Sashe 36
Yar Iya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ashe takwarar Granny CE, Masha Allah. A wane gari kike kuma?”
Cikin burus tace
“A Gallara nake, amma na baro can ɗin ne gabaɗaya saboda ina son birni, ina so nake saka kaya irin nakin nan, nake kwalliya kuma na zama mai matsayi” ta ƙarasa yayin da ƙwalla ke zubo mata.
Cike da tausayawa Nenne tace mata
“Kina son zama da Ni?, Zaki zauna a tare da Ni?”
Kai ta gyaɗa tace “Eh zan zauna”
“Shikenan zaki ke iya ƙira na da Nenne, ina da yara da kuma ƴan uwa sosai. Zamu koma can da zama, amma kimin alƙawarin zaki zauna lafiya da kowa”
“Eh Nenne”
Murmushi Nenne tayi daga nan ta bata labarin hatsarin da suka yi da yadda ya faru. Cikin ƙanƙanin lokaci alaƙa ta ƙullu tsakanin Ƴar Iya da kuma Nenne, Ƴar Iya najin cewa wannan matar ta cancanci zama uwa gare ta tunda yanzu babu Iya.
Ba'a jima ba Doctor yayi discharging nasu. Uncle Suraj Nenne ta ƙira ta sanar dashi, yace su wuce gida kawai. Babu musu suka wuce cikin motar da Nenne tazo da ita.
Tun a bakin Gate Ƴar Iya ta saki baki da hanci tana kallon gidan, cikin ranta tana faɗin “Aradu na huta, na kusa zama ƴar gayu nima”. Bayan sunyi parking Nenne ta fita, sannan ta buɗe side ɗin da Ƴar Iya take tare da janyo hannun ta suka fito. Part ɗin ta ta wuce da ita, lokacin babu kowa su Najma duk suna Islamiyya.
Bayan sun shiga Nenne taja hannun Ƴar Iya tace “Muje ki gyara jikin ki, ranar Saturday sai muje a gyara muku jiki tare da su Najma” ba tare da ta Musa ba tabi Nenne. Toilet ɗin su Najma ta kaita, tare da nuna mata yadda zata yi wankan, ta nuna mata brush da MacLean ta nuna mata yadda zata yi daga nan ta fice. Ita dai mamaki duk ya cika ta wai nan ne bayi?, “To a can ai babu komai kawai kewaye wurin aka yi da zana sai ramin shadda”
Mintuna 30 ta kwashe tana zuba ƙaiyancin ta, thank God ma ita kaɗai ce, Nenne dake zaman jiran fitowar ta taji shiru. Daidai door ɗin ta saka kanta tace
“Baki gama wankan bane?”
Sai lokacin ta tuna wanka fa aka ce tayi, cikin wata irin murya tace
“Nenne bana iya amfani da abubuwan”
“Bari na zo na koya miki”
Nenne da kanta tayi wa Ƴar Iya brush, duk irin damɓare damɓaren dattin da ya fita bai sa haƙwaren fita tas ba, ƙara wanke nata tayi sosai, lokaci guda suka fita kamar ba dai Ƴar Iya ba, har da su mouthfresh aka fesawa Ƴar Iya, ita dai ikon Allah kawai take kallo. Bayan nan Nenne ta sunce towel ɗin da ta ɗaura mata tare da ajiye shi, tas ta wanke Ƴar Iya tana mamakin irin dattin dake jikin ta, gashin kanta kuwa kasa gyara shi tayi tace sai sunje wurin wankin kai.
Bayan sun gama Nenne ta ɗaura nata towel ɗin tare da jan hannun ta zuwa bedroom ɗin ta, tas ta shirya ta, mayuka daban-daban ta shafa mata, powder sannan ta shafa mata wetlips a pinkish leɓen ta.
_Ƴar Iya Fans in kun ganta ba zaku gane ta ba_
Wata doguwar riga Nenne ta saka mata sannan ta saka mata hula. Masha Allah kawai nace tayi kyau kamar ba ita ba.
★★★★★★★★
Motar ce tayi packing a dai-dai parking space. Bayan ta tsaya gabaɗayan su suka fito kowa suka nufi sashen su.
A parlour Fauzah ta tarar da Mom tana aikin nata da ta tsiro na tunani.
Ɗauke da sallama ta shiga sai dai Mom ko sallamar bata ji ba.
A gefenta ta zauna sa'annan ta ɗaura hannun ta a kafaɗar Mom ɗin. Sai a lokacin Mom ta dawo daga duniyar da ta faɗa.
“Mom wai tunanin me kike yi ne haka?, Har fa na shigo baki san na shigo ba” ta faɗa cike da shagwaɓa.
Murmushin da bai kai zuci ba Mom ta sake tare da hugging nata
“Sorry Daughter Ina tunanin Hamman ku ne, gabaɗaya yanzu ya fara mancewa da mu, 2days kenan bai neme Ni ba” ta ƙarasa cikin sigar da ke nuna tsantsar damuwa.
“Kiyi haƙuri Mom kina yiwa Hamma Zaki addu'a, tunanin bashi da amfani.”
Sanyi Mom taji a ranta saboda ƴar maganar da suka yi da Fauzah.
“Oya fresh up muje wurin Granny ko?”
“Toh Mom”
Bayan Fauzah tayi wanka ta biyo bayan Mom, tare suka jera har suka isa part ɗin granny. A can suka tarar da Mommah da Ƴaƴanta ammah Nenne bata nan.
Sai wajajen maghrib suka watse kowa ya wuce, Fauzah ta cewa Mom bari taje wurin Yesmeen ne. Daga nan Mom ta wuce zuwa part ɗin ta.
A nan suka yi salla, bayan sunyi suka kafa dandalin hirar su wanda duk sun kafa ta ne a kan Shagalin da zasu yi a JSSCE nasu.
Har aka yi Ishã suna can sai da suka yi Najmah ta ƙira su suzo suyi dinner.
Idon su ne ya sauƙa kan Ƴar Iya da ta make a ƙasa tana harba lomar dambun couscous da ke gaban ta yayin da idon Nenne ke akanta tana sakin murmushi. Mamaki da kuma tsoro ne suka dira cikin zukatan su lokaci guda su basu ƙaraso ba kuma basu koma ba, ita kuwa wacce suke abun a kanta bata ma san da su ba.
Har ta gama cinyewa Allah bai basu ikon koda kuwa motsawa ba. Tana cinyewa ta ɗago da kanta, sai a lokacin idonta ya sauƙa kan kyawawan Ƴanmatan da ke tsaye suna kallon ta, lokaci ɗaya ta fahimci kallon tsoro suke mata. Murmushi ta sake sai da dimple nata ya bayyana. Kallon ta ta mayar kan Nenne da ke aiko mata da murmushi.
“Nenne na cinye,”
Nenne tace
“Ti kice alhamdulillah”
Ɓata fuskar tayi ƙasa-ƙasa tace
“Alhamdudillah”
Dariyar su Najma ne ta sa ta dawo da duban ta gare su, sai kuma ta marairaice fuska tana kallon Nenne.
Harara Nenne ta aika musu tana faɗin
“Kar ku saka min yarinya a gaba, ku bani waje in ba zaku ci abincin ba”
Wani iri suka ji hakan yasa suka ƙarasa a sukwane zuwa dining ɗin suka zuba abinci suka fara ci.
Ƴar Iya ta dubi Nenne tace
“Nenne ku dukan ku masu kyau ne, waɗannan Ƴan gayun su ma ƴaƴan ki ne?”
Murmushi Nenne tayi tace “Bari su gama ci sai na faɗa miki su waye ne”
Kai kawai ta gyaɗa taci gaba da kallon ƙauyen ta a parlourn.
TO FAH, ƳAR IYA A NAIRA FAMILY, KO YA KUKE TUNANIN WASAN ZAI KAYA? KUCI GABA DA BIBIYAR ALƘALAMIN DIAMOND BHATOOL DOMIN JIN YADDA ZATA KAYA.
MUCH LOVE MY ESTEEM FANS
COMMENT & SHARE FISABILILLAH!
[8/17, 6:17 PM] 𝙳𝚒𝚊𝚖𝚘𝚗𝚍_𝙱𝚑𝚊𝚝𝚘𝚘𝚕💎:
🌸🍀🌸🍀🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
SHAFI NA “““61&62”””
_Afwan masoya bayan wani dogon zango In Sha Allah yau na ɗaura alƙalami na kuma bana jin zan sauƙe sai na kammala muku wannan littafi, COMMENTS ɗin ku kawai nake so, ku taya ni SHARING kowanne update ta haka zan ƙara tabbatar da ƙaunar ku gare ni, Ina son ku irin loadi-loadin nan_💃🤩❤️
Bayan Najmah sun kammala cin abincin su, duka suka kwaso jiki suka dawo parlour, bisa lallausan carpet ďin dake shifide a parlourn suka zube tare da maida hankulan su kan Yar Iya da kuma Nenne.
Cikin karfin hali Najmah tace
“Nenne ina kika samo wannan?”
Harara Nenne ta jefa mata kafin tace
“To uwar tambaye-tambaye ban sani ba”
Marairaice fuska tayi tana faɗin
“I'm sorry Nenne an, kawai ta bani dariya ne, kiga fa yadda take cin abinci” ta faɗa cikin sigar zolaya. Ayrah da bata ce komai ba tunda suka dawo parlourn ta kece da wata irin dariya
“Kai Adda Najma, itama fa mutum ce”
Ran Nenne ne ya fara ɓaci da tsiyar da suke tsulawa hakan yasa ta daka musu tsawa “Is ok, bana son sakarcin banza, ku baku iya mutunta ɗan Adam bane?” ta jefa musu tambayar da ta saka lokaci ɗaya jikin su yayi sanyi. Cigaba da magana Nenne tayi
“Ahalinku sun san ƙimar mutane saboda haka bana son na ƙara gani ko jin makamancin abinda kuka yi yanzu not only to her but to anyone, ok?”
Gyaɗa Kai su duka suka yi yayin da Najma tace “Kiyi haƙuri Nennen mu ba zamu ƙara ba”.
Murmushi tayi musu sannan ta ɗora da
“Ban san ko a nan A'isha zata zauna ba, idan zamanta a nan ɗin ya tabbata ku shirya ɗaukar ta matsayin ƴar uwar ku. Kun gane”
“Eh Nenne” suka bata amsa. Daga haka bata ƙara ce da su uffan ba ta mayar da duban ta zuwa ga A'isha. Bata ga alamun rashin jin daɗin abinda suka yi mata a fuskar ta ba amma sai da ta bata haƙuri a kan hakan.
Cike da mamaki nake duba A'isha da tayi murmushi tace
“Babu komai Nenne, nima Iya ta da kuma Baffi na suna yawan cewa na koyi haƙuri saboda bani da shi kuma ban sanshi ba, amma yau sai naji na fara shi”
Dariya kaɗan Nenne tayi tace “Ai kuwa Iya sun kyauta, haƙuri yana da kyau sosai cikin rayuwa” kai ta gyaɗa alamar gamsuwa yayin da Nenne ke ƙara nazartar A'isha. Ɓoyayyiyar ajiyar zuciya ta sauƙe jin takun mai gidan uncle Suraj na shigowa.
Bata yi ƙoƙarin sauƙe A'isha da kanta ke bisa cinyarta ba, sai ma ƙoƙarin gyara ma kanta zama da tayi. Cikin fara'a ya ƙaraso ganin A'isha a tare da Nenne duk da dama ya tsammaci hakan, coz Nenne akwai son jama'a.
Sallamar ta amsa mishi tare da sannu da zuwa, ba tare da ya damu ba shima ya wuce ya watsa ruwa. Lokacin Nenne ta raka A'isha bedroom ɗin Hamma Zaki na ƙofar in yaso in taji matsayar zamanta sai ta maida ta ɗakin su Ayrah.
Cikin burus tace
“A Gallara nake, amma na baro can ɗin ne gabaɗaya saboda ina son birni, ina so nake saka kaya irin nakin nan, nake kwalliya kuma na zama mai matsayi” ta ƙarasa yayin da ƙwalla ke zubo mata.
Cike da tausayawa Nenne tace mata
“Kina son zama da Ni?, Zaki zauna a tare da Ni?”
Kai ta gyaɗa tace “Eh zan zauna”
“Shikenan zaki ke iya ƙira na da Nenne, ina da yara da kuma ƴan uwa sosai. Zamu koma can da zama, amma kimin alƙawarin zaki zauna lafiya da kowa”
“Eh Nenne”
Murmushi Nenne tayi daga nan ta bata labarin hatsarin da suka yi da yadda ya faru. Cikin ƙanƙanin lokaci alaƙa ta ƙullu tsakanin Ƴar Iya da kuma Nenne, Ƴar Iya najin cewa wannan matar ta cancanci zama uwa gare ta tunda yanzu babu Iya.
Ba'a jima ba Doctor yayi discharging nasu. Uncle Suraj Nenne ta ƙira ta sanar dashi, yace su wuce gida kawai. Babu musu suka wuce cikin motar da Nenne tazo da ita.
Tun a bakin Gate Ƴar Iya ta saki baki da hanci tana kallon gidan, cikin ranta tana faɗin “Aradu na huta, na kusa zama ƴar gayu nima”. Bayan sunyi parking Nenne ta fita, sannan ta buɗe side ɗin da Ƴar Iya take tare da janyo hannun ta suka fito. Part ɗin ta ta wuce da ita, lokacin babu kowa su Najma duk suna Islamiyya.
Bayan sun shiga Nenne taja hannun Ƴar Iya tace “Muje ki gyara jikin ki, ranar Saturday sai muje a gyara muku jiki tare da su Najma” ba tare da ta Musa ba tabi Nenne. Toilet ɗin su Najma ta kaita, tare da nuna mata yadda zata yi wankan, ta nuna mata brush da MacLean ta nuna mata yadda zata yi daga nan ta fice. Ita dai mamaki duk ya cika ta wai nan ne bayi?, “To a can ai babu komai kawai kewaye wurin aka yi da zana sai ramin shadda”
Mintuna 30 ta kwashe tana zuba ƙaiyancin ta, thank God ma ita kaɗai ce, Nenne dake zaman jiran fitowar ta taji shiru. Daidai door ɗin ta saka kanta tace
“Baki gama wankan bane?”
Sai lokacin ta tuna wanka fa aka ce tayi, cikin wata irin murya tace
“Nenne bana iya amfani da abubuwan”
“Bari na zo na koya miki”
Nenne da kanta tayi wa Ƴar Iya brush, duk irin damɓare damɓaren dattin da ya fita bai sa haƙwaren fita tas ba, ƙara wanke nata tayi sosai, lokaci guda suka fita kamar ba dai Ƴar Iya ba, har da su mouthfresh aka fesawa Ƴar Iya, ita dai ikon Allah kawai take kallo. Bayan nan Nenne ta sunce towel ɗin da ta ɗaura mata tare da ajiye shi, tas ta wanke Ƴar Iya tana mamakin irin dattin dake jikin ta, gashin kanta kuwa kasa gyara shi tayi tace sai sunje wurin wankin kai.
Bayan sun gama Nenne ta ɗaura nata towel ɗin tare da jan hannun ta zuwa bedroom ɗin ta, tas ta shirya ta, mayuka daban-daban ta shafa mata, powder sannan ta shafa mata wetlips a pinkish leɓen ta.
_Ƴar Iya Fans in kun ganta ba zaku gane ta ba_
Wata doguwar riga Nenne ta saka mata sannan ta saka mata hula. Masha Allah kawai nace tayi kyau kamar ba ita ba.
★★★★★★★★
Motar ce tayi packing a dai-dai parking space. Bayan ta tsaya gabaɗayan su suka fito kowa suka nufi sashen su.
A parlour Fauzah ta tarar da Mom tana aikin nata da ta tsiro na tunani.
Ɗauke da sallama ta shiga sai dai Mom ko sallamar bata ji ba.
A gefenta ta zauna sa'annan ta ɗaura hannun ta a kafaɗar Mom ɗin. Sai a lokacin Mom ta dawo daga duniyar da ta faɗa.
“Mom wai tunanin me kike yi ne haka?, Har fa na shigo baki san na shigo ba” ta faɗa cike da shagwaɓa.
Murmushin da bai kai zuci ba Mom ta sake tare da hugging nata
“Sorry Daughter Ina tunanin Hamman ku ne, gabaɗaya yanzu ya fara mancewa da mu, 2days kenan bai neme Ni ba” ta ƙarasa cikin sigar da ke nuna tsantsar damuwa.
“Kiyi haƙuri Mom kina yiwa Hamma Zaki addu'a, tunanin bashi da amfani.”
Sanyi Mom taji a ranta saboda ƴar maganar da suka yi da Fauzah.
“Oya fresh up muje wurin Granny ko?”
“Toh Mom”
Bayan Fauzah tayi wanka ta biyo bayan Mom, tare suka jera har suka isa part ɗin granny. A can suka tarar da Mommah da Ƴaƴanta ammah Nenne bata nan.
Sai wajajen maghrib suka watse kowa ya wuce, Fauzah ta cewa Mom bari taje wurin Yesmeen ne. Daga nan Mom ta wuce zuwa part ɗin ta.
A nan suka yi salla, bayan sunyi suka kafa dandalin hirar su wanda duk sun kafa ta ne a kan Shagalin da zasu yi a JSSCE nasu.
Har aka yi Ishã suna can sai da suka yi Najmah ta ƙira su suzo suyi dinner.
Idon su ne ya sauƙa kan Ƴar Iya da ta make a ƙasa tana harba lomar dambun couscous da ke gaban ta yayin da idon Nenne ke akanta tana sakin murmushi. Mamaki da kuma tsoro ne suka dira cikin zukatan su lokaci guda su basu ƙaraso ba kuma basu koma ba, ita kuwa wacce suke abun a kanta bata ma san da su ba.
Har ta gama cinyewa Allah bai basu ikon koda kuwa motsawa ba. Tana cinyewa ta ɗago da kanta, sai a lokacin idonta ya sauƙa kan kyawawan Ƴanmatan da ke tsaye suna kallon ta, lokaci ɗaya ta fahimci kallon tsoro suke mata. Murmushi ta sake sai da dimple nata ya bayyana. Kallon ta ta mayar kan Nenne da ke aiko mata da murmushi.
“Nenne na cinye,”
Nenne tace
“Ti kice alhamdulillah”
Ɓata fuskar tayi ƙasa-ƙasa tace
“Alhamdudillah”
Dariyar su Najma ne ta sa ta dawo da duban ta gare su, sai kuma ta marairaice fuska tana kallon Nenne.
Harara Nenne ta aika musu tana faɗin
“Kar ku saka min yarinya a gaba, ku bani waje in ba zaku ci abincin ba”
Wani iri suka ji hakan yasa suka ƙarasa a sukwane zuwa dining ɗin suka zuba abinci suka fara ci.
Ƴar Iya ta dubi Nenne tace
“Nenne ku dukan ku masu kyau ne, waɗannan Ƴan gayun su ma ƴaƴan ki ne?”
Murmushi Nenne tayi tace “Bari su gama ci sai na faɗa miki su waye ne”
Kai kawai ta gyaɗa taci gaba da kallon ƙauyen ta a parlourn.
TO FAH, ƳAR IYA A NAIRA FAMILY, KO YA KUKE TUNANIN WASAN ZAI KAYA? KUCI GABA DA BIBIYAR ALƘALAMIN DIAMOND BHATOOL DOMIN JIN YADDA ZATA KAYA.
MUCH LOVE MY ESTEEM FANS
COMMENT & SHARE FISABILILLAH!
[8/17, 6:17 PM] 𝙳𝚒𝚊𝚖𝚘𝚗𝚍_𝙱𝚑𝚊𝚝𝚘𝚘𝚕💎:
🌸🍀🌸🍀🍀🌸🍀🌸 🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
*ƳAR IYA* *(Mai hannun ɓarna)*
🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀🌸🍀
_NA_
*Fadimatu Adamu Hassan*
*Diamond Lady 💎*
SHAFI NA “““61&62”””
_Afwan masoya bayan wani dogon zango In Sha Allah yau na ɗaura alƙalami na kuma bana jin zan sauƙe sai na kammala muku wannan littafi, COMMENTS ɗin ku kawai nake so, ku taya ni SHARING kowanne update ta haka zan ƙara tabbatar da ƙaunar ku gare ni, Ina son ku irin loadi-loadin nan_💃🤩❤️
Bayan Najmah sun kammala cin abincin su, duka suka kwaso jiki suka dawo parlour, bisa lallausan carpet ďin dake shifide a parlourn suka zube tare da maida hankulan su kan Yar Iya da kuma Nenne.
Cikin karfin hali Najmah tace
“Nenne ina kika samo wannan?”
Harara Nenne ta jefa mata kafin tace
“To uwar tambaye-tambaye ban sani ba”
Marairaice fuska tayi tana faɗin
“I'm sorry Nenne an, kawai ta bani dariya ne, kiga fa yadda take cin abinci” ta faɗa cikin sigar zolaya. Ayrah da bata ce komai ba tunda suka dawo parlourn ta kece da wata irin dariya
“Kai Adda Najma, itama fa mutum ce”
Ran Nenne ne ya fara ɓaci da tsiyar da suke tsulawa hakan yasa ta daka musu tsawa “Is ok, bana son sakarcin banza, ku baku iya mutunta ɗan Adam bane?” ta jefa musu tambayar da ta saka lokaci ɗaya jikin su yayi sanyi. Cigaba da magana Nenne tayi
“Ahalinku sun san ƙimar mutane saboda haka bana son na ƙara gani ko jin makamancin abinda kuka yi yanzu not only to her but to anyone, ok?”
Gyaɗa Kai su duka suka yi yayin da Najma tace “Kiyi haƙuri Nennen mu ba zamu ƙara ba”.
Murmushi tayi musu sannan ta ɗora da
“Ban san ko a nan A'isha zata zauna ba, idan zamanta a nan ɗin ya tabbata ku shirya ɗaukar ta matsayin ƴar uwar ku. Kun gane”
“Eh Nenne” suka bata amsa. Daga haka bata ƙara ce da su uffan ba ta mayar da duban ta zuwa ga A'isha. Bata ga alamun rashin jin daɗin abinda suka yi mata a fuskar ta ba amma sai da ta bata haƙuri a kan hakan.
Cike da mamaki nake duba A'isha da tayi murmushi tace
“Babu komai Nenne, nima Iya ta da kuma Baffi na suna yawan cewa na koyi haƙuri saboda bani da shi kuma ban sanshi ba, amma yau sai naji na fara shi”
Dariya kaɗan Nenne tayi tace “Ai kuwa Iya sun kyauta, haƙuri yana da kyau sosai cikin rayuwa” kai ta gyaɗa alamar gamsuwa yayin da Nenne ke ƙara nazartar A'isha. Ɓoyayyiyar ajiyar zuciya ta sauƙe jin takun mai gidan uncle Suraj na shigowa.
Bata yi ƙoƙarin sauƙe A'isha da kanta ke bisa cinyarta ba, sai ma ƙoƙarin gyara ma kanta zama da tayi. Cikin fara'a ya ƙaraso ganin A'isha a tare da Nenne duk da dama ya tsammaci hakan, coz Nenne akwai son jama'a.
Sallamar ta amsa mishi tare da sannu da zuwa, ba tare da ya damu ba shima ya wuce ya watsa ruwa. Lokacin Nenne ta raka A'isha bedroom ɗin Hamma Zaki na ƙofar in yaso in taji matsayar zamanta sai ta maida ta ɗakin su Ayrah.