← Book details Shaquwace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 65

Sashe 23

Shaquwace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikeda kissa taci gaba da fad'in "Eh dama jibi ne zata tafi idan Allah Ya kaimu...... " Shema'u bata kai aya ba suka jiyo muryar Hajiya tana doka sallama..

Ai daga ita har AT mik'ewa sukayi zunbur suka nufo downstairs...

Hajiya sai huci take tana k'walla ma Hajiya Kulu kira tana fad'in ta fito....

AT ya k'araso da sauri yana tambayar Hajiya lafiya meke faruwa?..

Shek'ek'e Hajiya ta dubesa ta kuma duban Shema'u dake take masa baya kafin tace "Uwar matarka da wancan mai suffan karuwan nake so su bar gidan nan yanzun nan bada b'ata lokaci ba..."

Kuka Shema'u ta fashe dashi ta durk'usa gaban Hajiya tana fad'in "Haba Hajiya, meyasa kika tsaneni haka, meyasa kike jifata da munan kalamai, karuwa fah Hajiya, ko me na maki ban cancanci ki kirani karuwa ba balle babu abinda nayi, burina shine faranta ran yaran 'yar uwata da ta tafi ta bari idan baku gode min ba kwabini da mugayen kalamai ba..." Hajiya ta Saki baki tana kallon salon makirci...

Shi kuwa AT tausayin Shema'u ne ya rufesa, duk sai yaji babu dad'i, d'awainiyar da Shema'u keyi da yaransa yasa shi bata wani matsayi cikin zuciyar sa, don bazai tab'a mance wannan babban halarci data masa ba shida yaransa..

Saida Hajiya ta daka masa tsawa tana fad'in "Nace ka sallami Kulu da d'iyarta yanzun nan ko kuma kaga b'acin raina... Yara sunada masu rik'esu... Ta juya tana kallon Shema'u dake goge hawaye da bakin mayafinta kana tace "Bari ma kiji na shaida maki Attahiru uwa ta gari zai kawo masu cikin satin nan......"

AT tamkar gunki haka yake duban Hajiya.... Dai-dai lokacin da Momma ta fito daga corridor d'in da zai sadaka da d'akin bak'i.... "Lafiya nike jin hayaniya haka na tashi..?" cewar Momma bayan ta k'arasa shigowa cikin parlorn sai wani pankan-pankan take.... Saida ta murmusa kafin ta dubi Hajiya tace "Hajiya Fad'ime mun wuni lafiya, da fatan b'arauniyar yarinyar can bata tab'a yasheki ba..." Ai batakai aya ba Hajiya ta k'araso gabanta sosai tana fad'in "Ke Kulu wllhi kinyi kad'an bokanki yayi kad'an, kece jinin tsiya amma Maryama kam tafi k'arfin ta d'au wani abu naki, ban mata wannan tarbiyar ba kuma zaman Juwaira daram a gidan nan ke baki isa ki rabata da yaran nan ba, SHAK'UWAR da Allah Ya riga ya had'a yafi k'arfin d'an mutum, nan gani nan bari, sannan abu na k'arshe shine awa guda bazaki sake yi cikin gidan nan ba, tunda shi Attahirun bakida gadonsa... Banda asara kin tattaro kin tare gidan surkin ki ke ko kunya bakiji, wllhi kinji jiki kuma kinji kunya....."

Shewa Momma tayi kafin tace " Ko baki nemi na tafi ba zan tafi tunda na raba jikokina da wancan alak'ak'ai d'in, masu gadon tsiya marassa asali balle tushe...."

AT ya dafe kansa yana karanto innalillahi.... Duban Shema'u dake faman share hawayen k'arya yayi murya can k'asa yace "Pls take Momma to her room." Da sauri Shema'u ta gyad'a masa kai kafin ta shiga janye Momma suka nufi d'aki. Allah yasa sauk'in abin yaran sun tafi islamiya.

Hajiya bata daina balbala masifa ba tana fad'in "Wllhi Kulu sai kin bar gidan nan."

"Hajiya don girman Allah kiyi shiru haka nan, don Allah kiyi hak'uri." AT ya katse ta da fad'in haka kafin ya nemi waje saman carpet ya zauna.

Har lokacin dai bata daina huci ba, saman kujera ta zauna kafin ta dubesa da kyau tace "Attahiru, ka bud'e kunnuwanka da kyau ka saurari abinda zan fad'a maka. Ka zauna mata sai juyaka suke, inyi, waini yaushe ka zama lusari haka ne, toh wllhi idan kai asirin Kulu yayi tasiri akan ka ni baiyi ba, wllhi bata isa ba..."

AT ya shafi goshinsa kafin yace "Hajiya please enough of this, give me break please..."

Hannu ta d'aga masa alamun katsewa kafin tace "Um um karma ka soma min turancinkan nan da baka tashi yi sai ranka ya b'aci... Kaji na rantse maka ka gama zama babu mata, wllhi aure zakayi, bazan zauna inaji ina gani Kulu da d'iyarta su shanyeka ba ehe.." Ta k'arashe tana gyara zaman mayafinta.

Tashin hankali wanda ba'a saka masa rana, tabbas AT ya shiga tsaka mai wuya..... Gaba d'aya ya nemi kalma guda saman harshensa ya rasa, gaba d'aya kansa na neman kwacewa, abubuwa sun cakud'e a kwanyar sa... Bai ankara ba sai ganin Hajiya yayi ta mik'e tana gyara mayafinta kafin ta dubesa tace "Kadaiji abinda na fad'i maka Jumma'a mai zuwa d'aurin auren ka, ya rage maka ka samo matar cikin satin nan, idan baka samu ba ni zan sama maka..." Daga haka ta suri posanta dake ajiye saman sofa tayi ficewarta cikin sauri....

Tamkar wanda aka dasa haka yayi zaune a wajen.

Shema'u da Momma dake lab'e a corridor kallon juna sukayi, tuni idanun Shema'u sun firfito waje, duk iya shegenta tana mugun shakkan Hajiya, amma tabbas Hajiya ta kawota iya wuya, tana gab da salwantar da rayuwar ta...

Kallon Momma tayi tana girgiza kai tamkar tab'ebb'iya take fad'in "Momma aure zata masa, wllhi jarabebbiyar nan aure zata masa, Momma we need to do something bazan iya barin yaran 'yar uwata hannun kishiya ba, Momma pls we need to save your grandchildren,...." Gaba d'aya tamkar ta zare lokaci guda.

Hannun Momma tasa da sauri ta toshe bakin Shema'u don kar a iya jiyota... A hankali cikin rad'a ta soma fad'in "Ki dubesa yanda yayi zaune, this your best chance, he really needs company, yana buk'atan wanda zai masa magana yaji sanyi, kar kiyi wasa da wannan damar, kinga dai ni tafiya zanyi, and dole na tabbata na barki akan yaran nan for good, kinsan sune farin ciki na... Shema'u na yarda dake I know you can do it, pls don't fail me... Oya kintsa kanki ki k'arasa garesa..." Ta shiga goge ma Shema'u hawayen ta tana gyara mata fuskarta, ita kuwa Shema'u sai gyad'a kai take tana zazzare idanu tamkar mai tab'in hankali...

A hankali ta soma takowa cikin parlorn...

Har ta zauna ta d'an gabansa baiyi noticing ba, gaba d'aya hankalin sa bai tareda shi.... Muryar Shema'u ya jiyo cikeda kissa tana fad'in "Damuwa bai cancanceka ba sannan bai kamace ka, kayi hak'uri sannan ka sani sam babu laifin Hajiya ko k'ank'ani, wannan duk laifin Momma ce, at times idan Momma tayi wani abin nakanji mamaki sosai, amma idan na tuna girma ya soma sauk'o mata sai na mata uzuri, shakka babu Hajiya ma harda girma a abubuwan da takeyi, AT kayi hak'uri, ka k'ara akan wanda kake Allah yana son masu hak'uri sannan sukeda nasara a rayuwa, watarana komai zai wuce ya zama sai labari... Sannan if you need someone to talk to kar ka mance that I'll be right here kaji..."

D'ago kai yayi yana dubanta sosai, she sounds like Aysha, tabbas kalamanta sun d'anyi calming nasa... Bai iya ce mata komai ba sai gyad'a kai da yayi ya mik'e ya nufi sama. Shema'u ta bisa da kallo tana wata kafiran murmushi... Jim kad'an ya sauk'o da makullan motar sa..
Yasa kai zai fice daga parlorn Shema'u tayi saurin bin bayansa har tura k'ofar ya fice ya jiyo muryar ta tanai masa a dawo lafiya had'i da addu'an Allah Ya tsare....

Juyowa yayi ya dubeta kafin ya d'an murmusa yace "Na gode" a tak'aice.. Daga haka yayi saurin sa kai ya fice...

Bayansa tabi da kallo tana mai cikeda jin dad'i ganin sam baya gwaleta, ita kad'ai ta dinga murmushi tana sak'a abubuwa da dama cikin zuciyar ta....

Iya Kande ta k'araso ta sameta nan tsaye tana washe baki take fad'in "Kai Hajiyan sake hannu, ina mai tabbatar maki keda Datta ba k'aramin dacewa zakuyi ba, dukanku farare sol-sol wanke hannu ka tab'a...."

Shema'u tayi murmushin wanda yafi kama dana rainin hankali kafin ta dubi Iya Kande tace "Kande bari na tuna maki don kar ki mance,."

Iya Kande tayi saurin gyad'a kai alamun toh.

Shema'u ta murmusa tana dafa kafad'an Iya Kande kafin tace "Ba'a cin amanata idan na aminta da mutum don haka ki kiyaye..." Ta k'arashe maganar tana mai bud'e tafin hannun Iya Kande ta dunk'ula mata 'yan dubu-dubu guda uku..

Haba nan fah Iya Kande ta washe baki ta shiga kod'a Shema'u.....

***************

Hisham I'm lost, I'm completely lost... I...i just don't know what to do anymore.. Wllhi bansan yaya zanyi da Hajiya ba bansan me zan fad'a mata ta fahimce ni ba.." Ya k'arashe zancen yana hura iska a bakinsa.

Mik'ewa Hisham yayi daga saman sofan da yake zaune akai ya dawo gefen AT kafin ya dafa kafad'ansa yace "Tahir, you better take things easy, don't stress yourself, kabi komai a sannu, abokina nasanka nasan yanayin ka, wllhi nasha mamaki da naga ka zauna baka k'ara aure ba tun bayan mutuwar matarka tunda nasan kai ba bin matan banza kake ba, don I can still remember sanda muke sch azumi bai wuceka... Baka biye mana.." Ya k'arashe yana murmusawa.

Gajeren tsaki AT yayi kafin yace "Tuzuru banza kak'i aure kak'i canza hali... Wllhi Hisham kaji tsoron kamuwar Allah. Ni bama wannan bane a gabana, I can hold myself, yarana sune min gaba da komai ka gane." Ya k'arashe maganar yana lank'washe 'yan yatsun hannunsa.

"Okay fine naji, your children are your top priority, amma Tahir kayi auren mana kaman yanda Hajiya ta buk'ata, yin auren sai kaga ya kawo maka kwanciyar hankali da iyalanka, all this tashin hankula-hankula da kuke shiga sai kaga Allah Ya sauwak'e maka albarkacin auren."

AT yayi shiru yana sauraren sa yana nazarin maganganun nasa, fuzar da iska ya kumayi ya shafi goshinsa kafin ya had'e tafukan hannayen sa waje guda yana mai duban Hisham yake fad'in "Toh Hisham wa zan aura for goodness sake, you're fully aware of banida macen da nake so a halin yanzu, and you know what the worse part is... Waifa Hajiya cewa take zata samomin matar, kaifa kaji saikace k'aramin yaro a shekarunan nan, yo banda abun Hajiya ko Rano taje ta samesu da batun zata min aure ai dariya zasu mata, kaman wani matashin saurayi..." Ya k'arashe yana girgiza kai.
Chapter 23 · 0% Book details