Sashe 26
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana ƙarasowa ta zauna tare dayin murmushi. Ganin kamar ba kansu ɗaya ba yasa Mom fara gaida su.
“Ƴan mata ina yinin ku?”
Cikin ƙiƙina suka amsa babu kunya da
“Lafiya Mom,”
Mom! Mom ta ƙara nanata sunan cikin zuciyar ta, “Ikon Allah, wai mom ko wace Mom ɗin rai?” ta faɗa a ranta a fili kuma tayi murmushi tare da faɗin
“Sannun ku da zuwa, sai dai ban gane ku ba fah”
Sumy ce tayi ƙarfin halin faɗin
“Laa Mom yaranki ne ai”
Ishy ta cafke da faɗin
“Mun zo wurin Captain ne Mom”
Mom kam sun ɗaure ta da abun mamaki, ita dai iya sanin ta Son nata baya ma kula mata bare yayi mu'amala da waɗannan masu kama da Ashawos ɗin nan, murmushi kawai tayi tace
“Ku ƙira shi kuce kuna jiran shi parlourn”
Jin hakan yasa fitsararriya Pretty faɗin
“Ji rainin wayo...” bakin ta Ishy tayi saurin rufewa da hannun ta tare da fatan Allah yasa Mom Bata ji ba, sai dai aikin gama ya gama.
Fauzy ce tayi ƙarfin halin faɗin “Ki bar zancen ku da Sulaiman ya wuce mana Pretty, na san shine har yanzu a ranki” daga haka ta kalli Mom dake mamakin Pretty tace “Kiyi haƙuri Mom kada kiyi tunanin dake take, tana da rashin lafiyar maimaita abu idan ya faru da ita, ga bata iya mantuwa”
Murmushi Mom tayi tace “babu komai”
Ganin shiru babu wacce ta ɗago waya ta ƙira Hamma Zaki yasa Mom tace “Ku ƙira shi manah, ni zan wuce ciki”
Cike da duniyanci Ishy ta kaɗa yatsar ta “Wayyo Mom, Kinga saboda saurin da muke na har mun mace wayoyin mu a gida”
“Shikenan bari na wuce, zan ƙira shi”.
Bedroom ɗin ta ta koma tana mai juya maganganun baƙin Hamma Zaki. Bayan ta sanar da shi ta hanyar kiran shi a waya ta faɗa tunanin su waye waɗannan, ko suwaye da gani babu alkhairi a tattare da su, yara sam babu ɗaa bare girmama babba.....
“Hmm to Allah ya kyauta, amma tabbas tana son sanin abu game da su.
Kwance yake yana latsa wayar sa kasancewar bai jima da dawowa daga wurin aikin shi ba. Ya miƙa wayar zai ajiye gefe yaji ringing na wayar. Kamar ba zai yi picking ba ya na tsani tare da ɗagowa, ganin Mom yasa ga zare idanuwa tare da picking.
“Sweetheart...” ba tare da ta barshi ya faɗi me zai ce ba ta katse shi da faɗin
“Kana da baƙi a waje, suna jiran ka a parlour”
“Parlour?” ya faɗa cikin sigar tambaya coz Basu yi da Dr. Faruq zai shigo ba ko wani friend nashi.
“Who Are they Mom?”
“Get down and see” daga haka ta katse ƙiran.
Kamar baya so ya buɗe ƙofa tare da fitowa, shi ba mutum bane mai son gulma ba hakan yasa bai dubo daga can ba. Black jallabiya be jikin shi, kamar koyaushe ƙamshin daddaɗan turaren shi ke tashi. Sam ko kaɗan bai sa a ranshi matan nan ne baƙin shi ba hakan yasa ya miƙe zai je Bedroom ɗin Mom. Cak ya tsaya jin an riƙe hannun shi. A hanzarce ya waiwayo don ganin waye wannan. Dum! Ƙirjin shi ya buga, shi bai yi magana ba sai wani kallo da yake aika mata cikin ranshi kuma yana faɗin (This girl again?”.
Ganin hankalin shi na kanta yasa ta marairaice fuska “Please Sweetheart, no sau ɗaya ka bani damar nan, wallahi ina son ka shi yasa na baro Abuja takanas saboda kai, Please ko sau ɗaya ka bani lokaci”.
Ba tare da yace mata komai ba ya janye hannunsa ya wuce zuwa bedroom ɗin Mom wondering why yarinyar nan ta ƙara dawowa gare shi. Tun shigowar shi Mom ta tare shi “Kun gaisa da baƙin ne?”
Kai ya gyaɗa yace “Mom, why are they here, ban san su ba” Mom tace “Ban gane ba, baka sansu ba fa kace?”
Cike da ƙosawa yace “Is ok”
Daga haka ya fito, fitowar shi yayi dai-dai da shigowar Sarah daga bedroom ɗin ta.
“Good Evening bro”
“Evening” daga haka ya wuce zai haye stairs ɗin.
Ganin zai wuce yasa Pretty miƙewa da sassarfa tabi bayan shi, babu tsammani taji an riƙe ƙugunta ta baya. Juyawa tayi don ganin waye ke shirin yi mata shamaki da abun son ta.
Cikin sanyin murya Sarah tace “You again?, What brought u here?” ta faɗa tana pointing Pretty. Cikin son danne fushin ta don ita kanta ta fara tabbatar wa cewa Sarah matar Sweetheart ɗin ta ne ko da ganin mahaifiyar Sweetheart ɗin nata tace “Rabu da Ni ba rigima nazo yi ba”
“Then me ya kawo ki?” jin tayi shiru yasa tace “Idan ma saboda shi ne ki sani baki kai ya soki ba, mata masu daraja kaɗai ke samun matsuguni a zuciyar shi, hope I'm clear!”
Cikin jin haushi Pretty ta janye jikin tare da nufi bedroom ɗin da taga Mom ta shiga ɗazu, babu sallama tace
“Mom!” mamaki ya hana Mom ko da amsawa ne sai jin Muryar Pretty tayi tana faɗin
“Mom na zo ne don furta soyayya ta ga ɗan ki Captain, da farko i thought zai yi sauƙi kamar ke but ashe kawai hasashe ne iri nawa, don Allah Mom let him Know that Ina son shi. Gobe zan wuce gida Abuja, amma zan ƙara dawowa”
Daga haka ta fice tare da yiwa su Ishy da ke cikin mamaki da ɗimuwa alamar su fito. Babu shiri suka miƙe suna makawa Sarah harara tare da ficewa.
★★★★★★★★★
*ƳAR IYA POV*
Sana'a Ƴar iya ke yi babu kama hannun yaro, ciniki kuwa sosai baa magana, da zarar kayan sana'ar ya ƙare zata ɗebo ta ƙara busarwa taje gidan Arɗo ta daka abun ta.
Samun da take yi bai hanata yin halin da ta saba ba, gashi bikin A'i sati mai zuwa ne, hakan yasa Ƴar Iya bada himma wurin sana'ar ta, kullum tayi ciniki zata kawowa Halima ta ajiye mata.
Safiyar yau tunda Ƴar Iya ta tashi take jin shiga hancin mutane, hakan yasa ko karyawa batayi ba ta fice sai gidan Inna Zaliha. Inna Zaliha da aka ce wai ciki gare ta abun yayi wa Ƴar Iya daɗi don yadda ta san wannan kwaɗayayyiyar to dole zata ji daɗi musamman da ta tuna duk zuwa gidan da zata yi sai ta tarar da abun daɗi.
Tana isa lokacin Inna Zaliha ta shiga bayi ga kuma tukunya bisa murhu ƙamshi na tashi. A hankali cikin sanɗa ta ƙarasa wajen murhun tana lashe baki.
“Wayyo Ni Ƴar nan, yau akwai burauba, bari na samu na fice kafin mayyar nan ta fito.”
A haka ta ɗaga tukunyar daga kan murhun tare da lallaɓawa ta fice abun ta. Tana kaiwa hanyar waje ta ajiye don ganin menene a ciki. Ido ta zaro tana faɗin
“Shegu ai yau kam mun haɗu, Aradu kun daina ci ku kaɗai”.
Dahuwa ce ta kaza wacce daddawa taji a ciki, ga romon jajir da shi kamar me.
Bata tsaya ɓata lokaci ba ta arta a guje sai gidan Iyar ta.
COMMENT PLEASE
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
__Fictional story of life with full of childhood, entertainment, revenge, betrayal and heart touching love __
SHAFI NA “““43&44”””
_ina Taya ki murna sosai Ameeran Mama (amarya), Allah Ubangiji ya bada zaman lafiya ya sa gidan ki Kenan. Ina godiya da ƙaunar ki sannan ina ƙaunar ki da yawa_
_Shafin nan na baki shi ke kaɗai duk da cewa littafin na Nazari Writers ne amma Ni da kaina nayi kyautar shi😀😏
Inna Zaliha na fitowa daga bayi ta ƙyalla idon ta ga murhun da ta ɗaura dahuwar ta. Ƙwalalo idanuwa waje tayi tare da rufe bakinta da hannu.
“Subhanallahi” ta furta tana juya wa tare da fara ƴan dube dube. Ta shafe kusan mintuna 30 tana dube-duben da take yi gashi fitowarta daga wanka kenan.
Zuciyar ta na wani irin bugu ta shiga bukkar ta tare da ajiye soson buhu da kuma garin omo da tayi wanka da shi. Zanin ta iya ƙirji ta fito tana mai ci gaba da dube-duben nata sai dai babu tukunya babu kuma alamar ta. Hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba musamman da bata ji ko ganin alamar shigowar wani ko wata ba. Ganin dube-duben ba zai fisshe ta ba yasa ta koma bukkar ta tare da zama a bakin gadon karan ta tana jajantawa kanta.
Bata kawo cewa Ƴar masu gidan ce ta ɗauke ba duk tunanin ta Almajirai ne, bayan dawowar Baba da ta sanar masa ya lallashe ta tare da bata haƙuri.
*ƳAR IYA POV*
Tana Isa gida iya ta shige da gudu, bayan ta ajiye tukunyar ta fara ƙwallawa Iyar ƙira kamar wuyan ta zai faɗo
“Iya! Iya!”
Jin shiru yasa ta shiga bukkar ta. Kwance ta sameta tana sharara bacci har abun haushi, ga wani yawun baccin ta a wurin. Tsinke ta zara daga tsintsiyar kwakwa dake gurin, sai da ta saita cinyar iya ta caka mata tsinken tana cije baki.
“Inna lillahi” iya ta faɗa tana miƙewa a zabure, “Na shiga uku meyeh wannan ɗin”
Ƴar dariya Ƴar Iya ta sake tare da faɗin “Aiki na kawo miki, kizo ki ƙarasa dafa mana muci daɗi”
Bayan ta Iya ta bi suka fita, a dai-dai wurin tukunyar ta tsaya tare da nuna mata “Ki juye ki bani na mayar musu”
“Toh” iya ta faɗa tana juyewa cikin wata tukunyar.
Bayan ta juye Ƴar Iya ta ɗauki tukunyar tare da wucewa gidan Inna Zaliha, tana shiga kamar dai ɗazu haka ta lallaɓa ta ajiye tukunyar. Ta juya zata fice murfin tukunyar ya karkace tare da bata sautin ƙarr...ƙurrr.
Da gudu Inna Zaliha ta fito daga cikin bukkar ta don ganin ko an maido mata da dahuwar ta ne. Bata ga kowa ba sai wulgawar mutum, hakan yasa ta ƙaraso da gudu tana buɗe tukunyar sai dai ga mamakin ta babu komai a ciki.
Ihu ta tsala tana faɗin “Na shiga uku ni Zaliha ƴar dahuwar tawa aka sace min!”
Ta share mintuna tana kukan ganin dai babu sarki sai Ubangiji yasa ta janyo tukunyar ta wulla ta wurin wanke-wanke.
*ƳAR IYA POV*
“Ƴan mata ina yinin ku?”
Cikin ƙiƙina suka amsa babu kunya da
“Lafiya Mom,”
Mom! Mom ta ƙara nanata sunan cikin zuciyar ta, “Ikon Allah, wai mom ko wace Mom ɗin rai?” ta faɗa a ranta a fili kuma tayi murmushi tare da faɗin
“Sannun ku da zuwa, sai dai ban gane ku ba fah”
Sumy ce tayi ƙarfin halin faɗin
“Laa Mom yaranki ne ai”
Ishy ta cafke da faɗin
“Mun zo wurin Captain ne Mom”
Mom kam sun ɗaure ta da abun mamaki, ita dai iya sanin ta Son nata baya ma kula mata bare yayi mu'amala da waɗannan masu kama da Ashawos ɗin nan, murmushi kawai tayi tace
“Ku ƙira shi kuce kuna jiran shi parlourn”
Jin hakan yasa fitsararriya Pretty faɗin
“Ji rainin wayo...” bakin ta Ishy tayi saurin rufewa da hannun ta tare da fatan Allah yasa Mom Bata ji ba, sai dai aikin gama ya gama.
Fauzy ce tayi ƙarfin halin faɗin “Ki bar zancen ku da Sulaiman ya wuce mana Pretty, na san shine har yanzu a ranki” daga haka ta kalli Mom dake mamakin Pretty tace “Kiyi haƙuri Mom kada kiyi tunanin dake take, tana da rashin lafiyar maimaita abu idan ya faru da ita, ga bata iya mantuwa”
Murmushi Mom tayi tace “babu komai”
Ganin shiru babu wacce ta ɗago waya ta ƙira Hamma Zaki yasa Mom tace “Ku ƙira shi manah, ni zan wuce ciki”
Cike da duniyanci Ishy ta kaɗa yatsar ta “Wayyo Mom, Kinga saboda saurin da muke na har mun mace wayoyin mu a gida”
“Shikenan bari na wuce, zan ƙira shi”.
Bedroom ɗin ta ta koma tana mai juya maganganun baƙin Hamma Zaki. Bayan ta sanar da shi ta hanyar kiran shi a waya ta faɗa tunanin su waye waɗannan, ko suwaye da gani babu alkhairi a tattare da su, yara sam babu ɗaa bare girmama babba.....
“Hmm to Allah ya kyauta, amma tabbas tana son sanin abu game da su.
Kwance yake yana latsa wayar sa kasancewar bai jima da dawowa daga wurin aikin shi ba. Ya miƙa wayar zai ajiye gefe yaji ringing na wayar. Kamar ba zai yi picking ba ya na tsani tare da ɗagowa, ganin Mom yasa ga zare idanuwa tare da picking.
“Sweetheart...” ba tare da ta barshi ya faɗi me zai ce ba ta katse shi da faɗin
“Kana da baƙi a waje, suna jiran ka a parlour”
“Parlour?” ya faɗa cikin sigar tambaya coz Basu yi da Dr. Faruq zai shigo ba ko wani friend nashi.
“Who Are they Mom?”
“Get down and see” daga haka ta katse ƙiran.
Kamar baya so ya buɗe ƙofa tare da fitowa, shi ba mutum bane mai son gulma ba hakan yasa bai dubo daga can ba. Black jallabiya be jikin shi, kamar koyaushe ƙamshin daddaɗan turaren shi ke tashi. Sam ko kaɗan bai sa a ranshi matan nan ne baƙin shi ba hakan yasa ya miƙe zai je Bedroom ɗin Mom. Cak ya tsaya jin an riƙe hannun shi. A hanzarce ya waiwayo don ganin waye wannan. Dum! Ƙirjin shi ya buga, shi bai yi magana ba sai wani kallo da yake aika mata cikin ranshi kuma yana faɗin (This girl again?”.
Ganin hankalin shi na kanta yasa ta marairaice fuska “Please Sweetheart, no sau ɗaya ka bani damar nan, wallahi ina son ka shi yasa na baro Abuja takanas saboda kai, Please ko sau ɗaya ka bani lokaci”.
Ba tare da yace mata komai ba ya janye hannunsa ya wuce zuwa bedroom ɗin Mom wondering why yarinyar nan ta ƙara dawowa gare shi. Tun shigowar shi Mom ta tare shi “Kun gaisa da baƙin ne?”
Kai ya gyaɗa yace “Mom, why are they here, ban san su ba” Mom tace “Ban gane ba, baka sansu ba fa kace?”
Cike da ƙosawa yace “Is ok”
Daga haka ya fito, fitowar shi yayi dai-dai da shigowar Sarah daga bedroom ɗin ta.
“Good Evening bro”
“Evening” daga haka ya wuce zai haye stairs ɗin.
Ganin zai wuce yasa Pretty miƙewa da sassarfa tabi bayan shi, babu tsammani taji an riƙe ƙugunta ta baya. Juyawa tayi don ganin waye ke shirin yi mata shamaki da abun son ta.
Cikin sanyin murya Sarah tace “You again?, What brought u here?” ta faɗa tana pointing Pretty. Cikin son danne fushin ta don ita kanta ta fara tabbatar wa cewa Sarah matar Sweetheart ɗin ta ne ko da ganin mahaifiyar Sweetheart ɗin nata tace “Rabu da Ni ba rigima nazo yi ba”
“Then me ya kawo ki?” jin tayi shiru yasa tace “Idan ma saboda shi ne ki sani baki kai ya soki ba, mata masu daraja kaɗai ke samun matsuguni a zuciyar shi, hope I'm clear!”
Cikin jin haushi Pretty ta janye jikin tare da nufi bedroom ɗin da taga Mom ta shiga ɗazu, babu sallama tace
“Mom!” mamaki ya hana Mom ko da amsawa ne sai jin Muryar Pretty tayi tana faɗin
“Mom na zo ne don furta soyayya ta ga ɗan ki Captain, da farko i thought zai yi sauƙi kamar ke but ashe kawai hasashe ne iri nawa, don Allah Mom let him Know that Ina son shi. Gobe zan wuce gida Abuja, amma zan ƙara dawowa”
Daga haka ta fice tare da yiwa su Ishy da ke cikin mamaki da ɗimuwa alamar su fito. Babu shiri suka miƙe suna makawa Sarah harara tare da ficewa.
★★★★★★★★★
*ƳAR IYA POV*
Sana'a Ƴar iya ke yi babu kama hannun yaro, ciniki kuwa sosai baa magana, da zarar kayan sana'ar ya ƙare zata ɗebo ta ƙara busarwa taje gidan Arɗo ta daka abun ta.
Samun da take yi bai hanata yin halin da ta saba ba, gashi bikin A'i sati mai zuwa ne, hakan yasa Ƴar Iya bada himma wurin sana'ar ta, kullum tayi ciniki zata kawowa Halima ta ajiye mata.
Safiyar yau tunda Ƴar Iya ta tashi take jin shiga hancin mutane, hakan yasa ko karyawa batayi ba ta fice sai gidan Inna Zaliha. Inna Zaliha da aka ce wai ciki gare ta abun yayi wa Ƴar Iya daɗi don yadda ta san wannan kwaɗayayyiyar to dole zata ji daɗi musamman da ta tuna duk zuwa gidan da zata yi sai ta tarar da abun daɗi.
Tana isa lokacin Inna Zaliha ta shiga bayi ga kuma tukunya bisa murhu ƙamshi na tashi. A hankali cikin sanɗa ta ƙarasa wajen murhun tana lashe baki.
“Wayyo Ni Ƴar nan, yau akwai burauba, bari na samu na fice kafin mayyar nan ta fito.”
A haka ta ɗaga tukunyar daga kan murhun tare da lallaɓawa ta fice abun ta. Tana kaiwa hanyar waje ta ajiye don ganin menene a ciki. Ido ta zaro tana faɗin
“Shegu ai yau kam mun haɗu, Aradu kun daina ci ku kaɗai”.
Dahuwa ce ta kaza wacce daddawa taji a ciki, ga romon jajir da shi kamar me.
Bata tsaya ɓata lokaci ba ta arta a guje sai gidan Iyar ta.
COMMENT PLEASE
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
__Fictional story of life with full of childhood, entertainment, revenge, betrayal and heart touching love __
SHAFI NA “““43&44”””
_ina Taya ki murna sosai Ameeran Mama (amarya), Allah Ubangiji ya bada zaman lafiya ya sa gidan ki Kenan. Ina godiya da ƙaunar ki sannan ina ƙaunar ki da yawa_
_Shafin nan na baki shi ke kaɗai duk da cewa littafin na Nazari Writers ne amma Ni da kaina nayi kyautar shi😀😏
Inna Zaliha na fitowa daga bayi ta ƙyalla idon ta ga murhun da ta ɗaura dahuwar ta. Ƙwalalo idanuwa waje tayi tare da rufe bakinta da hannu.
“Subhanallahi” ta furta tana juya wa tare da fara ƴan dube dube. Ta shafe kusan mintuna 30 tana dube-duben da take yi gashi fitowarta daga wanka kenan.
Zuciyar ta na wani irin bugu ta shiga bukkar ta tare da ajiye soson buhu da kuma garin omo da tayi wanka da shi. Zanin ta iya ƙirji ta fito tana mai ci gaba da dube-duben nata sai dai babu tukunya babu kuma alamar ta. Hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba musamman da bata ji ko ganin alamar shigowar wani ko wata ba. Ganin dube-duben ba zai fisshe ta ba yasa ta koma bukkar ta tare da zama a bakin gadon karan ta tana jajantawa kanta.
Bata kawo cewa Ƴar masu gidan ce ta ɗauke ba duk tunanin ta Almajirai ne, bayan dawowar Baba da ta sanar masa ya lallashe ta tare da bata haƙuri.
*ƳAR IYA POV*
Tana Isa gida iya ta shige da gudu, bayan ta ajiye tukunyar ta fara ƙwallawa Iyar ƙira kamar wuyan ta zai faɗo
“Iya! Iya!”
Jin shiru yasa ta shiga bukkar ta. Kwance ta sameta tana sharara bacci har abun haushi, ga wani yawun baccin ta a wurin. Tsinke ta zara daga tsintsiyar kwakwa dake gurin, sai da ta saita cinyar iya ta caka mata tsinken tana cije baki.
“Inna lillahi” iya ta faɗa tana miƙewa a zabure, “Na shiga uku meyeh wannan ɗin”
Ƴar dariya Ƴar Iya ta sake tare da faɗin “Aiki na kawo miki, kizo ki ƙarasa dafa mana muci daɗi”
Bayan ta Iya ta bi suka fita, a dai-dai wurin tukunyar ta tsaya tare da nuna mata “Ki juye ki bani na mayar musu”
“Toh” iya ta faɗa tana juyewa cikin wata tukunyar.
Bayan ta juye Ƴar Iya ta ɗauki tukunyar tare da wucewa gidan Inna Zaliha, tana shiga kamar dai ɗazu haka ta lallaɓa ta ajiye tukunyar. Ta juya zata fice murfin tukunyar ya karkace tare da bata sautin ƙarr...ƙurrr.
Da gudu Inna Zaliha ta fito daga cikin bukkar ta don ganin ko an maido mata da dahuwar ta ne. Bata ga kowa ba sai wulgawar mutum, hakan yasa ta ƙaraso da gudu tana buɗe tukunyar sai dai ga mamakin ta babu komai a ciki.
Ihu ta tsala tana faɗin “Na shiga uku ni Zaliha ƴar dahuwar tawa aka sace min!”
Ta share mintuna tana kukan ganin dai babu sarki sai Ubangiji yasa ta janyo tukunyar ta wulla ta wurin wanke-wanke.
*ƳAR IYA POV*