Sashe 19
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haushi ne ya cika Baba Haro Jin Muryar yarinya tana masa baɗala a bishiyar da ke cikin lambun sa.
“Wallahi in na hau duk sai kun raina kan ku, ƴan iskan yara marasa tarbiyya”
Daga sama Ƴar Iya ta ƙara jefo wani ƙwallon mangwaron tana faɗin.
“Shegu tsofin nan sai shegen son girman tsiya kamar gyambo, Toh ina ka isa ka hau”
Baba Haro yace
“Ammah dai kukan Allah yayi matasa albarka, tsofait-sofai da ni kuke wa ɗiban albarka, Toh yau kuwa baku isa barin lambun na nlafiya ba.
A'i tayi dariya cike da raini da gatsali tace
“In mun zo fita lafiya ka zare lafiyar tamu. Kaji tsoho da ɗan banzan mugun baki”
Ƴar Iya tayi caraf tace
“Ni shi yasa bana sararawa tsofin nan, da lanƙwasassun ƙafafuwan su kamar agwagi”
Duk wannan tsiyar da suke wa Baba Haro kawai ya ƙyale su ne, rigar sa ya ɗage tare da naɗe ƙafar wando sai kan bishiya.
Ganin yana hawa bai sa sun ji tsoro ba saboda sun san salon su zai ƙayatar. Sai da Baba Haro ya fara nisa a hawan bishiyar su kuwa dariya kawai suke yi ganin yadda yake wani kama bishiya kamar ba namiji ba.
Daf da reshen da suke ya bi hakan yasa suka fara niyyar barin reshen, duk inda suka yi sai yace sai ya bisu. A haka suka yi ta kewaya wa da Baba Haro ɗan ƙarfin hali har sai da suka tabbatar ya wahala ba kuma zai iya cigaba ba.
A'i ce ta fara sauƙa ta can wani bangare ita kuma Ƴar Iya tabi wani tsililin reshe. Baba Haro ganin babu nisa tsakanin shi da wannan hatsabibiyar yarinya yasa yayi azamar bin ta.
Tsam ta dire ƙasa abun ta tana kaɗe ƙasar da ta buɗe jikin ta sannan ta tsaya dakon faɗowar rigimammen tsohon.
Tiiiiiiiiim kake ji sai ga Baba Haro a ƙasa.
“Wayyo Allah na, na shiga uku Ni Haro, shikenan wayyoh Allah na”
Dariya mugunta Ƴar Iya ta sheƙe da ita tana yima Baba Haro gwalo.
“Shegen tsoho ai sai muga ƙarshen abun naka, yanzu sai ka bi mu ai. Babu ko kunya kana bin Ƴaƴan cikin ka don sun hau mangwaro.” ta ƙarasa tana wulla masa harara tare da ke cewa da wata dariyar. A'i kuwa dariya ta hanata faɗin komai sai iya nuna Baba Haro take d yatsa tana dariya.
“Tashi mana ɗan tsoho rigimamme” Ƴar iya ta faɗa cikin shaƙiyyanci.
Baba Haro kuwa danasanin biye su yake yi, ya haɗa uban zufa kamar wanda yayi gudun ceton rai, fuskar nan shaɓe-shaɓe da hawaye da majina.
A gaban sa suka koma kan bishiyar tunda ya kasa ko da tashi ne yana ma tunanin ya karye. Tun daga bishiyar suke wullo ɓula ɓukan mangwaro ƙasa kuma sai sun saita kan Baba Haro su wullo. Baba Haro dai yau yaga ta kanshi, sai da suka wullo fiye da mangwaro hamsin tukun suka sauƙo daga bishiyar.
Tsam ko ɗaya basu bar mangwaron ba suke kwashe abun su cikin wani daro dake cikin lambun. Bayan sun kwashe suka ɗauko ƙullin kashu ɗin su suka yi hanyar fita, har zasu wuce Ƴar Iya ta juyo tare da zaro mangwaro ɗaya daga daron dake kan Ai.
A gaban Baba Haro ta tsugunna haɗi da miƙa masa mangwaron sannan ta ce:
“Allah ya sauwaƙe Baba Mai mangwaro, sai mun zo ciran na gobe.
In an tambaye ka waye yayi maka haka kace Ƴar Iya mai hannun ɓarna ce.”
Daga haka suka fice daga lambun suka ɗauki hanyar gidan Halima.
(Nace wannan ƙawance haka, daga haɗuwa ɗaya har anyi wa Iya hijira?”
TOH FAH!
ƳAR IYA ANYI ƘAWA FA DA GASKE.
GA KUMA SU HAMMA ZAKI FARIN CIKIN ƳAN MATA.
YANZU FA WASAN ZAI FARA
KU CI GABA DA KASANCEWA DA ALƘALAMIN DIAMOND LADY
SHARE & COMMENT PLEASE!
[5/9, 7:59 PM] 💎Diamond Bhatool💎:
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
__Fictional story with life full of childhood, entertainment, revenge, betrayal and heart touching love __
SHAFI NA ‘‘‘‘‘31&32’’’’’
[*Gare ki ƴar uwa mai albarka, ki riƙe ibadar ki yadda ya kamata a gidan auren ki*. *ko da wasa kada kiyi abota da mutanen banza, ko kin san illar alaƙar mace mai aure da mutanen banza?*
*To kaɗe kunnuwan ki kiji alaƙa da mutanen banza tsaf zai sa ki rasa ƙimar ki a wurin mai gida saboda ko yaushe zasu kasance cikin baki gurɓatacciyar shawara ne wanda in baki yi hankali kin lura da wuri ba kan sa ki rasa mijin gabaɗaya*
*Saboda haka a kula da ƙawayen da za'a yi mu'amala da su a gidan aure, da zarar kin fahimci ƙawar nan ba ta ƙwarai bace to tun wuri ki sallame ta kafin tayi galabar koya miki miyagun halaye.*
*A ko da yaushe, ki riƙe wannan ƙawar da in kin samu saɓani da mai gida bayan kin sanar da ita zata yi ta baki haƙuri tare da nusar dake laifin ki cikin zaman auren ki*.]
Daga haka suka fice daga lambun suka ɗauki hanyar gidan Halima.
“Salamu Alekum, masu gidan suna nan?” A'i ta faɗa tare da shigewa gidan Ƴar Iya na bin bayan ta.
Daga cikin ɗaki Halima ta fito tane washe baki
“Wa alaikumussalamu, masu gidan suna nan...maraba da baƙi ku iso ciki manah”
Ƴar Iya da suke tsaye bakin bishiyar yandi dake tsakar gidan suka fara ajiye shirgin su, A'i ta sauƙe daron mangwaro Ƴar Iya ta jiye ƙullin kashu ɗin su a ƙasa.
Halima ce ta ƙaraso yadda suke ɗauke da taburma a hannun ta. “Maraba da Ƴar Iya mai hannun ɓarna” dariyar shaƙiyyanci Ƴar Iya tayi yayin da take ƙoƙarin zama kan taburmar da Halima ta shimfiɗa musu.
Sai da suka zauna ɗamas sannan suka fara janyo mangwaro da kashu ɗin.
Murmushi Halima tayi tace
“Mangwaro haka daga ina?”
Ƴar Iya ta amsa da faɗin
“Cirowa muka yi a lambun Baba Haro”
A'i ta ƙyalƙyale da dariya tace
“Yana can mun bar shi ma a ɓalle”
Zare ido Halima tayi tana ƙara kallon su alamar tana buƙatar ƙarin bayani.
A'i tace
“Munje cira inji in gaya miki tsohon ya hana mu, shine muka masa kwaskwarima muka cira daga nan muka yo nan”
“Hmm” Halima tace “Ku dai kam bakwa gajiya da tsokala, ko da yake akwai mai hannun ɓarna cikin ku.” ta ɗan dakata ganin irin kallon da Ƴar Iya ke bin ta da shi, cikin wayincewa taci gaba
“Duk da haka gaba ta kaimu Ni da sabbin ƙawaye na, To yanzu dai bari na wanke mana uku uku sai mu sha”
Tashi Halima tayi ta wanke mangwaro goma ta jawo su suka fara sha suna hira. Daga ƙarshe dai tas suka shanye wannan mangwaro haka kashu, daga nan suka yi mata sallama Ƴar Iya na faɗin zata tafi neman halal ɗin ta ita ma. Daga haka A'i tayi gidan su Ƴar Iya ta nufi gidan Iyar ta.
★★★★★★★★
*SHAREEF POV*
Shirye-shirye ake cikin gidan General Muhammad Naira. Ta kowanne ɓangare shiri ake yi babu kama ƙafar yaro. Kowa ka gani cikin farin ciki yake yayin da Hamma Zaki yaƙi fitowa gabaɗaya.
Zaune yake a bedside kamar kullum cikin white pyjamas, ƙafarsa ɗaya na kan ɗaya yayin da fuskar shi ke a ɗaure. Hakan ya bani damar fahimtar ba don hidimar yake ba duba da yadda ahalin sa ke ɗauki akai.
Wayar shi da yake latsawa ce tayi ringing bai yi niyyar picking ba saboda sam yau baya son a dame shi. Can ganin mai ƙiran nashi da niyyar dainawa yasa ya zaro wayar da niyyar kashe ta gabaɗaya, sunan Dude da ya gani yasa yaja tsaki tare da picking. Can ƙasan maƙoshi ya amsa sallamar Dr. Faruq ɗin
“Wa alykumussalam” Dr faruq kuwa murmushi Mai sauti yayi tare da faɗin
“Buddy duk cikin magagin rashi don taron ne har nayi kira uku baka yi picking ba?
“Mtss” Hamma Zaki yayi tsaki kamar wanda aka yiwa dole yace “Idan abun da ka ƙira ka faɗa ne, lemme hang the call.”
Cak Dr. Faruq ya tsaya da dariyar da yake yi coz ya san halin mutumin nashi.
Cikin son danne dariyar tashi yace
“Yau Buddy shiru naji daga ɓangaren ka, Hamma Saleem ɗazu ya ƙira yana tambaya ta ko ya batun shirye-shiryen namu, I told him baka ce komai ba sai yanzu dai yace nayi maka magana”
“Ok” kawai Hamma Zaki yace. Cikin takaici Dr. Faruq yace
“Alright tunda ok kaɗai zaka ce, sai mutum ya dage yayi maka magana ka wani ce ok. Shikenan nimah zan cewa Hamma Saleem ɗin kace ok kawai”
Cike da ƙosawa da maganar ɗin tuni kan shi ya fara sarawa yace
“Sorry Buddy, ban hana ku shirya komai ba, kawai ni ɗin ne bana buƙatar shiri dole ta sa zan yi attending ma”
“Na fahimce ka Buddy, worry less please zan kula da komai and ka daure ka fara sabawa da jama'a da kuma hayaniya ko don saboda gaba.”
“Ok” Hamma zaki ya faɗa tare da katse ƙiran yana jan tsaki.
Sauƙa yayi tare da sanya bathrobe ya nufi toilet. Yana fitowa yayi drying jikin shi tare da shafa creams nashi. Cikin closet ya ɗauko wata white jallabiya ya sanya, ko turare be samu damar fesawa ba ya nufi sidedrawer tare da ɗauko pcm tablet, fridge ya nufa ya ɗauko warm bottle water tare da Shan pcm ɗin yana yamutsa fuska. Yana gama sha ya haye bed Don ya huta.
Vibration na wayar shi ya tayar da shi
Major Kabir Joda ne hakan yasa yayi picking tare da kara wayar a kunnen sa.
“Assalamu Alykum” aka ce daga ɓangaren can. Sai a lokacin Hamma Zaki ya fara motsa baki tare da yamutsa fuska.
“Wa alykumussalam” ya amsa can ƙasa-ƙasa.
“Captain?, Ain't u preparing anything there?”
“Nothing sir!” ya bashi amsa a taƙaice.
“Toh akwai sabbin uniform da zaka sanya a wurin taron, Please ka aiko a amsa maka”
“Ok sir!”
Sanin Halin Captain yasa Major Kabir hanging call ɗin.
“Wallahi in na hau duk sai kun raina kan ku, ƴan iskan yara marasa tarbiyya”
Daga sama Ƴar Iya ta ƙara jefo wani ƙwallon mangwaron tana faɗin.
“Shegu tsofin nan sai shegen son girman tsiya kamar gyambo, Toh ina ka isa ka hau”
Baba Haro yace
“Ammah dai kukan Allah yayi matasa albarka, tsofait-sofai da ni kuke wa ɗiban albarka, Toh yau kuwa baku isa barin lambun na nlafiya ba.
A'i tayi dariya cike da raini da gatsali tace
“In mun zo fita lafiya ka zare lafiyar tamu. Kaji tsoho da ɗan banzan mugun baki”
Ƴar Iya tayi caraf tace
“Ni shi yasa bana sararawa tsofin nan, da lanƙwasassun ƙafafuwan su kamar agwagi”
Duk wannan tsiyar da suke wa Baba Haro kawai ya ƙyale su ne, rigar sa ya ɗage tare da naɗe ƙafar wando sai kan bishiya.
Ganin yana hawa bai sa sun ji tsoro ba saboda sun san salon su zai ƙayatar. Sai da Baba Haro ya fara nisa a hawan bishiyar su kuwa dariya kawai suke yi ganin yadda yake wani kama bishiya kamar ba namiji ba.
Daf da reshen da suke ya bi hakan yasa suka fara niyyar barin reshen, duk inda suka yi sai yace sai ya bisu. A haka suka yi ta kewaya wa da Baba Haro ɗan ƙarfin hali har sai da suka tabbatar ya wahala ba kuma zai iya cigaba ba.
A'i ce ta fara sauƙa ta can wani bangare ita kuma Ƴar Iya tabi wani tsililin reshe. Baba Haro ganin babu nisa tsakanin shi da wannan hatsabibiyar yarinya yasa yayi azamar bin ta.
Tsam ta dire ƙasa abun ta tana kaɗe ƙasar da ta buɗe jikin ta sannan ta tsaya dakon faɗowar rigimammen tsohon.
Tiiiiiiiiim kake ji sai ga Baba Haro a ƙasa.
“Wayyo Allah na, na shiga uku Ni Haro, shikenan wayyoh Allah na”
Dariya mugunta Ƴar Iya ta sheƙe da ita tana yima Baba Haro gwalo.
“Shegen tsoho ai sai muga ƙarshen abun naka, yanzu sai ka bi mu ai. Babu ko kunya kana bin Ƴaƴan cikin ka don sun hau mangwaro.” ta ƙarasa tana wulla masa harara tare da ke cewa da wata dariyar. A'i kuwa dariya ta hanata faɗin komai sai iya nuna Baba Haro take d yatsa tana dariya.
“Tashi mana ɗan tsoho rigimamme” Ƴar iya ta faɗa cikin shaƙiyyanci.
Baba Haro kuwa danasanin biye su yake yi, ya haɗa uban zufa kamar wanda yayi gudun ceton rai, fuskar nan shaɓe-shaɓe da hawaye da majina.
A gaban sa suka koma kan bishiyar tunda ya kasa ko da tashi ne yana ma tunanin ya karye. Tun daga bishiyar suke wullo ɓula ɓukan mangwaro ƙasa kuma sai sun saita kan Baba Haro su wullo. Baba Haro dai yau yaga ta kanshi, sai da suka wullo fiye da mangwaro hamsin tukun suka sauƙo daga bishiyar.
Tsam ko ɗaya basu bar mangwaron ba suke kwashe abun su cikin wani daro dake cikin lambun. Bayan sun kwashe suka ɗauko ƙullin kashu ɗin su suka yi hanyar fita, har zasu wuce Ƴar Iya ta juyo tare da zaro mangwaro ɗaya daga daron dake kan Ai.
A gaban Baba Haro ta tsugunna haɗi da miƙa masa mangwaron sannan ta ce:
“Allah ya sauwaƙe Baba Mai mangwaro, sai mun zo ciran na gobe.
In an tambaye ka waye yayi maka haka kace Ƴar Iya mai hannun ɓarna ce.”
Daga haka suka fice daga lambun suka ɗauki hanyar gidan Halima.
(Nace wannan ƙawance haka, daga haɗuwa ɗaya har anyi wa Iya hijira?”
TOH FAH!
ƳAR IYA ANYI ƘAWA FA DA GASKE.
GA KUMA SU HAMMA ZAKI FARIN CIKIN ƳAN MATA.
YANZU FA WASAN ZAI FARA
KU CI GABA DA KASANCEWA DA ALƘALAMIN DIAMOND LADY
SHARE & COMMENT PLEASE!
[5/9, 7:59 PM] 💎Diamond Bhatool💎:
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
__Fictional story with life full of childhood, entertainment, revenge, betrayal and heart touching love __
SHAFI NA ‘‘‘‘‘31&32’’’’’
[*Gare ki ƴar uwa mai albarka, ki riƙe ibadar ki yadda ya kamata a gidan auren ki*. *ko da wasa kada kiyi abota da mutanen banza, ko kin san illar alaƙar mace mai aure da mutanen banza?*
*To kaɗe kunnuwan ki kiji alaƙa da mutanen banza tsaf zai sa ki rasa ƙimar ki a wurin mai gida saboda ko yaushe zasu kasance cikin baki gurɓatacciyar shawara ne wanda in baki yi hankali kin lura da wuri ba kan sa ki rasa mijin gabaɗaya*
*Saboda haka a kula da ƙawayen da za'a yi mu'amala da su a gidan aure, da zarar kin fahimci ƙawar nan ba ta ƙwarai bace to tun wuri ki sallame ta kafin tayi galabar koya miki miyagun halaye.*
*A ko da yaushe, ki riƙe wannan ƙawar da in kin samu saɓani da mai gida bayan kin sanar da ita zata yi ta baki haƙuri tare da nusar dake laifin ki cikin zaman auren ki*.]
Daga haka suka fice daga lambun suka ɗauki hanyar gidan Halima.
“Salamu Alekum, masu gidan suna nan?” A'i ta faɗa tare da shigewa gidan Ƴar Iya na bin bayan ta.
Daga cikin ɗaki Halima ta fito tane washe baki
“Wa alaikumussalamu, masu gidan suna nan...maraba da baƙi ku iso ciki manah”
Ƴar Iya da suke tsaye bakin bishiyar yandi dake tsakar gidan suka fara ajiye shirgin su, A'i ta sauƙe daron mangwaro Ƴar Iya ta jiye ƙullin kashu ɗin su a ƙasa.
Halima ce ta ƙaraso yadda suke ɗauke da taburma a hannun ta. “Maraba da Ƴar Iya mai hannun ɓarna” dariyar shaƙiyyanci Ƴar Iya tayi yayin da take ƙoƙarin zama kan taburmar da Halima ta shimfiɗa musu.
Sai da suka zauna ɗamas sannan suka fara janyo mangwaro da kashu ɗin.
Murmushi Halima tayi tace
“Mangwaro haka daga ina?”
Ƴar Iya ta amsa da faɗin
“Cirowa muka yi a lambun Baba Haro”
A'i ta ƙyalƙyale da dariya tace
“Yana can mun bar shi ma a ɓalle”
Zare ido Halima tayi tana ƙara kallon su alamar tana buƙatar ƙarin bayani.
A'i tace
“Munje cira inji in gaya miki tsohon ya hana mu, shine muka masa kwaskwarima muka cira daga nan muka yo nan”
“Hmm” Halima tace “Ku dai kam bakwa gajiya da tsokala, ko da yake akwai mai hannun ɓarna cikin ku.” ta ɗan dakata ganin irin kallon da Ƴar Iya ke bin ta da shi, cikin wayincewa taci gaba
“Duk da haka gaba ta kaimu Ni da sabbin ƙawaye na, To yanzu dai bari na wanke mana uku uku sai mu sha”
Tashi Halima tayi ta wanke mangwaro goma ta jawo su suka fara sha suna hira. Daga ƙarshe dai tas suka shanye wannan mangwaro haka kashu, daga nan suka yi mata sallama Ƴar Iya na faɗin zata tafi neman halal ɗin ta ita ma. Daga haka A'i tayi gidan su Ƴar Iya ta nufi gidan Iyar ta.
★★★★★★★★
*SHAREEF POV*
Shirye-shirye ake cikin gidan General Muhammad Naira. Ta kowanne ɓangare shiri ake yi babu kama ƙafar yaro. Kowa ka gani cikin farin ciki yake yayin da Hamma Zaki yaƙi fitowa gabaɗaya.
Zaune yake a bedside kamar kullum cikin white pyjamas, ƙafarsa ɗaya na kan ɗaya yayin da fuskar shi ke a ɗaure. Hakan ya bani damar fahimtar ba don hidimar yake ba duba da yadda ahalin sa ke ɗauki akai.
Wayar shi da yake latsawa ce tayi ringing bai yi niyyar picking ba saboda sam yau baya son a dame shi. Can ganin mai ƙiran nashi da niyyar dainawa yasa ya zaro wayar da niyyar kashe ta gabaɗaya, sunan Dude da ya gani yasa yaja tsaki tare da picking. Can ƙasan maƙoshi ya amsa sallamar Dr. Faruq ɗin
“Wa alykumussalam” Dr faruq kuwa murmushi Mai sauti yayi tare da faɗin
“Buddy duk cikin magagin rashi don taron ne har nayi kira uku baka yi picking ba?
“Mtss” Hamma Zaki yayi tsaki kamar wanda aka yiwa dole yace “Idan abun da ka ƙira ka faɗa ne, lemme hang the call.”
Cak Dr. Faruq ya tsaya da dariyar da yake yi coz ya san halin mutumin nashi.
Cikin son danne dariyar tashi yace
“Yau Buddy shiru naji daga ɓangaren ka, Hamma Saleem ɗazu ya ƙira yana tambaya ta ko ya batun shirye-shiryen namu, I told him baka ce komai ba sai yanzu dai yace nayi maka magana”
“Ok” kawai Hamma Zaki yace. Cikin takaici Dr. Faruq yace
“Alright tunda ok kaɗai zaka ce, sai mutum ya dage yayi maka magana ka wani ce ok. Shikenan nimah zan cewa Hamma Saleem ɗin kace ok kawai”
Cike da ƙosawa da maganar ɗin tuni kan shi ya fara sarawa yace
“Sorry Buddy, ban hana ku shirya komai ba, kawai ni ɗin ne bana buƙatar shiri dole ta sa zan yi attending ma”
“Na fahimce ka Buddy, worry less please zan kula da komai and ka daure ka fara sabawa da jama'a da kuma hayaniya ko don saboda gaba.”
“Ok” Hamma zaki ya faɗa tare da katse ƙiran yana jan tsaki.
Sauƙa yayi tare da sanya bathrobe ya nufi toilet. Yana fitowa yayi drying jikin shi tare da shafa creams nashi. Cikin closet ya ɗauko wata white jallabiya ya sanya, ko turare be samu damar fesawa ba ya nufi sidedrawer tare da ɗauko pcm tablet, fridge ya nufa ya ɗauko warm bottle water tare da Shan pcm ɗin yana yamutsa fuska. Yana gama sha ya haye bed Don ya huta.
Vibration na wayar shi ya tayar da shi
Major Kabir Joda ne hakan yasa yayi picking tare da kara wayar a kunnen sa.
“Assalamu Alykum” aka ce daga ɓangaren can. Sai a lokacin Hamma Zaki ya fara motsa baki tare da yamutsa fuska.
“Wa alykumussalam” ya amsa can ƙasa-ƙasa.
“Captain?, Ain't u preparing anything there?”
“Nothing sir!” ya bashi amsa a taƙaice.
“Toh akwai sabbin uniform da zaka sanya a wurin taron, Please ka aiko a amsa maka”
“Ok sir!”
Sanin Halin Captain yasa Major Kabir hanging call ɗin.