na rana, ɗumamen da iya tayi taci sannan taci caccanga da miya da iya tayi da rana. Sai da tayi hani'an ta miƙe tayi wanka. Tana fitowa ta ɗauko murtar da Iya ke ajiye Vaseline nata, shafawa tayi abunta duk da cewa wani wurin yayi yawa wani wurin kuwa bai san wani zance ake ciki ba don babu alamar maiƙo a tattare da shi. Tana shafawa ta ɗauko kwandon kwalliyar ta ɗauko ledar powder irin mai ƙasar nan tare da ɗauko madubi tana kallon fuskar ta. Murmushi tayi kafin ta fara shafa powder ɗin tace “Nimah dai kyakkyawa ce, idan nayi ado ai sai naci gasar kyau ta duniya” dariyar da tayi kumatun ta suka lotsa, abun da ban taɓa tunanin akwai shi fuskar ta ba.
Ganin in ta tsaya kallon madubin zata ɓata lokaci yasa ta fara shafa powder ɗin. Yadda take laftawa kai kasan za'a kwashi kyau a wurin. Kamar dai yadda shafin manta ya kasance haka shafin powder ɗin ma, duk tayi damɓare damɓare ga powder Allah ya zuba mata ja kamar masifa. Tuni fuskar nan ta sauya kama daga ta mutum zuwa ta aljana Ƴar Iya.
Murmushi tayi tana ci gaba da kallon madubin ta “Ni ƴar nan da yanzu na zama ƴar gayu fah a birni” tayi murmushi lokacin ɗaya kuma ta kwaɓe fuska “Toh ƴan birnin mugaye ne shi yasa amma ina son sukul ɗin” kamar zata yi kuka ta ƙara cewa “Zan koma watarana lokacin na ɗan ƙara wayo....ko dan sai nayi aure tukun” haka ƴar Iya ta saka madubin a gaba tana ƴan zantukan ta.
Jambaki ta ɗauko tare da murɗa shi har sai da ya kai ƙarshe, ai kuwa a lokacin ya karye. Tsaki tayi tana kwaɓe fuska “Mtss kaima ai sai kayi, don ubanka yau duk sai ka ƙare” ta ƙarasa tare da damƙo jambakin da ya ɓalle daga stand nashi ya faɗo. Ba iya baki bane ya samu janbaki har kusan hancin ta ta sama ta ƙasa kuwa har haɓar ta. Ganin akwai saura yasa ta shafa akan cikakkiyar girar ta tare da shafa wani a saman fatar idon ta.
Har zata miƙe ta ƙara kallon madubin. Murmushi ta sake tace “Aradu zan ci kuɗin samari, dubi kyau kamar Ni nayi kai na!”
Ta faɗa tana miƙewa. Bagco nata ta ƙarasa tare da ɗauko atamfar ta leda mai kalar ja, blue, green, yellow sai orange. Blue gyalen ta ta ɗauko ta yafa tare da janyo daron kayan sana'ar ta.
Har ta ɗaura a kanta ta tuno da wuƙar ta, saurin ɗaga katifar ta tayi ta janyo ta sannan ta soka ta a kunkumin ta. Daga nan ta ɗaura daron kayan sana'a ta fice tana waƙar ta
_kai ku kama sana'a mata_
_kai ku kama sana'a mata_
_macen da bata sana'a aura ce_
Haka tayi ta waƙen ta wasun dai-dai wasun kuwa ta kwaɓa abinda taga dama. Gidan Arɗo ta fara shiga.
“Salamu Alekum, gafaran ku dai iyayen ƙauye, gafaran ku dai matan sarki, ga baƙuwa mai neman halaliyar ta nan”
Ta ƙarasa tare da shigewa cikin gidan.
Ƙofar Saratu ta shiga tana tafka sallama kamar wacce ta kawo abun arziƙi. Daga ɗaka Saratu ta fito jin Muryar Ƴar Iya tana amsa mata sallamar.
“Wa Alekumussalamu, maraba da Ƴar Iya shugabar kowa cikin ƙauyen Gallara, maraba da Ƴar Iya tamu mai hannun ɓarna”
Jin kirarin da Saratu ke zabga mata yasa tayi murmushi tare da ƙara sawa wajen ta. Sauƙe daron tayi “Wayyoh”
Saratu tace “Sannu da zuwa ga taburma nan” ta faɗa tana nuna mata taburmar roba da ta ɗauko daga ɗakin ta.
Ƴar Iya ta amsa da “Ubanki ne!, Daka zanyi”. Saratu na jin Muryar Ƴar Iya ta lallaɓa ta wuce can ɓangaren Innani ba tare da ta kuma cewa komai ba.
Tass ta daga ciyawar nan har ta zama gari, daga nan ta juye ta zuba kashin shanun.....shima dai kamar ciyawa sai da ya koma gari, haka ta zuba kashin awakin nan da nan shima ya zama gari.
Kai ta ɗan jijjiga alamar ne zata yi next, can kuwa tayi murmushi na samo solution. Haɗe abubuwan da ta daka tayi cikin turmin tare da gauraya. Cikin ikon Allah ta kammala nan kuwa dakan nan ya bada colour mai kyau kamar dai ba kashi ne da ciyawa ba.
Kaɗan ta lakuto a hannun ta tare kaiwa hanci tana shinshina kamar mayya. Zaro ido tayi Jin warin still na nan.
“Kutumelesin uban can” ta faɗa tare da ƙara dandalowa tana ƙara kai hanci
“Aradu warin sa har yanzu na nan, to uban me zan saka ya daina warin”
Lokaci ɗaya ta saki murmushi....
Juye abunda ta daka tayi tare da ficewa daga gidan Arɗo don neman abun da zai kashe warin. Gonar Baba Haro ta wuce tare da. Tsinto ganyen mangwaro, ganyen kashu busassu ta koma gidan Arɗo.
Suma sai da ta daka su sannan ta haɗe su baki ɗaya. Kamar yadda tayi ɗazu Yanzu ma Sai da ta shinshina haɗin nata, jin warin ya ragu sosai yanzu sai ma ƙamshi ƙamshin ganye yake yasa tayi dariya.
Har ta saka hannu Zata kwashe tace “A'ah, akwai ciyawar lemon tsami a bayan ɗakin Arɗo bari na ƙara sai ƙamshin yayi yawa”
Tsam taje tare da ciro ɗanyar lemon grass da ƙamshin ta ke fita lokaci guda.
Da yake a jiƙe take tuni ta fara haɗe garin maganin waje ɗaya, sai da ta tabbatar ya daku da kyau ta janyo ludayi tare da ɓanɓaro haɗin kayan sana'ar ta. Ba tare da tayiwa kowa magana ba ta wuce tana ƴar waƙarta har gidan Iya.
A kan rumfar yayi da kara da aka yi don rufe madafa ta ajiye. Tana ajiyewa ta juyo, bata kai ga fara tafiya ba ta kama baki tare da faɗin:
“Na fan gulmar Iya, tana gani sai ta tambaya, mtss” ta ƙarasa da sakin wani dogon tsaki tare da janyo daron ta ta wuce da shi bukkar ta.
Wani baccin wahala ne yayi gaba da Ƴar Iya ko dan guje-gujen da tayi a lambun Baba Haro, ga yawon neman kayan haɗin ta.
Ba ita ta tashi ba sai da yamma, miƙa tayi tana hamma, ba tare da ta rufe baki ba ta miƙe ta zagaya baya don kama ruwa. Ko tsarki bata samu damar yi ba ta fice da guduuuuuu.
Kasuwa ta shiga yayin da wasu ke miƙa gaisuwar su saboda tsoron kada ta ci zalin kayayyakin su. Ganin mutumin Salisu mai burodi tuni ta saki murmushi. Har da wani sunkunyar da kai kafin ta shige rumfar.
“Ah Salisu kana nan abun ka!”
Murmushin da bai kai zuciya ba yayi yace
“Eh wallahi, aka ce mana kin je birni ke kam, yaushe kika dawo rai”
Ƴar Iya tace
“Ai nayi kwana biyu da dawowa nan ɗin ne ban fiye shigowa ba”
“Ayya sannu da dawowa” ya faɗa tare da miƙa mata burodi biyu cikin leda. Murmushi tayi ta ce
“Nagode Salisu, kamar ka san yunwa ce ta kawo ni”
Mamaki duk ya cika Salisu jin mutuniyar tashi da godiya, abun da tunda suke bai taɓa jin tayi ba. Maganar ta ne ta dawo dashi hankalin sa
“To Salisu na tafi, sai na kewayo”
Ta faɗa tana wucewa
“To toh toh” shima ya faɗa a ɗan firgice.
Tana barin wurin Salisu ta ƙara kutsa kai cikin kasuwar. Can da ta gaji da kewaya wa ta fito tare da komawa gida. Gwaten shinkafa da wake Iya tayi musu, daron da ake saka mata ta janyo ba tare da wanke hannu ba ta fara ci hannu baka hannu ƙwarya kamar wacce bata taɓa ci ba, few minutes ta haɗa cinyewa tare da janyo burodin ta, tas ta cinye tana yin gatsa .
Shaf ta manta fa ashe bata da abun ƙulla kayan neman halal ɗin ta. Ai kuwa a zabure ta miƙe ta fice a guje, tana isa kasuwa ta shiga shagon Baban Balki. Ganin yana salla kuma ga ledodi nan a baje fara da baƙa kan teburin shagon ai kuwa ta wawusa tare da cikawa bujen ta iska.
Tana komawa gida ta fara ƙulla abun da nimah kaina ban san me take nufi da shi ba. Tana murmurshi har ta kammala ƙullawa. Lokacin har an fara ƙiraye-ƙirayen Ishã saboda haka ta adana abun ta. Daga nan ta fice dandali ba tare da bi takan A'i ba.
Ba ita ta dawo ba sai da taga dare ta ɗan yi nisa, a hanyar ta ta dawowa ta tsinci wuƙa. Kar kuso kuga murna a gun Ƴar Iya kamar wacce ta samu abun arziƙi. Rungume wuƙar tayi a ƙirjin ta sannan tace
“Kai yau dai da shegiyar Sa'a na tashi Aradu, wuƙa sabuwa haka” ta faɗa tana ƙarema wuƙar kallo “Kai daga gani wuƙar nan zata yi kaifi aradu” dariya mai sauti tayi sannan tace “Da gaske mutanen ƙauyen nan so suke na fara samun halaliya ta!!! Toh ai shikenan nikam bani da wata matsala zan yi sana'a da ita” daga haka ta caka wuƙar a kunkumin ta tana tafiya tana ƙwambo irin dai yadda masu yawo da. Wuƙar nan suke yi cike da taƙama.
Cike da farin ciki ta wuce abunta har ta isa gida. Tana shiga ta ƙara jawo daron ta ta buɗe tare da irgawa don kada taje fitar ta Iya ta sace Mata. Tas ta lissafa tare da yankewa kayan sana'ar ta kuɗi. Daga nan ta ɗale gadon ta mai ɗauke da katifar yayi Nan ta faɗa duniyar bacci. Babu jimawa sautin gwartin ta ya karaɗe ɗakin.
(Nace Allah hokku sa'a Ƴar Iya”)
Ba ita ta tashi ba sai wuraren ƙarfe goma na agogo. Hankali kwance tayi miƙa tare da tashi, yawun baccin da ya bushe a fuskar tata ta ɗan ɗebi guntun ruwan dake ƙasan buta ta goge sannan ta cika bujen ta da iska.
Ba ita ta dawo ba sai wuraren sha ɗaya na rana, ɗumamen da iya tayi taci sannan taci caccanga da miya da iya tayi da rana. Sai da tayi hani'an ta miƙe tayi wanka. Tana fitowa ta ɗauko murtar da Iya ke ajiye Vaseline nata, shafawa tayi abunta duk da cewa wani wurin yayi yawa wani wurin kuwa bai san wani zance ake ciki ba don babu alamar maiƙo a tattare da shi. Tana shafawa ta ɗauko kwandon kwalliyar ta ɗauko ledar powder irin mai ƙasar nan tare da ɗauko madubi tana kallon fuskar ta. Murmushi tayi kafin ta fara shafa powder ɗin tace “Nimah dai kyakkyawa ce, idan nayi ado ai sai naci gasar kyau ta duniya” dariyar da tayi kumatun ta suka lotsa, abun da ban taɓa tunanin akwai shi fuskar ta ba.
Ganin in ta tsaya kallon madubin zata ɓata lokaci yasa ta fara shafa powder ɗin. Yadda take laftawa kai kasan za'a kwashi kyau a wurin. Kamar dai yadda shafin manta ya kasance haka shafin powder ɗin ma, duk tayi damɓare damɓare ga powder Allah ya zuba mata ja kamar masifa. Tuni fuskar nan ta sauya kama daga ta mutum zuwa ta aljana Ƴar Iya.
Murmushi tayi tana ci gaba da kallon madubin ta “Ni ƴar nan da yanzu na zama ƴar gayu fah a birni” tayi murmushi lokacin ɗaya kuma ta kwaɓe fuska “Toh ƴan birnin mugaye ne shi yasa amma ina son sukul ɗin” kamar zata yi kuka ta ƙara cewa “Zan koma watarana lokacin na ɗan ƙara wayo....ko dan sai nayi aure tukun” haka ƴar Iya ta saka madubin a gaba tana ƴan zantukan ta.
Jambaki ta ɗauko tare da murɗa shi har sai da ya kai ƙarshe, ai kuwa a lokacin ya karye. Tsaki tayi tana kwaɓe fuska “Mtss kaima ai sai kayi, don ubanka yau duk sai ka ƙare” ta ƙarasa tare da damƙo jambakin da ya ɓalle daga stand nashi ya faɗo. Ba iya baki bane ya samu janbaki har kusan hancin ta ta sama ta ƙasa kuwa har haɓar ta. Ganin akwai saura yasa ta shafa akan cikakkiyar girar ta tare da shafa wani a saman fatar idon ta.
Har zata miƙe ta ƙara kallon madubin. Murmushi ta sake tace “Aradu zan ci kuɗin samari, dubi kyau kamar Ni nayi kai na!”
Ta faɗa tana miƙewa. Bagco nata ta ƙarasa tare da ɗauko atamfar ta leda mai kalar ja, blue, green, yellow sai orange. Blue gyalen ta ta ɗauko ta yafa tare da janyo daron kayan sana'ar ta.
Har ta ɗaura a kanta ta tuno da wuƙar ta, saurin ɗaga katifar ta tayi ta janyo ta sannan ta soka ta a kunkumin ta. Daga nan ta ɗaura daron kayan sana'a ta fice tana waƙar ta
_kai ku kama sana'a mata_
_kai ku kama sana'a mata_
_macen da bata sana'a aura ce_
Haka tayi ta waƙen ta wasun dai-dai wasun kuwa ta kwaɓa abinda taga dama. Gidan Arɗo ta fara shiga.
“Salamu Alekum, gafaran ku dai iyayen ƙauye, gafaran ku dai matan sarki, ga baƙuwa mai neman halaliyar ta nan”
Ta ƙarasa tare da shigewa cikin gidan.
Ƙofar Saratu ta shiga tana tafka sallama kamar wacce ta kawo abun arziƙi. Daga ɗaka Saratu ta fito jin Muryar Ƴar Iya tana amsa mata sallamar.
“Wa Alekumussalamu, maraba da Ƴar Iya shugabar kowa cikin ƙauyen Gallara, maraba da Ƴar Iya tamu mai hannun ɓarna”
Jin kirarin da Saratu ke zabga mata yasa tayi murmushi tare da ƙara sawa wajen ta. Sauƙe daron tayi “Wayyoh”
Saratu tace “Sannu da zuwa ga taburma nan” ta faɗa tana nuna mata taburmar roba da ta ɗauko daga ɗakin ta.