Sashe 17
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A zaune ta tarar da iya bisa kujerar tsakar gida, da gudu ta faɗa kanta tana sakin kuka.
“Iya ta bakiyi kewa ta ba neh?” ta faɗa bayan ta tsagaita da kukan da take yi.
“Haba shalelen Iya ni ɗin ne kuwa nayi kewar ki, kullum sai nayi hawaye ina tunanin shalele na”
Murmushi tayi tare da sakin Iya
“Iya birni babu daɗi, akwai mugaye a sukul ɗin mu”
Zare ido yayi tayi tace
“Miye sukul kuma shalelen iya?”
Dariya da shewa Iya ta saki lokaci guda.
“Ayyiriri nanaye....lallai Iya na manta ashe fa ke ƴar ƙauye ce” ta dakata tana wani fari da ido kamar wacce ke gaban saurayin ta.
Iya kam dariya tayi tana faɗin
“Yo Ni kam ai nan ne iyaka ta sai ƙauyukan kewaye, ban taɓa zuwa birni ba shiyasa naso ke ki tashi a can kinga wata rana sai ki kai ni”
Ta ƙarasa sounding serious.
Dariya Ƴar Iya tayi tace
“Iya kenan, to Aradu ƴan birnin nan mugaye ne barin ma masu baƙin kayan na, hegu kingan su ƙataye da su ammah sai da na basu kashi”
Ta ƙarasa tare da kaɗa yatsa.
Cike da ƙosawa iya tace
“Yanzu faɗa min suku ne Kika ce ko sumul?”
“Hhhh..... Kiji Iya wai suku😒😂, to ai ba haka ake faɗa ba, in Kika faɗa a gaban ƴan birni to dariya zasu yi miki” ta faɗa tana wani kaɗa kai ita ala dole ƴar birni.
“Toh ai sai ki gyara min yadda nima in na shiga maƙwabta zanyi musu su san Shalele na taje birni”
Murmushi Ƴar Iya tayi tace
“Ai kuwa, to Iya ai sukul ake cewa ba suku ba”
“Ayya sukwal”
“Hahhhh. Iya ba sukwal ba sukul”
“Ai to sukul”
“Yauwa Iya ta yanzu dai-dai kika faɗa”
Dariyar farin ciki iya tayi tace
“Toh shi sukul ɗin me yake nufi?”
Ta tambaya cike da ƙaguwa.
Sai da ta juya kai kafin tace
“Makaranta shine sukul ɗin”
Haka suka yi ta shirmen su yayin da cikin gari ya ɗauka ai Ƴar Iya ta dawo. Wasu na farin ciki musamman A'i wasu kuma har sun fara kuka da kansu.
★★★★★★★★★
*ALEE POV*
Bayan sun isa wurin da suka bar motocin su, kai tsaye suka shige tare da wucewa. Bayan sun isa waɗanda suka samu rauni aka miƙa su asibitin dake can for effective treatment yayin da Hamma Zaki yaƙi tsayawa.
Bai samu kunna wayar shi ba ko da bayan sun dawo, saboda haka ya kunna tare da ƙiran Joseph, cikin mintuna kaɗan Joseph ya ƙaraso yayi driving Hamma Zaki gida.
Tun kafin motar ta gama packing gaba ɗaya mutanen gidan suka iso wurin,p Mom da fuskar ta ke ɗauke da tsantsan damuwa da sauri ta shige gaba ganin Joseph ya buɗe mishi motar, cikin zafin nama taje tayi hugging nashi tana sakin wani irin kuka.
Zuciyar shi ce ta karye ganin yadda Mom ɗin shi ke kuka.
Granny ma ba a bar ta baya ba,
“Ku bani waje nagan shi don Allah, lafiya ƙalau yake ai koh?” ta faɗa tana Matsowa kusa da shi.
Ganin raunin da ya samu yasa jikin kowa yin sanyi. Nan take Mom tace su wuce Hospital, bai iya yi mata musu ba haka suka ɗunguma zuwa Hospital. Bayan an yi treating raunukan likita ya buƙaci su koma don yana buƙatar hutawa.
★★★★★★★★★
Yammacin ranar kuwa Ƴar Iya tayi wanka har da wanke baki da gawayi da kuma alimun, aka saka kaya masu kyau ita ala dole an je birni.
Ko sallama bata yiwa Iya ba ta fito abun ta tana taku tana yauƙi kamar wata kuɓaiwa. Kai tsaye gidan su Aminiyar ta A'i ta wuce, kafin isar ta kuwa duk wurin da ta gifta sai anyi gulmar ta wai Ƴar Iya taje birni baku ga har sauya tafiya tayi Baneh irin ta ƴan birni?.
Sai da suka sha hirar yaushe gamo da kuma labarin bayan rabuwa a nan A'i ke faɗa mata tsiyar da ƴan garin suke mata bayan tafiyar ta.
“Hmm ƙawata dai tunda kika sa ƙafa kika bar Gallara shikenan ƴan gari suka tsaneni,”
“Ban gane ba”
“Ina faɗi miki Aradu har duka na wasu suke yi wai zasu huce tsiyar da muka tsula duka a kaina”
Mamaki ne ya kama Ƴar Iya jin abun da ƴan garin suka yi wa Aminiyar ta kuma ta ɗaukar mata alƙawarin ɗaukar mata fansa.
Daga haka suka fice don yawata gari. Gulma ko ina Ƴar Iya annoba, Ƴar Iya mai hannun ɓarna ta dawo, wasu wurin kuma gulmar su bata wuce yadda Ƴar Iya ta sauya tafiya ba ga kuma kaya masu kyau da suka gani a jikin ta saɓanin da da sai tayi wata da kaya a jikin ta.
(Nace ah toh, don ma makaranta taje da ace wani gidan ƴan gayun taje da tafi haka).
A dai-dai wata corner suka ga wani yaro ɗauke da kaji a hannun shi alamun sayar da su zai yi.
Ƴar Iya kuwa murmushin mugunta tayi sannan ta dakatar da shi.
“Dauda ina ne zaka je haka a yammacin nan da kaji?”
Dauda da duk ya tsorata ya duburburce saboda ya san karon sun da Ƴar Iya mai hannun ɓarna ya fara magana cikin ƙiƙina.
“da...da...dama...innnn...innna ta...ce...ta..ta...ce..na..je ka...ka..kasuwa na..sa..sa..yar da...kajin...sai...na.auno...geron tuwa”.
Murmushi kawai tayi tace shikenan jeka abun ka ammah kace kada a ƙara aiken ka da kaji kaji ko?”
Kai ya gyaɗa daga nan suka bar shi ya wuce.
Nausawa cikin kasuwar suka yi still Ƴar Iya na kwalmaɗewa kamar wata kara tana ƙara gyara tafiya.
Dai-dai wurin Bala Mai kifi suka tsaya ganin lokacin yake soya kifin.
Fari Ƴar Iya tayi da ido sannan ta gaida Bala wanda take zuciyar sa ta fara wani irin bugu.
“Ina wuni mai kifi”
Cikin ƙarfin hali Bala ya amsa yace
“Ina wuni Ƴar Iya ya gida?, Kin dawo ashe”
“Eh wallahi mun dawo jiya da Yamma, akwai kifin ne?”
Ta faɗa tana ƙara leƙa kifin dake zube kan teburin.
Bala ya amsa mata da
“Eh akwai”
Ai da tunda suka zo bata ce uffan ba ta ce
“Mai zafi zaka saka muna”
Da “Toh ” ya amsa sannan ya jawo leda ya cika ta da kifi daga nan ya miƙa musu. Godiya suka yi mishi sannan suka ja ƙafafuwan su sai gidan Iya.
Bayan sallar maghrib A'i ta yi sallah a ɗakin Iya, don ita duk tsiyar ta tana yi ne idan mai tare mata tana nan kuma ba laifi tana bubbuga sallar ta duk da cewa ba yadda ake yi ba abun ku da mutanen ƙauye.
Kai tsaye gidan wata Halima suka shiga. Duk da cewa basu taɓa shiga gidan ba ammah haka Ƴar Iya ta jagoranci A'i zuwan cikin gidan saboda ta jiyo ƙamshin dahuwar da ke tashi ta jikin zana.
Ƴar Iya ce ta fara kwaɗa Salama
“Salamu Alekum, Salamu Alekum ga baƙin maghriba”
Halima da bata san waye ba ta amsa tana gyara murya da alamar a makewayi take.
Shigowa suka yi suka zauna kamar mutanen kirki a kan taburmar da ta shimfiɗa kusa da murhun.
Halima mace ce mai son gayu, fara ce kakkaura kuma ba ƴar cikin Gallara bane, daga Azare aka auro ta. Da yake tayi zama cikin birni kuma irin matan nan ne masu kutsawa cikin manya babu wahala ta san abubuwa da dama. Sana'ar ta a nan Gallara shine sayar da maganin mata iri iri kuma babu laifi ana siya saboda kowa so take ta zama gwana wurin mijin ta. Hakan yasa Halima ta saba da ƴan garin cikin ƙanƙanin lokaci, da wuya kazo gidan ta baka tarar da baƙi ba wasu sun zo ayi musu irin dahuwar nan ne wasu kuma siyan maganin mata suke yi.
Ɗaure da zani a ƙirjin ta ta fito daga makewayi tana kallon su Ƴar Iya da suka make a kan taburma tana aika musu kallon tambaya.
“Sannun ku da zuwa Ƴan mata”
“Yauwah sannu” Ƴar Iya ta amsa tana ƙara kame kanta wuri guda kamar ta ƙwarai.
“Bari na sako kaya sai nazo”
Bayan mintuna 30 sai ga Halima ta fito cikin wata koɗaɗɗiyar atamfa sai dai tas-tas take babu alamun datti. Tayi kwalliyar ta ta kuma shafa janbaki har da eyeshadow. KO ƙifta ido Ƴar Iya bata yi ganin irin adon da matar ta caɓa. Haka nan taji matar ta burge ta kuma tana son su ƙulla zumunci.
“Kuyi haƙuri ƴan mata na ɗan ɓata muku lokaci, wacce ce amaryar a ciki?” ta faɗa tana yin wani murmushi tare da zama kusa da su bisa taburmar.
Kallon mamaki Ƴar Iya ke bin ta da shi jin wai wacece amarya?. A'i da yake an riga an sanya bikin ta bayan tafiyar Ƴar Iya birni saboda dama tun kwanaki aka fara auren sa'annin su.
Sunkuyar da kai ƙasa tayi tace
“Nice, Ina wuni”
Murmushi Halima tayi tace
“Lafiya ƙalau ai na ɗauka wannan ce amaryar”
Ta faɗa tana nuna Ƴar Iya da yatsa.
Kamar ta Allah Ƴar Iya bata ce komai ba sai murmushi kawai take saki nace anya kuwa wannan murmushi babu biyu a ƙasa kuwa?.
Bayan sun gaisa tace
“Bari na sauƙe dahuwar nan don Allah, kema ya kamata ki fara shirin auren nan fa, in kin je gida ki cewa Innar ki ta fara shirya ki kuma ki ce mata ina gyara sosai da kuma bada magungunan mata masu kyau”
Caraf Ƴar Iya tace
“Gyara kuma na me?”
Halima da yake irin matan nan ne marasa kunya kuma babu ruwan su da yaro ko babba tace
“Bari na sauƙe na dawo”
Sauƙe tukunyar tayi tare da ɗaura wata tukunyar da alamar abincin dare zata girka. Wurin su ta dawo ta zauna sannan ta maida kallon ta ga Ƴar Iya.
“Yauwah Ƙawar amarya kike tambaya kan batun gyara koh?” kai Ƴar Iya ta gyaɗa tare da maida hankalin ta ga Halima.
“Toh kafin nan dai ya kamata na san sunan amarya da ƙawar ta ko?”
A'i tace
“Ni suna na A'i wannan kuma Aminiya ta ce Ƴar Iya, halan zaki ji ana labarin ta ko da yake mu ma kan mu bamu san ki ba a ƙauyen duk irin yawon mu”
“Iya ta bakiyi kewa ta ba neh?” ta faɗa bayan ta tsagaita da kukan da take yi.
“Haba shalelen Iya ni ɗin ne kuwa nayi kewar ki, kullum sai nayi hawaye ina tunanin shalele na”
Murmushi tayi tare da sakin Iya
“Iya birni babu daɗi, akwai mugaye a sukul ɗin mu”
Zare ido yayi tayi tace
“Miye sukul kuma shalelen iya?”
Dariya da shewa Iya ta saki lokaci guda.
“Ayyiriri nanaye....lallai Iya na manta ashe fa ke ƴar ƙauye ce” ta dakata tana wani fari da ido kamar wacce ke gaban saurayin ta.
Iya kam dariya tayi tana faɗin
“Yo Ni kam ai nan ne iyaka ta sai ƙauyukan kewaye, ban taɓa zuwa birni ba shiyasa naso ke ki tashi a can kinga wata rana sai ki kai ni”
Ta ƙarasa sounding serious.
Dariya Ƴar Iya tayi tace
“Iya kenan, to Aradu ƴan birnin nan mugaye ne barin ma masu baƙin kayan na, hegu kingan su ƙataye da su ammah sai da na basu kashi”
Ta ƙarasa tare da kaɗa yatsa.
Cike da ƙosawa iya tace
“Yanzu faɗa min suku ne Kika ce ko sumul?”
“Hhhh..... Kiji Iya wai suku😒😂, to ai ba haka ake faɗa ba, in Kika faɗa a gaban ƴan birni to dariya zasu yi miki” ta faɗa tana wani kaɗa kai ita ala dole ƴar birni.
“Toh ai sai ki gyara min yadda nima in na shiga maƙwabta zanyi musu su san Shalele na taje birni”
Murmushi Ƴar Iya tayi tace
“Ai kuwa, to Iya ai sukul ake cewa ba suku ba”
“Ayya sukwal”
“Hahhhh. Iya ba sukwal ba sukul”
“Ai to sukul”
“Yauwa Iya ta yanzu dai-dai kika faɗa”
Dariyar farin ciki iya tayi tace
“Toh shi sukul ɗin me yake nufi?”
Ta tambaya cike da ƙaguwa.
Sai da ta juya kai kafin tace
“Makaranta shine sukul ɗin”
Haka suka yi ta shirmen su yayin da cikin gari ya ɗauka ai Ƴar Iya ta dawo. Wasu na farin ciki musamman A'i wasu kuma har sun fara kuka da kansu.
★★★★★★★★★
*ALEE POV*
Bayan sun isa wurin da suka bar motocin su, kai tsaye suka shige tare da wucewa. Bayan sun isa waɗanda suka samu rauni aka miƙa su asibitin dake can for effective treatment yayin da Hamma Zaki yaƙi tsayawa.
Bai samu kunna wayar shi ba ko da bayan sun dawo, saboda haka ya kunna tare da ƙiran Joseph, cikin mintuna kaɗan Joseph ya ƙaraso yayi driving Hamma Zaki gida.
Tun kafin motar ta gama packing gaba ɗaya mutanen gidan suka iso wurin,p Mom da fuskar ta ke ɗauke da tsantsan damuwa da sauri ta shige gaba ganin Joseph ya buɗe mishi motar, cikin zafin nama taje tayi hugging nashi tana sakin wani irin kuka.
Zuciyar shi ce ta karye ganin yadda Mom ɗin shi ke kuka.
Granny ma ba a bar ta baya ba,
“Ku bani waje nagan shi don Allah, lafiya ƙalau yake ai koh?” ta faɗa tana Matsowa kusa da shi.
Ganin raunin da ya samu yasa jikin kowa yin sanyi. Nan take Mom tace su wuce Hospital, bai iya yi mata musu ba haka suka ɗunguma zuwa Hospital. Bayan an yi treating raunukan likita ya buƙaci su koma don yana buƙatar hutawa.
★★★★★★★★★
Yammacin ranar kuwa Ƴar Iya tayi wanka har da wanke baki da gawayi da kuma alimun, aka saka kaya masu kyau ita ala dole an je birni.
Ko sallama bata yiwa Iya ba ta fito abun ta tana taku tana yauƙi kamar wata kuɓaiwa. Kai tsaye gidan su Aminiyar ta A'i ta wuce, kafin isar ta kuwa duk wurin da ta gifta sai anyi gulmar ta wai Ƴar Iya taje birni baku ga har sauya tafiya tayi Baneh irin ta ƴan birni?.
Sai da suka sha hirar yaushe gamo da kuma labarin bayan rabuwa a nan A'i ke faɗa mata tsiyar da ƴan garin suke mata bayan tafiyar ta.
“Hmm ƙawata dai tunda kika sa ƙafa kika bar Gallara shikenan ƴan gari suka tsaneni,”
“Ban gane ba”
“Ina faɗi miki Aradu har duka na wasu suke yi wai zasu huce tsiyar da muka tsula duka a kaina”
Mamaki ne ya kama Ƴar Iya jin abun da ƴan garin suka yi wa Aminiyar ta kuma ta ɗaukar mata alƙawarin ɗaukar mata fansa.
Daga haka suka fice don yawata gari. Gulma ko ina Ƴar Iya annoba, Ƴar Iya mai hannun ɓarna ta dawo, wasu wurin kuma gulmar su bata wuce yadda Ƴar Iya ta sauya tafiya ba ga kuma kaya masu kyau da suka gani a jikin ta saɓanin da da sai tayi wata da kaya a jikin ta.
(Nace ah toh, don ma makaranta taje da ace wani gidan ƴan gayun taje da tafi haka).
A dai-dai wata corner suka ga wani yaro ɗauke da kaji a hannun shi alamun sayar da su zai yi.
Ƴar Iya kuwa murmushin mugunta tayi sannan ta dakatar da shi.
“Dauda ina ne zaka je haka a yammacin nan da kaji?”
Dauda da duk ya tsorata ya duburburce saboda ya san karon sun da Ƴar Iya mai hannun ɓarna ya fara magana cikin ƙiƙina.
“da...da...dama...innnn...innna ta...ce...ta..ta...ce..na..je ka...ka..kasuwa na..sa..sa..yar da...kajin...sai...na.auno...geron tuwa”.
Murmushi kawai tayi tace shikenan jeka abun ka ammah kace kada a ƙara aiken ka da kaji kaji ko?”
Kai ya gyaɗa daga nan suka bar shi ya wuce.
Nausawa cikin kasuwar suka yi still Ƴar Iya na kwalmaɗewa kamar wata kara tana ƙara gyara tafiya.
Dai-dai wurin Bala Mai kifi suka tsaya ganin lokacin yake soya kifin.
Fari Ƴar Iya tayi da ido sannan ta gaida Bala wanda take zuciyar sa ta fara wani irin bugu.
“Ina wuni mai kifi”
Cikin ƙarfin hali Bala ya amsa yace
“Ina wuni Ƴar Iya ya gida?, Kin dawo ashe”
“Eh wallahi mun dawo jiya da Yamma, akwai kifin ne?”
Ta faɗa tana ƙara leƙa kifin dake zube kan teburin.
Bala ya amsa mata da
“Eh akwai”
Ai da tunda suka zo bata ce uffan ba ta ce
“Mai zafi zaka saka muna”
Da “Toh ” ya amsa sannan ya jawo leda ya cika ta da kifi daga nan ya miƙa musu. Godiya suka yi mishi sannan suka ja ƙafafuwan su sai gidan Iya.
Bayan sallar maghrib A'i ta yi sallah a ɗakin Iya, don ita duk tsiyar ta tana yi ne idan mai tare mata tana nan kuma ba laifi tana bubbuga sallar ta duk da cewa ba yadda ake yi ba abun ku da mutanen ƙauye.
Kai tsaye gidan wata Halima suka shiga. Duk da cewa basu taɓa shiga gidan ba ammah haka Ƴar Iya ta jagoranci A'i zuwan cikin gidan saboda ta jiyo ƙamshin dahuwar da ke tashi ta jikin zana.
Ƴar Iya ce ta fara kwaɗa Salama
“Salamu Alekum, Salamu Alekum ga baƙin maghriba”
Halima da bata san waye ba ta amsa tana gyara murya da alamar a makewayi take.
Shigowa suka yi suka zauna kamar mutanen kirki a kan taburmar da ta shimfiɗa kusa da murhun.
Halima mace ce mai son gayu, fara ce kakkaura kuma ba ƴar cikin Gallara bane, daga Azare aka auro ta. Da yake tayi zama cikin birni kuma irin matan nan ne masu kutsawa cikin manya babu wahala ta san abubuwa da dama. Sana'ar ta a nan Gallara shine sayar da maganin mata iri iri kuma babu laifi ana siya saboda kowa so take ta zama gwana wurin mijin ta. Hakan yasa Halima ta saba da ƴan garin cikin ƙanƙanin lokaci, da wuya kazo gidan ta baka tarar da baƙi ba wasu sun zo ayi musu irin dahuwar nan ne wasu kuma siyan maganin mata suke yi.
Ɗaure da zani a ƙirjin ta ta fito daga makewayi tana kallon su Ƴar Iya da suka make a kan taburma tana aika musu kallon tambaya.
“Sannun ku da zuwa Ƴan mata”
“Yauwah sannu” Ƴar Iya ta amsa tana ƙara kame kanta wuri guda kamar ta ƙwarai.
“Bari na sako kaya sai nazo”
Bayan mintuna 30 sai ga Halima ta fito cikin wata koɗaɗɗiyar atamfa sai dai tas-tas take babu alamun datti. Tayi kwalliyar ta ta kuma shafa janbaki har da eyeshadow. KO ƙifta ido Ƴar Iya bata yi ganin irin adon da matar ta caɓa. Haka nan taji matar ta burge ta kuma tana son su ƙulla zumunci.
“Kuyi haƙuri ƴan mata na ɗan ɓata muku lokaci, wacce ce amaryar a ciki?” ta faɗa tana yin wani murmushi tare da zama kusa da su bisa taburmar.
Kallon mamaki Ƴar Iya ke bin ta da shi jin wai wacece amarya?. A'i da yake an riga an sanya bikin ta bayan tafiyar Ƴar Iya birni saboda dama tun kwanaki aka fara auren sa'annin su.
Sunkuyar da kai ƙasa tayi tace
“Nice, Ina wuni”
Murmushi Halima tayi tace
“Lafiya ƙalau ai na ɗauka wannan ce amaryar”
Ta faɗa tana nuna Ƴar Iya da yatsa.
Kamar ta Allah Ƴar Iya bata ce komai ba sai murmushi kawai take saki nace anya kuwa wannan murmushi babu biyu a ƙasa kuwa?.
Bayan sun gaisa tace
“Bari na sauƙe dahuwar nan don Allah, kema ya kamata ki fara shirin auren nan fa, in kin je gida ki cewa Innar ki ta fara shirya ki kuma ki ce mata ina gyara sosai da kuma bada magungunan mata masu kyau”
Caraf Ƴar Iya tace
“Gyara kuma na me?”
Halima da yake irin matan nan ne marasa kunya kuma babu ruwan su da yaro ko babba tace
“Bari na sauƙe na dawo”
Sauƙe tukunyar tayi tare da ɗaura wata tukunyar da alamar abincin dare zata girka. Wurin su ta dawo ta zauna sannan ta maida kallon ta ga Ƴar Iya.
“Yauwah Ƙawar amarya kike tambaya kan batun gyara koh?” kai Ƴar Iya ta gyaɗa tare da maida hankalin ta ga Halima.
“Toh kafin nan dai ya kamata na san sunan amarya da ƙawar ta ko?”
A'i tace
“Ni suna na A'i wannan kuma Aminiya ta ce Ƴar Iya, halan zaki ji ana labarin ta ko da yake mu ma kan mu bamu san ki ba a ƙauyen duk irin yawon mu”