Sashe 38
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Rayuwa kenan, yau kaine gobe kuma ba kai bane, haka Ƴar Iya wacce a yanzu ta koma Khairy ta cika sati guda cikin Naira family, abubuwa sun faru cikin satin, a ciki akwai ganawarta da Mom, wacce lokaci guda taji ƙaunar yarinyar cikin ranta, sai kuma hutun makaranta da sauran yara suka samu. Duk tsawon wannan lokaci, Hamma Zaki bai antayo gida ba, wayar da yake yi musu ma yanzu ba sosai ba.
Mom ta shiga matsanancin tashin hankali game da hakan, amma kullum addu'a kawai take yiwa yaron nata kan Allah ya kuɓutar da shi daga sharrin wannan matar tashi.
Yau juma'a, Mom da kanta ta saka yaran su shirya zasu je shopping, basu wani ɓata lokaci ba kowa ya shirya, fuskar kowa ɗauke da farin ciki da annashuwa banda Adda Salma, wacce haka kawai taji ta tsani Khairy, ba don komai sai tsananin kishin yadda kowa yake nan da nan da ita yayin da ita Khairy bata ma san tana yi ba.
Mall suka fara nufa, Mom tace kowa ya ɗauki abun da yake buƙata, ta saka Adda Najmah zaɓarwa Khairy kayayyakin buƙata. Kayan da aka loada mata kamar wata ƴar gata (ko dan, yanzu kam ƴar gatan ce ai). Bayan sun gama aka wuce da su wurin gyaran jiki, kowacce ta ƙara kyau kamar ba gobe, tabbas familyn Naira babu na yarwa.
Ban tsinke da mamaki ba sai da na hango Khairy wacce duk ta zarce kyawawan ahalin kusan kowanne fanni. Fuskar nan tata ta ƙara haske, ga wani ƙyalli da take yi, ban gama dawowa hankali na ba na cilla ido na kan gashin da aka gyara sai ƙyalli yake. In da badan da ido na na kalli gashin nan ba da sai nace ba na Khairy bane, wannan danƙararren gashin nata ya koma wani miƙaƙƙen gashi.
Ayrah ce ta kalli Khairy tace “Khairy kin ganki kuwa?”
Wani murmushi ta sake, take wasu fararen haƙware jere ras da su suka bayyana, yayinda kuncin ta ya lotsa. Cikin Muryar ta mai daɗi tace “Aradu kuma kunyi kyau”
Mom dake kallon su cike da sha'awa ta cilla wa Khairy harara, ba shiri tace “Yi haƙuri Mom, na manta!”
Sake fuska mom ɗin tayi tana rungumo Khairyn “Is ok daughter, kiyi ƙoƙarin gyara maganar ki, yanzu in wani yaji kina cewa Aradu to ko kallon ki ba zai kuma ba duk irin kyan da kika yi”
Zaro ido tayi tace “Zan ma gyara ai” ta ƙarasa a yangance har sai da ƴan uwanta suka dara. Daga nan suka fito suka wuce gida.
Cikin hutun su Fauzah Khairy ta ƙara wayewa, Mom na janta a jiki, haka Mommah yayin da duk kulawar da suke bata Nenne ta kere su a wannan fanni.
Daf da zasu koma ne Granny ta shawarci uncle Suraj game da karatun Khairyn.
“Eh Hajiya nima Ina son tuntuɓar ki Kan hakan amma ina laifin a fara nema mata mai Lesson daga baya sai ta shiga makarantar?”
Granny tace “Babu laifi, dama kawai saboda yadda naga itama ta fara sha'awar karatun ne”
“To Hajiya zanyi wa Nennen yara magana, ta nema mata Malama mace in yasa ko na 1month tayi mata sai a Kaita makarantar”.
“Toh madalla, Allah amfana”.
Daga nan suka shiga hirar su ta Duniya.
Nenne da kanta ta zaɓawa Khairy ɗaliba, ranar da Madam Ajimola ta fara zuwa tayi iyakar iyawarta ganin Khairy ta fahimci darasin, babu laifi ta gane sosai. Malama Ruƙayya ma tazo tayi mata karatun Alkur'ani sai dai babu wani cigaba, hakan yasa ta nemi ganawa da Nenne kan batun.
★★★★★★★★
*ALEE POV*
Kwance yake akan makeken gadon sa ya rasa me yake masa daɗi a duniyar, a hankali ya miƙe tare da ziraro kyakkyawar ƙafarsa ƙasa, parlourn ya fito ya duba ko ina Pretty ta shiga. Cike da ƙyanƙyami yake takawa duk da akwai takalmi a ƙafar tashi, fuska ya yamutsa a hankali ya furta “bullshit”
Ƙarar fitar motar ta da yaji yasa ya maida dubansa ga window, ganin tabbas motar ta ce ta fita yasa yaja tsaki tare da dafe kanshi.
Cike da takaicin Hali iri na pretty ya koma bedroom ɗinsa.
Da kanshi ya tattare ya gyara bed ɗin sannan ya share, ya fesa room freshener, nan da Nan ɗakin ya gauraye da ƙamshi, Yana yi Yana tsaki. Cikin ranshi kuwa Allah wadaran aure irin nashi yake yi, to me ma Wai yakai shi Auren pretty ne?”
Kanshi da ya Sara ne yasa ya bar tunanin ya nufi toilet, cikin ranshi Yana ayyana dalilin da yasa idan zai yi dogon nazari Akan pretty sai kanshi ya Sara.
A daddafe ya fito ya shirya cikin khakin sojoji Wanda ke matuƙar amsarshi, fuskar nan tamau Kamar a filin yaƙi. Yurare ya buɗa sannan ya fito. Direct parking lot ya nufa, daidai farar motarshi ya ysaya Yana ɗan yamutsa fuska, ko ta Kan gateman dake gaisuwa bai bi ba ya figi motarshi sai barrack.
Captain Stanley wanda ya zamo sabon aboki gare shi ya fahimci Hamma Zaki na cikin damuwa.
“Dude, watz wrong, you look so worn out, why?”
Har sai da ya cire ran zai amsa mishi can yaji muryarsa na faɗin “I want to go home friend” ya faɗa cikin tsantsar nuna damuwa. Captain Stanley kuwa mamaki ya cika shi, tunani yake wai dama Captain Alee na da relations a Nigeria?, If Yana da why baya ziyarar su. Murmushi yayi Yana kamo hannun sa
“C'mon friend tare Zamu je ai, naga Kamar baka da lafiya ma”
Shiru Hamma Zaki yayi Yana bin Captain Stanley da Ido.
A ranar yayi musu booking flight, sannan ya koma gida, har lokacin pretty Bata dawo ba. Tsaki yayi ya wuce Zuwa bedroom ɗin shi sannan ya haɗa kayansa cikin trolley.
Ko tsaraba bai yi musu ba ya nemi wajen baccin sa.
Washegari da safe suka wuce airport, sai Adamawa, Dr. Faruq ne yazo ya miƙa su gida. Lokacin Mom na haɗa snacks a kitchen Kamar daga sama ta jiyo ƙamshin turaren da ko giya ta Sha in taji tasan na waye.
Cikin sauri ta juyo Dan ganewa idon ta abun da take tsammani. Ai kuwa shi din ne, Bata yi aune ba Hawaye suka fara zubo mata, Shima hawayen ne yake zubowa daga idanuwan sa, idan yace bai yi missing mom din NASA ba to yayi ƙarya.
Hamma Zaki ne yayi ƙarfin halin share hawayen dake ambaliya daga idanuwan Mom ɗin.
“Is ok Mom, I miss u, ”
Ya faɗa Yana hugging Mom ɗin,
Murmushi Mai haɗe da Hawaye ta sake itama tana hugging nashi tightly Kamar zaa ƙwace mata shi.
A parlour suka yada zango, ganin yadda ya rame yasa Mom ƙara tausaya mishi, ko Bata sani ba tasan yana Jin jiki. Trolleyn shi yaja zuwa bedroom ɗin shi, daidai frame ɗin dake ɗakin ya tsaya Kamar wani dolo ƴana nazari. Wayar shi da tayi ƙara yasa ya zabura Yana sakin tsaki. Ganin Mai ƙiran yasa yayi picking. Ba tare da yace komai ba yaji muryarta na dukan dodon kunnen sa.
“Haba Aliyu, yanzu FISABILILLAHI don zaka je wurin iyayenka kawai sai ka tafi babu wani notification, ba za ka ma iya jura na ba kenan....?, Naji ka rasa wa zaka barwa saƙon ma sai maigadi, to lallai lallai Sati ɗaya na baka ka tabbatar ka dawo kaji ko?”
Kamar tana gaban sa ya gyaɗa kai Yana hanging call ɗin.
“Kai Fauzah, kin san Allah a duniyar nan ni babu abunda nike tsoro, ina daidai da komai da kika ganni”
Ayrah ta sheƙe da dariya tace “gaskiya Khairy baki da dama, to wallahi duk iya shegen ki da zaki ga Hamma Zaki wollah sai kin jijjiga”
Itama dariyar tayi tana miƙewa tsaye
“Inma Hamma Namun daji ne ba zaki ba wollah bai kai naji tsoronsa ba, ni naga Alama koma waye shi tsoronshi kuke, hala malamin kune?”
Janyo ta Yesmeen tayi ta zauna tace “Ke Khairy wallahi ki godewa Allah Hamma Zaki baya nan yanzu, kina cewa malamin mu ne shine fa na jikin picture ɗin parlourn Mom, ƴaƴan Fauzah ne”
Dumm gabanta ya faɗin cikin ranta tace “Wannan mai siffar aljanun tsabagen kyau?” zahiri kuma ta cillawa Yesmeen harara
“Ke kar ki wani dame ni, ina ruwa na da shi, nidai abunda na sani shine ko shi waye bazan ji tsoronsa ba”.
“hmm” Fauzah ta faɗa “Zanso naga ƙarshen iyashegen ki Khairy, wollah zan so naga karon ki da Hamma Zaki”
“Mtss sai kiyi kuma, don baki san wacece Ƴar Iya ba shiyasa kike tunanin zanji tsoron wani mahaluki, ni nan da kike gani duk ƙauyen mu kowa tsoro na yake, b don komai ba wasu kam sai saboda hannu na”
Ta faɗa tana pointing hannun nata.
Mom ta shiga matsanancin tashin hankali game da hakan, amma kullum addu'a kawai take yiwa yaron nata kan Allah ya kuɓutar da shi daga sharrin wannan matar tashi.
Yau juma'a, Mom da kanta ta saka yaran su shirya zasu je shopping, basu wani ɓata lokaci ba kowa ya shirya, fuskar kowa ɗauke da farin ciki da annashuwa banda Adda Salma, wacce haka kawai taji ta tsani Khairy, ba don komai sai tsananin kishin yadda kowa yake nan da nan da ita yayin da ita Khairy bata ma san tana yi ba.
Mall suka fara nufa, Mom tace kowa ya ɗauki abun da yake buƙata, ta saka Adda Najmah zaɓarwa Khairy kayayyakin buƙata. Kayan da aka loada mata kamar wata ƴar gata (ko dan, yanzu kam ƴar gatan ce ai). Bayan sun gama aka wuce da su wurin gyaran jiki, kowacce ta ƙara kyau kamar ba gobe, tabbas familyn Naira babu na yarwa.
Ban tsinke da mamaki ba sai da na hango Khairy wacce duk ta zarce kyawawan ahalin kusan kowanne fanni. Fuskar nan tata ta ƙara haske, ga wani ƙyalli da take yi, ban gama dawowa hankali na ba na cilla ido na kan gashin da aka gyara sai ƙyalli yake. In da badan da ido na na kalli gashin nan ba da sai nace ba na Khairy bane, wannan danƙararren gashin nata ya koma wani miƙaƙƙen gashi.
Ayrah ce ta kalli Khairy tace “Khairy kin ganki kuwa?”
Wani murmushi ta sake, take wasu fararen haƙware jere ras da su suka bayyana, yayinda kuncin ta ya lotsa. Cikin Muryar ta mai daɗi tace “Aradu kuma kunyi kyau”
Mom dake kallon su cike da sha'awa ta cilla wa Khairy harara, ba shiri tace “Yi haƙuri Mom, na manta!”
Sake fuska mom ɗin tayi tana rungumo Khairyn “Is ok daughter, kiyi ƙoƙarin gyara maganar ki, yanzu in wani yaji kina cewa Aradu to ko kallon ki ba zai kuma ba duk irin kyan da kika yi”
Zaro ido tayi tace “Zan ma gyara ai” ta ƙarasa a yangance har sai da ƴan uwanta suka dara. Daga nan suka fito suka wuce gida.
Cikin hutun su Fauzah Khairy ta ƙara wayewa, Mom na janta a jiki, haka Mommah yayin da duk kulawar da suke bata Nenne ta kere su a wannan fanni.
Daf da zasu koma ne Granny ta shawarci uncle Suraj game da karatun Khairyn.
“Eh Hajiya nima Ina son tuntuɓar ki Kan hakan amma ina laifin a fara nema mata mai Lesson daga baya sai ta shiga makarantar?”
Granny tace “Babu laifi, dama kawai saboda yadda naga itama ta fara sha'awar karatun ne”
“To Hajiya zanyi wa Nennen yara magana, ta nema mata Malama mace in yasa ko na 1month tayi mata sai a Kaita makarantar”.
“Toh madalla, Allah amfana”.
Daga nan suka shiga hirar su ta Duniya.
Nenne da kanta ta zaɓawa Khairy ɗaliba, ranar da Madam Ajimola ta fara zuwa tayi iyakar iyawarta ganin Khairy ta fahimci darasin, babu laifi ta gane sosai. Malama Ruƙayya ma tazo tayi mata karatun Alkur'ani sai dai babu wani cigaba, hakan yasa ta nemi ganawa da Nenne kan batun.
★★★★★★★★
*ALEE POV*
Kwance yake akan makeken gadon sa ya rasa me yake masa daɗi a duniyar, a hankali ya miƙe tare da ziraro kyakkyawar ƙafarsa ƙasa, parlourn ya fito ya duba ko ina Pretty ta shiga. Cike da ƙyanƙyami yake takawa duk da akwai takalmi a ƙafar tashi, fuska ya yamutsa a hankali ya furta “bullshit”
Ƙarar fitar motar ta da yaji yasa ya maida dubansa ga window, ganin tabbas motar ta ce ta fita yasa yaja tsaki tare da dafe kanshi.
Cike da takaicin Hali iri na pretty ya koma bedroom ɗinsa.
Da kanshi ya tattare ya gyara bed ɗin sannan ya share, ya fesa room freshener, nan da Nan ɗakin ya gauraye da ƙamshi, Yana yi Yana tsaki. Cikin ranshi kuwa Allah wadaran aure irin nashi yake yi, to me ma Wai yakai shi Auren pretty ne?”
Kanshi da ya Sara ne yasa ya bar tunanin ya nufi toilet, cikin ranshi Yana ayyana dalilin da yasa idan zai yi dogon nazari Akan pretty sai kanshi ya Sara.
A daddafe ya fito ya shirya cikin khakin sojoji Wanda ke matuƙar amsarshi, fuskar nan tamau Kamar a filin yaƙi. Yurare ya buɗa sannan ya fito. Direct parking lot ya nufa, daidai farar motarshi ya ysaya Yana ɗan yamutsa fuska, ko ta Kan gateman dake gaisuwa bai bi ba ya figi motarshi sai barrack.
Captain Stanley wanda ya zamo sabon aboki gare shi ya fahimci Hamma Zaki na cikin damuwa.
“Dude, watz wrong, you look so worn out, why?”
Har sai da ya cire ran zai amsa mishi can yaji muryarsa na faɗin “I want to go home friend” ya faɗa cikin tsantsar nuna damuwa. Captain Stanley kuwa mamaki ya cika shi, tunani yake wai dama Captain Alee na da relations a Nigeria?, If Yana da why baya ziyarar su. Murmushi yayi Yana kamo hannun sa
“C'mon friend tare Zamu je ai, naga Kamar baka da lafiya ma”
Shiru Hamma Zaki yayi Yana bin Captain Stanley da Ido.
A ranar yayi musu booking flight, sannan ya koma gida, har lokacin pretty Bata dawo ba. Tsaki yayi ya wuce Zuwa bedroom ɗin shi sannan ya haɗa kayansa cikin trolley.
Ko tsaraba bai yi musu ba ya nemi wajen baccin sa.
Washegari da safe suka wuce airport, sai Adamawa, Dr. Faruq ne yazo ya miƙa su gida. Lokacin Mom na haɗa snacks a kitchen Kamar daga sama ta jiyo ƙamshin turaren da ko giya ta Sha in taji tasan na waye.
Cikin sauri ta juyo Dan ganewa idon ta abun da take tsammani. Ai kuwa shi din ne, Bata yi aune ba Hawaye suka fara zubo mata, Shima hawayen ne yake zubowa daga idanuwan sa, idan yace bai yi missing mom din NASA ba to yayi ƙarya.
Hamma Zaki ne yayi ƙarfin halin share hawayen dake ambaliya daga idanuwan Mom ɗin.
“Is ok Mom, I miss u, ”
Ya faɗa Yana hugging Mom ɗin,
Murmushi Mai haɗe da Hawaye ta sake itama tana hugging nashi tightly Kamar zaa ƙwace mata shi.
A parlour suka yada zango, ganin yadda ya rame yasa Mom ƙara tausaya mishi, ko Bata sani ba tasan yana Jin jiki. Trolleyn shi yaja zuwa bedroom ɗin shi, daidai frame ɗin dake ɗakin ya tsaya Kamar wani dolo ƴana nazari. Wayar shi da tayi ƙara yasa ya zabura Yana sakin tsaki. Ganin Mai ƙiran yasa yayi picking. Ba tare da yace komai ba yaji muryarta na dukan dodon kunnen sa.
“Haba Aliyu, yanzu FISABILILLAHI don zaka je wurin iyayenka kawai sai ka tafi babu wani notification, ba za ka ma iya jura na ba kenan....?, Naji ka rasa wa zaka barwa saƙon ma sai maigadi, to lallai lallai Sati ɗaya na baka ka tabbatar ka dawo kaji ko?”
Kamar tana gaban sa ya gyaɗa kai Yana hanging call ɗin.
“Kai Fauzah, kin san Allah a duniyar nan ni babu abunda nike tsoro, ina daidai da komai da kika ganni”
Ayrah ta sheƙe da dariya tace “gaskiya Khairy baki da dama, to wallahi duk iya shegen ki da zaki ga Hamma Zaki wollah sai kin jijjiga”
Itama dariyar tayi tana miƙewa tsaye
“Inma Hamma Namun daji ne ba zaki ba wollah bai kai naji tsoronsa ba, ni naga Alama koma waye shi tsoronshi kuke, hala malamin kune?”
Janyo ta Yesmeen tayi ta zauna tace “Ke Khairy wallahi ki godewa Allah Hamma Zaki baya nan yanzu, kina cewa malamin mu ne shine fa na jikin picture ɗin parlourn Mom, ƴaƴan Fauzah ne”
Dumm gabanta ya faɗin cikin ranta tace “Wannan mai siffar aljanun tsabagen kyau?” zahiri kuma ta cillawa Yesmeen harara
“Ke kar ki wani dame ni, ina ruwa na da shi, nidai abunda na sani shine ko shi waye bazan ji tsoronsa ba”.
“hmm” Fauzah ta faɗa “Zanso naga ƙarshen iyashegen ki Khairy, wollah zan so naga karon ki da Hamma Zaki”
“Mtss sai kiyi kuma, don baki san wacece Ƴar Iya ba shiyasa kike tunanin zanji tsoron wani mahaluki, ni nan da kike gani duk ƙauyen mu kowa tsoro na yake, b don komai ba wasu kam sai saboda hannu na”
Ta faɗa tana pointing hannun nata.