Sashe 30
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Can Ƴar Iya tayi murmushi tace
“Ba kowa ne wanda na fitar a matsayin miji na ba sai kai Arɗo, kai ne zan aura”
Ta faɗa tana pointing nashi da yatsar ta.
(Toh fah, kunji pretty dai ta samu Hamma Zaki na zai aure ta.! I'm jelous fah☹️😥. Su Ƴar Iya kuma ta yadda aka ɓullo kenan! Toh zadai.muji yadda zata kaya!)
COMMENT, LIKE and SHARE FISABILILLAHI!
Mu haɗu gobe don jin yadda zata kaya, comments ɗinku kawai nake buƙata don shine ƙwarin guiwa ta.
[6/22, 12:47 PM] Diamond Bhatool💎🩷✍️:
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
Eid Mubarak to you all!
Barkan ku da sallah, muna roƙon Allah ya maimaita mana Amin.
Gaisuwa gareku Ƴar Iya READERs
Faty Sharif~
Ameeran Mama~
Oum Basmat~
Ummi Hafsat~
~And the rest.....Allah ya bar ƙauna.
SHAFI NA “““49&50”””
Arɗo da ya rasa tunaninshi na wucin gadi baki kawai ya sake yana ganin ikon Allah yayin da sauran matasa suka shiga wani irin yanayi mai kama da tsoro, tsoron su Allah tsoron su kada iskanci irin na Ƴar Iya ya ƙaru sakamakon auren arɗon gari.
Bayan wasu mintuna ta ƙara murmushi tare da kallon Arɗon wanda har lokacin bai gama dawowa daidai ba tace.
“Arɗo baka ce komai ba har yanzu”
Cikin wani irin yanayi arɗo yace
“Haba Ƴar Iya ai nayi miki tsufa, ki dube Ni kice ni Zaki aura, Ina laifin Matashi mai jini a jika?”
Haɗe rai tayi tace
“Na gama magana Arɗo, Ni kai ɗin dai nike so”
Irin yadda tayi da fuskar tata yasa Arɗo tsorata cikin karyayyiyar Muryar sa yace
“Shikenan Ƴar Iya babu komai Allah ya kai mu lokacin”
Sai a lokacin Ƴar Iya ta saki fuska tare da faɗin
“Yauwa Arɗo sai a fara shiri, wani satin ne bikin”
Daga haka taro ya baje, kowa mamaki kawai yake wai Arɗo zai auri Ƴar Iya. Abun ka da ƙaramin gari tuni zancen ya bazu, babu shiri Inna Zaliha ta ƙudurta ziyartar Bulebule washegari.
Gidan Arɗo ma an rasa zaman lafiya don kuwa Saratu ihu tayi ta kurmawa jin batun auren Arɗo da Ƴar Iya. Daren ranar dai babu bacci don kuwa Innani ma abun bai mata daɗi ba sai dai babu yadda suka iya dole su bi umarnin Sarauniya Ƴar Iya.
Saratu kuwa mancewa da waye Ƴar Iya tayi, washegari sassafe tayi niyyar wucew kahin ta kwaso Ƴan daba azo aci uban Ƴar Iya.
(😂😂😂, Zamu ga yadda za'a yi dai. Su Ƴar Iya masu bikin manya, an zaɓi miji kuma an saka rana. Hooohohooo).
Inna Zaliha da safe ta wuce wurin Bulebule. Taso a dakatar da auren a cewar ta mahaukaciyar nan bata dace da auren Arɗo ba sai dai Bulebule ya tabbatar mata da cewa auren nan dole za'a yi shi sai dai ba zai yi ƙargo ba. Wannan yasa ta ɗan samu salama cikin ranta ai ko ba komai zata fito daga gidan. Bulebule ya tambaye ta yanzu me take so ayi. Nan ta wangale baki tace tana so Ƴar Iya tayi nesa da gida.
Babu ɓata lokaci Bulebule ya haɗa mata magungunan da yadda zata yi amfani da shi daga nan ta baro wurin zuwa gida.
★★★★★★★★★
*ALEE POV*
Soyayyar Hamma Zaki da kuma Pretty ta kankama don kuwa yanzu babu laifi shima yana jin wani abu game da ita, shi kan shi yanzu ya ƙosa suyi auren nan.
Mom da kuma sauran Familyn Alhaji Naira sun dukufa wurin yiwa Hamma Zakin addu'a don sun tabbatar ba haka kawai future wife din shi ta barshi ba musamman yadda suka san ɗabi'un shi na rashin son mata, matan ma marasa kamun kai sai gashi rana tsaka yace sai ita.
Burin su Allah ya maida mummunan nufin Pretty kanta saboda Hamma Zaki bai cutar da kowa suma basu fatan Ubangiji ya bawa wani izinin cutar da shi.
Ana saura two week bikin Hamma Zaki da kanshi ya wuce Canada ya haɗo lefen gimbiyar shi Pretty. A cikin satin su Nenne suka kai gidan su amarya. Tuni lefen ya karaɗe duniyar sada zumunta don irin yadda ya kashe kuɗi wurin haɗa shi.
*ƳAR IYA POV*
Bayan ta koma gida wurin Iya bata yi ƙoƙarin ɓoye mata ba, tas ta kwashe batun auren ta sanar da ita. Iya tayi farin ciki sosai ko ba komai ƴar ta zata huta tunda a gidan arɗo zata yi auren. Nan fa Iya ma aka fara shirye-shiryen biki, a cewar ta zata yiwa shalelen ta bikin Ƴar gata, irin wadda ba'a taɓa yiwa wata ɗiya Mace ba a cikin garin Gallara da kewaye ba.
Ɓangaren Saratu kamar yadda ta ƙudurta sassafe ta fice daga fada, babu ɓsta lokaci ta nufi hanyar kahin. Da isarta kuwa bata ɓata lokaci ba ta nufi wurin su Balamo da su Hodiyo waɗanda suka kasance gagararru cikin kahin. Da ƙyar suka amince da ƙudurin ta daga nan suka ɗaura bayan ta sai Gallara.
Saratu ce ta nuna musu gidan su Ƴar Iya sannan ta tsaya a ƙofar gidan, wani yaro da yazo wucewa ta ƙira akan ya ƙira mata Ƴar Iya amma kul yace inji ta ne, yace ƙawarta ke neman ta.
Cikin gidan yaron ya rantaɓa sallama tare da isar da aikan matar sarki, daga nan yace da su “Tana zuwa” ya wuce abunsa.
Saratu na cije baki tace “Don Allah in ta fito ku nakasa ta, ku daki banza ku daki wofi... Ta rasa ubanwa zata aura sai miji na, yar bura......”
Bata kai ga ƙarasawa ba taci karo da Ƴar Iya na fitowa, alama tayi wa su Balamo, ai kuwa tana ida fitowa suka fara ɗaga bulalun da sunan bugunta. A nan kuwa suka ga burauba don dukan Kawo wuƙa tayi musu da ƙyar suka samu hanyar fecewa. Kan Saratu tayi ta bugi banza daga nan ta barta ƙofar gidan. Da rarrafe Saratu ta koma gida ta yi jinyar kanta.
Ranar Laraba aka kawo lefen Ƴar Iya, babu laifi kaya sunyi a matsayin ta na sarauniya to be. Washegari aka saka Ƴar Iya a lalle.
Ranar juma'a da misalin karfe biyu na rana aka ɗaura Auren A'isha Umar Gallara da kuma angon ta Alhaji Arɗo Usmanu Jauro. Ɗaurin auren da ya samu halartar mutane masu ɗan karen yawa.
Cikin gidan Iya kuwa cike yake maƙil da jama'a, ƴan uwa da abokan arziƙi kowa sAi shige da fice yake. Shinkafa kuwa an daga sama da kwano ashirin don kuwa zuwa ake ana tafiya.
Wasu daga cikin dangin amarya ne suka ce su zasu yi mata rakiya, ai kuwa babu tsammani suka ji tace
“Ni zan kai kaina ban yadda wata tabini gida na ba”
Miƙit suka yi saboda sun san halin ko zancen basu ƙara tadawa ba.
Sai da aka yi sallah Halima tace Ƴar Iya tazo ayi mata ado, babu musu da yake ƙawarta ce ta amince, kwalliya aka sheƙawa Ƴar Iya ta kuzo mugani. Duk da cewa ba wata hamshaƙiya bace tayi mata amma tayi kyau sosai kamar ba ita ba musamman yadda ainihin kyau da Ubangiji yayi mata ya ƙara bayyana.
Ana gama mata kwalliya ta yi sallama da iya wacce ke riskar kuka kamar ba gobe sannan tayi gaba abun ta. Gidan Arɗo wato mijin ta kenan ta nufa kai tsaye. Bata ga kowa ba hakan yasa ta nufi ƙorarta wacce aka yi mata ginin bildin (block) inji su da faɗa.
A hankali ta tura ƙofar tare da shigewa ciki. Baki ta buɗe sosai tana kallon irin kayan arziƙin da Iyarta tayi mata. Bayan ta gama ƙauyancin ta ta haye gadon ta mai rumfa tare da sheƙarewa nan bacci ya ɗauke ta.
(To amarya Ƴar Iya mai abun mamaki Allah ya bada zaman lafiya, ayi amarci lafiya)
*ALEE POV*
Mom CE ta hana yin duk wasu shagulgula a bikin, da ƙyar ta amince mishi da dinner da gidan su amarya suka shirya. Irin rawar kan da Hamma Zaki yake kaɗai zai ƙara tabbatar maka ba lafiya musamman ga wanda ya sanshi before wannan abu ya auko mishi.
Gidan shi da yake Banana Island ya Sha gyara don kuwa dai ƙarfi da yaji Pretty tasa kuka wai ita ba zata zauna a Adamawa ba. Hakan yasa ya zaɓar musu zama a Lagos ɗin tare da ɗaukar transfer zuwa can ɗin. Ba'a daɗe ba kuwa Mom ta gano take_taken shi, babu shiri kuwa ta dakatar dashi kan cewa su zauna a Abuja tunda bata son Adamawa, dalilin mom na hana hakan shine ba zata bar yarinyar nan tayi rayuwa a Lagos ba yanzu ma ya aka kaya balle ta koma Lagos. (Ni kuwa nace ita da take yawo duk yadda taga dama halan ta yi zaman Lagos ɗin ma Mom). Dalili na biyu kuma irin yadda Mom taci alwashin ƙarawa Hamma Zaki aure koda cikin cousin sisters ɗin shi ne.
A lokacin da Hamma Zaki ya sanar da Pretty cewa a Abuja zasu zauna not lagos ji tayi kamar ta shaƙe Mom ɗin nan nashi don taga alama matar babu sauƙi a tattare da ita kuma zata saita ta ne, bari dai shi mai kankat ɗin.
Ranar Laraba a ɓangaren Pretty sunyi kamu, wanda dai ango dama yace shi baya zuwa, ranar Alhamis suka yi Ladies' party. Cikin duk waɗannan events AMARYA tasha kwalliya abunta kamar mai zuwa gasar kyau, sai dai akace mai hali baya fasawa kayan da ta saka sam basu dace ba. Nan social media ta ɗauka wasu na zaginta wasu kuma na zagin mijin, a cewar su ai laifin shi ne da ya barta ta sanya su.
A daren ne kuma taje wurin party da friends nata suka shirya mata wai farewell party. (Ni kaina Bhatool ban so zuwa wurin ba coz Babu alkhairi a ciki). Duk da cewa Mamin ta tayi mata faɗa kan ta guji maza na wani lokacin in ba haka ba duk gyara da aikin da aka yi mata zai ɓaci amma tayi kunnen uwar shegu da ita don kuwa a nan ta kwana tare da su, wannan yayi ya bawa wannan wannan ma yayi ya bawa wannan a cewar su ai farewell ne. Sai da safe ta koma gida ba tare da wani ya fahimta ba ta nemi wuri ta baje sai bacci......
“Ba kowa ne wanda na fitar a matsayin miji na ba sai kai Arɗo, kai ne zan aura”
Ta faɗa tana pointing nashi da yatsar ta.
(Toh fah, kunji pretty dai ta samu Hamma Zaki na zai aure ta.! I'm jelous fah☹️😥. Su Ƴar Iya kuma ta yadda aka ɓullo kenan! Toh zadai.muji yadda zata kaya!)
COMMENT, LIKE and SHARE FISABILILLAHI!
Mu haɗu gobe don jin yadda zata kaya, comments ɗinku kawai nake buƙata don shine ƙwarin guiwa ta.
[6/22, 12:47 PM] Diamond Bhatool💎🩷✍️:
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
Eid Mubarak to you all!
Barkan ku da sallah, muna roƙon Allah ya maimaita mana Amin.
Gaisuwa gareku Ƴar Iya READERs
Faty Sharif~
Ameeran Mama~
Oum Basmat~
Ummi Hafsat~
~And the rest.....Allah ya bar ƙauna.
SHAFI NA “““49&50”””
Arɗo da ya rasa tunaninshi na wucin gadi baki kawai ya sake yana ganin ikon Allah yayin da sauran matasa suka shiga wani irin yanayi mai kama da tsoro, tsoron su Allah tsoron su kada iskanci irin na Ƴar Iya ya ƙaru sakamakon auren arɗon gari.
Bayan wasu mintuna ta ƙara murmushi tare da kallon Arɗon wanda har lokacin bai gama dawowa daidai ba tace.
“Arɗo baka ce komai ba har yanzu”
Cikin wani irin yanayi arɗo yace
“Haba Ƴar Iya ai nayi miki tsufa, ki dube Ni kice ni Zaki aura, Ina laifin Matashi mai jini a jika?”
Haɗe rai tayi tace
“Na gama magana Arɗo, Ni kai ɗin dai nike so”
Irin yadda tayi da fuskar tata yasa Arɗo tsorata cikin karyayyiyar Muryar sa yace
“Shikenan Ƴar Iya babu komai Allah ya kai mu lokacin”
Sai a lokacin Ƴar Iya ta saki fuska tare da faɗin
“Yauwa Arɗo sai a fara shiri, wani satin ne bikin”
Daga haka taro ya baje, kowa mamaki kawai yake wai Arɗo zai auri Ƴar Iya. Abun ka da ƙaramin gari tuni zancen ya bazu, babu shiri Inna Zaliha ta ƙudurta ziyartar Bulebule washegari.
Gidan Arɗo ma an rasa zaman lafiya don kuwa Saratu ihu tayi ta kurmawa jin batun auren Arɗo da Ƴar Iya. Daren ranar dai babu bacci don kuwa Innani ma abun bai mata daɗi ba sai dai babu yadda suka iya dole su bi umarnin Sarauniya Ƴar Iya.
Saratu kuwa mancewa da waye Ƴar Iya tayi, washegari sassafe tayi niyyar wucew kahin ta kwaso Ƴan daba azo aci uban Ƴar Iya.
(😂😂😂, Zamu ga yadda za'a yi dai. Su Ƴar Iya masu bikin manya, an zaɓi miji kuma an saka rana. Hooohohooo).
Inna Zaliha da safe ta wuce wurin Bulebule. Taso a dakatar da auren a cewar ta mahaukaciyar nan bata dace da auren Arɗo ba sai dai Bulebule ya tabbatar mata da cewa auren nan dole za'a yi shi sai dai ba zai yi ƙargo ba. Wannan yasa ta ɗan samu salama cikin ranta ai ko ba komai zata fito daga gidan. Bulebule ya tambaye ta yanzu me take so ayi. Nan ta wangale baki tace tana so Ƴar Iya tayi nesa da gida.
Babu ɓata lokaci Bulebule ya haɗa mata magungunan da yadda zata yi amfani da shi daga nan ta baro wurin zuwa gida.
★★★★★★★★★
*ALEE POV*
Soyayyar Hamma Zaki da kuma Pretty ta kankama don kuwa yanzu babu laifi shima yana jin wani abu game da ita, shi kan shi yanzu ya ƙosa suyi auren nan.
Mom da kuma sauran Familyn Alhaji Naira sun dukufa wurin yiwa Hamma Zakin addu'a don sun tabbatar ba haka kawai future wife din shi ta barshi ba musamman yadda suka san ɗabi'un shi na rashin son mata, matan ma marasa kamun kai sai gashi rana tsaka yace sai ita.
Burin su Allah ya maida mummunan nufin Pretty kanta saboda Hamma Zaki bai cutar da kowa suma basu fatan Ubangiji ya bawa wani izinin cutar da shi.
Ana saura two week bikin Hamma Zaki da kanshi ya wuce Canada ya haɗo lefen gimbiyar shi Pretty. A cikin satin su Nenne suka kai gidan su amarya. Tuni lefen ya karaɗe duniyar sada zumunta don irin yadda ya kashe kuɗi wurin haɗa shi.
*ƳAR IYA POV*
Bayan ta koma gida wurin Iya bata yi ƙoƙarin ɓoye mata ba, tas ta kwashe batun auren ta sanar da ita. Iya tayi farin ciki sosai ko ba komai ƴar ta zata huta tunda a gidan arɗo zata yi auren. Nan fa Iya ma aka fara shirye-shiryen biki, a cewar ta zata yiwa shalelen ta bikin Ƴar gata, irin wadda ba'a taɓa yiwa wata ɗiya Mace ba a cikin garin Gallara da kewaye ba.
Ɓangaren Saratu kamar yadda ta ƙudurta sassafe ta fice daga fada, babu ɓsta lokaci ta nufi hanyar kahin. Da isarta kuwa bata ɓata lokaci ba ta nufi wurin su Balamo da su Hodiyo waɗanda suka kasance gagararru cikin kahin. Da ƙyar suka amince da ƙudurin ta daga nan suka ɗaura bayan ta sai Gallara.
Saratu ce ta nuna musu gidan su Ƴar Iya sannan ta tsaya a ƙofar gidan, wani yaro da yazo wucewa ta ƙira akan ya ƙira mata Ƴar Iya amma kul yace inji ta ne, yace ƙawarta ke neman ta.
Cikin gidan yaron ya rantaɓa sallama tare da isar da aikan matar sarki, daga nan yace da su “Tana zuwa” ya wuce abunsa.
Saratu na cije baki tace “Don Allah in ta fito ku nakasa ta, ku daki banza ku daki wofi... Ta rasa ubanwa zata aura sai miji na, yar bura......”
Bata kai ga ƙarasawa ba taci karo da Ƴar Iya na fitowa, alama tayi wa su Balamo, ai kuwa tana ida fitowa suka fara ɗaga bulalun da sunan bugunta. A nan kuwa suka ga burauba don dukan Kawo wuƙa tayi musu da ƙyar suka samu hanyar fecewa. Kan Saratu tayi ta bugi banza daga nan ta barta ƙofar gidan. Da rarrafe Saratu ta koma gida ta yi jinyar kanta.
Ranar Laraba aka kawo lefen Ƴar Iya, babu laifi kaya sunyi a matsayin ta na sarauniya to be. Washegari aka saka Ƴar Iya a lalle.
Ranar juma'a da misalin karfe biyu na rana aka ɗaura Auren A'isha Umar Gallara da kuma angon ta Alhaji Arɗo Usmanu Jauro. Ɗaurin auren da ya samu halartar mutane masu ɗan karen yawa.
Cikin gidan Iya kuwa cike yake maƙil da jama'a, ƴan uwa da abokan arziƙi kowa sAi shige da fice yake. Shinkafa kuwa an daga sama da kwano ashirin don kuwa zuwa ake ana tafiya.
Wasu daga cikin dangin amarya ne suka ce su zasu yi mata rakiya, ai kuwa babu tsammani suka ji tace
“Ni zan kai kaina ban yadda wata tabini gida na ba”
Miƙit suka yi saboda sun san halin ko zancen basu ƙara tadawa ba.
Sai da aka yi sallah Halima tace Ƴar Iya tazo ayi mata ado, babu musu da yake ƙawarta ce ta amince, kwalliya aka sheƙawa Ƴar Iya ta kuzo mugani. Duk da cewa ba wata hamshaƙiya bace tayi mata amma tayi kyau sosai kamar ba ita ba musamman yadda ainihin kyau da Ubangiji yayi mata ya ƙara bayyana.
Ana gama mata kwalliya ta yi sallama da iya wacce ke riskar kuka kamar ba gobe sannan tayi gaba abun ta. Gidan Arɗo wato mijin ta kenan ta nufa kai tsaye. Bata ga kowa ba hakan yasa ta nufi ƙorarta wacce aka yi mata ginin bildin (block) inji su da faɗa.
A hankali ta tura ƙofar tare da shigewa ciki. Baki ta buɗe sosai tana kallon irin kayan arziƙin da Iyarta tayi mata. Bayan ta gama ƙauyancin ta ta haye gadon ta mai rumfa tare da sheƙarewa nan bacci ya ɗauke ta.
(To amarya Ƴar Iya mai abun mamaki Allah ya bada zaman lafiya, ayi amarci lafiya)
*ALEE POV*
Mom CE ta hana yin duk wasu shagulgula a bikin, da ƙyar ta amince mishi da dinner da gidan su amarya suka shirya. Irin rawar kan da Hamma Zaki yake kaɗai zai ƙara tabbatar maka ba lafiya musamman ga wanda ya sanshi before wannan abu ya auko mishi.
Gidan shi da yake Banana Island ya Sha gyara don kuwa dai ƙarfi da yaji Pretty tasa kuka wai ita ba zata zauna a Adamawa ba. Hakan yasa ya zaɓar musu zama a Lagos ɗin tare da ɗaukar transfer zuwa can ɗin. Ba'a daɗe ba kuwa Mom ta gano take_taken shi, babu shiri kuwa ta dakatar dashi kan cewa su zauna a Abuja tunda bata son Adamawa, dalilin mom na hana hakan shine ba zata bar yarinyar nan tayi rayuwa a Lagos ba yanzu ma ya aka kaya balle ta koma Lagos. (Ni kuwa nace ita da take yawo duk yadda taga dama halan ta yi zaman Lagos ɗin ma Mom). Dalili na biyu kuma irin yadda Mom taci alwashin ƙarawa Hamma Zaki aure koda cikin cousin sisters ɗin shi ne.
A lokacin da Hamma Zaki ya sanar da Pretty cewa a Abuja zasu zauna not lagos ji tayi kamar ta shaƙe Mom ɗin nan nashi don taga alama matar babu sauƙi a tattare da ita kuma zata saita ta ne, bari dai shi mai kankat ɗin.
Ranar Laraba a ɓangaren Pretty sunyi kamu, wanda dai ango dama yace shi baya zuwa, ranar Alhamis suka yi Ladies' party. Cikin duk waɗannan events AMARYA tasha kwalliya abunta kamar mai zuwa gasar kyau, sai dai akace mai hali baya fasawa kayan da ta saka sam basu dace ba. Nan social media ta ɗauka wasu na zaginta wasu kuma na zagin mijin, a cewar su ai laifin shi ne da ya barta ta sanya su.
A daren ne kuma taje wurin party da friends nata suka shirya mata wai farewell party. (Ni kaina Bhatool ban so zuwa wurin ba coz Babu alkhairi a ciki). Duk da cewa Mamin ta tayi mata faɗa kan ta guji maza na wani lokacin in ba haka ba duk gyara da aikin da aka yi mata zai ɓaci amma tayi kunnen uwar shegu da ita don kuwa a nan ta kwana tare da su, wannan yayi ya bawa wannan wannan ma yayi ya bawa wannan a cewar su ai farewell ne. Sai da safe ta koma gida ba tare da wani ya fahimta ba ta nemi wuri ta baje sai bacci......