Sashe 96
Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
Ahankali mb da sauran abokansu suka shigo falon ATA kowannensu sanye da farin yadi mai shegen tsada ,basu ganshi ba dan haka mb ya tura kofar bedroom dinsa anan ya gansa kwance a kasa shame shame tamkar matace ,da wani irin sauri ya qarasa inda yake kwance ya durkusa a gabansa yana cewa" Kai adam ka tashi mana lokacin zuwa daurin aure yayi fa "ya fad'a yana kallon kofar shigowa dakin "kai yasir kuzo ku ganshi ya qara shan giya ya bugu fiyye da jiya ya sake kallon fuskar ATA yana shafa fuskarsa ," kai wai meye haka ne ?subuhallah ya bugu kuma? inji cewar salim da yasir da suka shigo atare cikin tsananin tashin hankali."
" kamo shi mb yayi yana cewa "ku taimaka min mu daga shi gbdy suka kamo shi zuwa kan bed dinsa suka kwantar dashi suka dinga jijiga shi" ka tashi dan girman allah lokacin daurin aurenka yayi ,amman shiru kake jin ATA dan ko motsi baya yi numfashi ma da kyar yake fitarwa yasir ya kai hannu ya bude idanunshi yana kiran sunansa," kai ku duba fa kugani kwayar idanunshi sun dauke inna lillahi wa inna ilaihi rajiun kai abokina ka bude idanunka muna tare da kai dan allah karka min haka bana son na rasaka ."mb ya fad'a cikin tsananin tashin hankali mara iyaka .
"kana jina abokina ka bude idanunka yana magana yana jijiga shi amman har lokacin ATA bai motsa ba bai ma san a halin da yake ciki ba duk yadda sukayi su tashesa amman abun yaki cikin tashin hankali mb yake kallonsa gabansa na faduwa acikin kwana biyu kacal da soma shirye shiryen biki ya zare ya fita haiyacinsa bai ta'ba tsamanin zai shiga wannan halin ba da shi karon kashi ya shawarci mami a hakura da auren kawai kowa ya huta ."
sosai mb yaji babu dadi ganin halin da amininsa yake ciki da sauri mb ya nufi kofar fita daga dakin kunnensa manne da waya yana cewa "hello sadiq kana ina ? "dan girman Allah ka ..ka taimaka min ATA nan ya zayyane masa komai cikin tashin hankali eh kazo da allurar please ya katse kiran ya koma cikin dakin har lokacin kwayar idanunshi bai dawo daidai ba ko dan sambatun nan na bugaggu bai yi ba ."
suna tsaye sadiq ya shigo ya fara dubasa "yana da rai numfashinsa ne yayi nisa sakamakon buguwar da yayi amman zan masa allura nan da wasu yan awanni zai dawo daidai ya ciro sirinji daga cikin bakar jakar daya shigo dashi ya hada duk allurar zaiyi masa bayan yayi masa ne suka fito daga cikin dakin dukkaninsu jikinsu a sanyaye inda zuciyar mb Ke bugawa da karfi kamar wasu kurame haka suka sauko babu ango, ganin mami yasa duk suka dan saki fuska dan karta gane akwai abinda yake faruwa sai dai kallo daya tayi masu ta fahimci akwai matsala tun kafin su kai ga fita ta nufi hanyar dakinsa ."
Tana shiga dakin yana kwance a buge Kmr jiya ta tsura masa ido bata ko liftawa ga wani tashin hankali data tsinci kanta ciki wanda bata ta'ba jin irinsa ba ,bta ta'ba nadama da danasani ba sai a safiyar yau din nan ,gabadaya jikinta ya dauki rawa kasa dauke idanunta tayi akanshi wadan da tuni sun rikice suna qoqarin zubar da hawaye cikin wani irin salo na yan shaye shaye taji yana kiran sunan "my princess kece rayuwata kece duniyata kinki bayyana min kanki saboda baki sona laifin me nayi miki ?yadda yayi maganar da sunan da yake ta faman kira ba qaramin rudar da mami yayi ba ,da sauri ta fito daga cikin dakin tana goge hawayen nadama da danasani sam sam bata ga laifinsa ko jin haushinsa ba domin itace sila jefa rayuwarsa cikin wannan halin ."
mutane masu mahimanci suna zaune acikin massalaci dake cikin estate din abdullahi auren Adam Tariq abdullahi aka fara daurawa tare da maryam abdulra'uf akan sadaki kankani bisa umarnin mami sannan aka daura na hisham Muhammad sani tare da nana hauwa'u tariq abdullahi duk yadda hisham yake son yayi jarumta amman a karshe sai da kwalla ta zubo masa jin an daura aurensa da wata ba da nuzlarsa ba .wani irin bakinciki ne mara misaltuwa ya lullube zuciyar hisham hannunsa salim ya rike cikin cool voice yace "ka sausautawa kanka sannan ka sanya aranka daman can nuzla ba matarka bace ."
Ana gama daurin aure maroka suka fara shela acikin mutane hamdala mami tayi alokacin daakce mata an daura auren sai dai zuciyarta bata cikin jin dadi sannan bakinta bai daina ambaton sunan Allah ba maryam kam fadawa tayi jikin aunty khadija tana fashewa da kuka mai karfi "aunty khadija ta soma rarrashinta kukan murna da kukan bakinciki maryam take bakincikinta yaya adam baya sonta na farinciki kuma burinta ya cika ta auri abun qaunarta ."hajiya zulfa'u ta kira salim cewar suzo da hisham bangaren hjy zulai suka shigo a tare da abokan ango hisham ko kallon inda nana hauwa'u take bai yi ba nan masu daukar hoto dake biye dasu suka shiga aikinsu anyi hotuna sosai ."
Da misalin karfe biyu na rana mami ta shiga dakin ATA tare da mrym yana kwnace adduoi ta dinga yi tana shafa masa a fuskarsa yayinda maryam ta qaraso ta kafeshi da ido tana kallonsa tana jin wutar sonshi na qaruwa acikin zuciyarta qoqarin mikewa yake nan mami ta kama masa ya tashi ta jingina masa pillow a bayansa kallonsu kawai ya tsaya yi kafin ya rufe idanunshi yana sauke ajiyar zuciya "adamcy nah yau ka zama cikakken mutun ina cikin farinciki an daura aurenka da maryam sannna ina cikin bakinciki irin halin daka jefa kanka ciki ta qarasa mgnr tana kuka ".
"meye kuma abun kuka bayan burinki ya cika ?ya fad'a yana goge mata hawaye "kukan murna da bakinciki ne , yau ina cikin farinciki da bakinciki ka taimaki rayuwar mahaifiyarka karka canza daga adamcy data sani ,rayuwa qaddara ce sannan kai muslim ne ka yarda da qaddara kayi farinciki da auren nan ka barwa allah komai "numfashi ya sauke baya jin zai yi wani farinciki da wannna auren maryam kam idanunta na kanshi har sai da taji sautin muryar mami ta doki dodon kunneta "maryam jeki hado masa tea ki kawo masa ta fice daga dakin."
Bayan fitarta da kyar mami tasa shi ya tashi ya shiga yayi brush da wanka sabbin kayansa ya saka lokacin da mami ke fesa masa turare maryam ta turo kofar dakin ta shigo mami ta karfi cup din hannunta da kanta ta dinga bashi a baki tana masa nasiha ita kam mrym duk hankalinta na kanshi sai faman kallonsa take shi kanshi mamakin irin kallon da take masa yayi wanda kallo ne mai dauke da tsantsar soyayya acikin lokaci kankani...."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 30
Ahankali ya d'auke kwayar idanunshi zuwa wani bangaren dabam yana jan tsaki dan bazai iya cigaba da kallonta ba "me yasa sweetheart take masa haka ?tasan baya son ganin yarinyar atare dashi amman ita burinta bai wuce taga sun kasance a waje d'aya ba."
"dan Allah adamcy ka cire damuwar nan aranka ka kwantar min da hankali ahalin yanzu babu abinda nake buqata kamar natsuwarka da kwanciyar hankalinka ,duk duniya babu wanda zai so maka kwanciyar hankali da farinciki kamar ni mahaifiyar ka saboda nice nafi kowa sanin ciwonka ."
"daga ni har kai da duk wani mai qaunarka babu wanda zai so ka qarasa rayuwarka haka batare da ka ajiye iyali ba , sannan zamanka kai kad'ai illa ne ga rayuwarka, idan wasu sun yarda da kai akan baka aikata komai na sa'bo ,wasu bazasu yarda ba, wasu zasu d'aukeka a matsayin mai neman mata ne duba da irin tarin dukiyar da allah yayi maka ,dan haka kayi hakuri ka rungume wannan rayuwar domin itace qaddararka dan adam bai isa ya canzawa kanshi qaddararsa ba."
sosai ya fad'a cikin kogin tunani hankalinsa ya bar duniyar da yake wanda hakan ya bawa maryam damar cigaba da kallonsa son ranta tana jin tmkr ta fad'a jikinsa ta rungumeshi ta rarrashi kayanta ,jin saukar hannun mami jikinsa ya sanyashi dawowa cikin natsuwarsa ya d'ago kanshi ya zuba mata idanunshi dake cike da matsanancin damuwa ."
"Ina neman alfarmar a wajenka a karo na biyu " wata irin razana yayi yayinda zuciyarsa ta soma bugawa da karfi kamar zai fasa qirjinsa domin bai san wace irin alfarma zata sake nema a wajensa ba ,bai ce mata komai ba ya cigaba da kallonta da tsumammun idanunshi yana mai allah allah yaji abinda zata fad'a."
"na gode maka da alfarmar da kayi min na farko na amincewa auren maryam da kayi alfarmar ta biyu ka taimakeni adamcy kayi min alkwarin bazaka sake kai kwalbar giya bakinka ba bare sigari " tayi maganar Kmr zata zubar da hawaye dan tuni kwayar idanunta sun canza kala ."
Wani naunayen ajiyar zuciya da numfashi ya sauke atare dan bai d'auka abinda zai fito daga bakinta ba kenan, ya d'auka zatayi masa magana ne akan tarewar yarinyar "kayi dan Allah dani amadadin giyar da zaka yita sha kana buguwa gara ka rike addua adamcy ,jikinsa yayi sanyi da jin maganarta ya risinar da kanshi kasa batare daya bude bakinsa ba a ransa yace "wannan rayuwarta ce ,ciwona ne ".
ta cigaba da kallonsa shi kuwa bai ce mata uffan ba dan baya son yayi mata aqawarin da bazai cika ba ,bugu da qari baya son a shiga rayuwarsa a barshi da damuwarsa kawai sannan abar shi ya sha giyarsa da sigarinsa son ransa domin a halin da yake ciki su kad'ai ne abinda suke rage masa rad'ad'in damuwarsa ."
" kamo shi mb yayi yana cewa "ku taimaka min mu daga shi gbdy suka kamo shi zuwa kan bed dinsa suka kwantar dashi suka dinga jijiga shi" ka tashi dan girman allah lokacin daurin aurenka yayi ,amman shiru kake jin ATA dan ko motsi baya yi numfashi ma da kyar yake fitarwa yasir ya kai hannu ya bude idanunshi yana kiran sunansa," kai ku duba fa kugani kwayar idanunshi sun dauke inna lillahi wa inna ilaihi rajiun kai abokina ka bude idanunka muna tare da kai dan allah karka min haka bana son na rasaka ."mb ya fad'a cikin tsananin tashin hankali mara iyaka .
"kana jina abokina ka bude idanunka yana magana yana jijiga shi amman har lokacin ATA bai motsa ba bai ma san a halin da yake ciki ba duk yadda sukayi su tashesa amman abun yaki cikin tashin hankali mb yake kallonsa gabansa na faduwa acikin kwana biyu kacal da soma shirye shiryen biki ya zare ya fita haiyacinsa bai ta'ba tsamanin zai shiga wannan halin ba da shi karon kashi ya shawarci mami a hakura da auren kawai kowa ya huta ."
sosai mb yaji babu dadi ganin halin da amininsa yake ciki da sauri mb ya nufi kofar fita daga dakin kunnensa manne da waya yana cewa "hello sadiq kana ina ? "dan girman Allah ka ..ka taimaka min ATA nan ya zayyane masa komai cikin tashin hankali eh kazo da allurar please ya katse kiran ya koma cikin dakin har lokacin kwayar idanunshi bai dawo daidai ba ko dan sambatun nan na bugaggu bai yi ba ."
suna tsaye sadiq ya shigo ya fara dubasa "yana da rai numfashinsa ne yayi nisa sakamakon buguwar da yayi amman zan masa allura nan da wasu yan awanni zai dawo daidai ya ciro sirinji daga cikin bakar jakar daya shigo dashi ya hada duk allurar zaiyi masa bayan yayi masa ne suka fito daga cikin dakin dukkaninsu jikinsu a sanyaye inda zuciyar mb Ke bugawa da karfi kamar wasu kurame haka suka sauko babu ango, ganin mami yasa duk suka dan saki fuska dan karta gane akwai abinda yake faruwa sai dai kallo daya tayi masu ta fahimci akwai matsala tun kafin su kai ga fita ta nufi hanyar dakinsa ."
Tana shiga dakin yana kwance a buge Kmr jiya ta tsura masa ido bata ko liftawa ga wani tashin hankali data tsinci kanta ciki wanda bata ta'ba jin irinsa ba ,bta ta'ba nadama da danasani ba sai a safiyar yau din nan ,gabadaya jikinta ya dauki rawa kasa dauke idanunta tayi akanshi wadan da tuni sun rikice suna qoqarin zubar da hawaye cikin wani irin salo na yan shaye shaye taji yana kiran sunan "my princess kece rayuwata kece duniyata kinki bayyana min kanki saboda baki sona laifin me nayi miki ?yadda yayi maganar da sunan da yake ta faman kira ba qaramin rudar da mami yayi ba ,da sauri ta fito daga cikin dakin tana goge hawayen nadama da danasani sam sam bata ga laifinsa ko jin haushinsa ba domin itace sila jefa rayuwarsa cikin wannan halin ."
mutane masu mahimanci suna zaune acikin massalaci dake cikin estate din abdullahi auren Adam Tariq abdullahi aka fara daurawa tare da maryam abdulra'uf akan sadaki kankani bisa umarnin mami sannan aka daura na hisham Muhammad sani tare da nana hauwa'u tariq abdullahi duk yadda hisham yake son yayi jarumta amman a karshe sai da kwalla ta zubo masa jin an daura aurensa da wata ba da nuzlarsa ba .wani irin bakinciki ne mara misaltuwa ya lullube zuciyar hisham hannunsa salim ya rike cikin cool voice yace "ka sausautawa kanka sannan ka sanya aranka daman can nuzla ba matarka bace ."
Ana gama daurin aure maroka suka fara shela acikin mutane hamdala mami tayi alokacin daakce mata an daura auren sai dai zuciyarta bata cikin jin dadi sannan bakinta bai daina ambaton sunan Allah ba maryam kam fadawa tayi jikin aunty khadija tana fashewa da kuka mai karfi "aunty khadija ta soma rarrashinta kukan murna da kukan bakinciki maryam take bakincikinta yaya adam baya sonta na farinciki kuma burinta ya cika ta auri abun qaunarta ."hajiya zulfa'u ta kira salim cewar suzo da hisham bangaren hjy zulai suka shigo a tare da abokan ango hisham ko kallon inda nana hauwa'u take bai yi ba nan masu daukar hoto dake biye dasu suka shiga aikinsu anyi hotuna sosai ."
Da misalin karfe biyu na rana mami ta shiga dakin ATA tare da mrym yana kwnace adduoi ta dinga yi tana shafa masa a fuskarsa yayinda maryam ta qaraso ta kafeshi da ido tana kallonsa tana jin wutar sonshi na qaruwa acikin zuciyarta qoqarin mikewa yake nan mami ta kama masa ya tashi ta jingina masa pillow a bayansa kallonsu kawai ya tsaya yi kafin ya rufe idanunshi yana sauke ajiyar zuciya "adamcy nah yau ka zama cikakken mutun ina cikin farinciki an daura aurenka da maryam sannna ina cikin bakinciki irin halin daka jefa kanka ciki ta qarasa mgnr tana kuka ".
"meye kuma abun kuka bayan burinki ya cika ?ya fad'a yana goge mata hawaye "kukan murna da bakinciki ne , yau ina cikin farinciki da bakinciki ka taimaki rayuwar mahaifiyarka karka canza daga adamcy data sani ,rayuwa qaddara ce sannan kai muslim ne ka yarda da qaddara kayi farinciki da auren nan ka barwa allah komai "numfashi ya sauke baya jin zai yi wani farinciki da wannna auren maryam kam idanunta na kanshi har sai da taji sautin muryar mami ta doki dodon kunneta "maryam jeki hado masa tea ki kawo masa ta fice daga dakin."
Bayan fitarta da kyar mami tasa shi ya tashi ya shiga yayi brush da wanka sabbin kayansa ya saka lokacin da mami ke fesa masa turare maryam ta turo kofar dakin ta shigo mami ta karfi cup din hannunta da kanta ta dinga bashi a baki tana masa nasiha ita kam mrym duk hankalinta na kanshi sai faman kallonsa take shi kanshi mamakin irin kallon da take masa yayi wanda kallo ne mai dauke da tsantsar soyayya acikin lokaci kankani...."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 30
Ahankali ya d'auke kwayar idanunshi zuwa wani bangaren dabam yana jan tsaki dan bazai iya cigaba da kallonta ba "me yasa sweetheart take masa haka ?tasan baya son ganin yarinyar atare dashi amman ita burinta bai wuce taga sun kasance a waje d'aya ba."
"dan Allah adamcy ka cire damuwar nan aranka ka kwantar min da hankali ahalin yanzu babu abinda nake buqata kamar natsuwarka da kwanciyar hankalinka ,duk duniya babu wanda zai so maka kwanciyar hankali da farinciki kamar ni mahaifiyar ka saboda nice nafi kowa sanin ciwonka ."
"daga ni har kai da duk wani mai qaunarka babu wanda zai so ka qarasa rayuwarka haka batare da ka ajiye iyali ba , sannan zamanka kai kad'ai illa ne ga rayuwarka, idan wasu sun yarda da kai akan baka aikata komai na sa'bo ,wasu bazasu yarda ba, wasu zasu d'aukeka a matsayin mai neman mata ne duba da irin tarin dukiyar da allah yayi maka ,dan haka kayi hakuri ka rungume wannan rayuwar domin itace qaddararka dan adam bai isa ya canzawa kanshi qaddararsa ba."
sosai ya fad'a cikin kogin tunani hankalinsa ya bar duniyar da yake wanda hakan ya bawa maryam damar cigaba da kallonsa son ranta tana jin tmkr ta fad'a jikinsa ta rungumeshi ta rarrashi kayanta ,jin saukar hannun mami jikinsa ya sanyashi dawowa cikin natsuwarsa ya d'ago kanshi ya zuba mata idanunshi dake cike da matsanancin damuwa ."
"Ina neman alfarmar a wajenka a karo na biyu " wata irin razana yayi yayinda zuciyarsa ta soma bugawa da karfi kamar zai fasa qirjinsa domin bai san wace irin alfarma zata sake nema a wajensa ba ,bai ce mata komai ba ya cigaba da kallonta da tsumammun idanunshi yana mai allah allah yaji abinda zata fad'a."
"na gode maka da alfarmar da kayi min na farko na amincewa auren maryam da kayi alfarmar ta biyu ka taimakeni adamcy kayi min alkwarin bazaka sake kai kwalbar giya bakinka ba bare sigari " tayi maganar Kmr zata zubar da hawaye dan tuni kwayar idanunta sun canza kala ."
Wani naunayen ajiyar zuciya da numfashi ya sauke atare dan bai d'auka abinda zai fito daga bakinta ba kenan, ya d'auka zatayi masa magana ne akan tarewar yarinyar "kayi dan Allah dani amadadin giyar da zaka yita sha kana buguwa gara ka rike addua adamcy ,jikinsa yayi sanyi da jin maganarta ya risinar da kanshi kasa batare daya bude bakinsa ba a ransa yace "wannan rayuwarta ce ,ciwona ne ".
ta cigaba da kallonsa shi kuwa bai ce mata uffan ba dan baya son yayi mata aqawarin da bazai cika ba ,bugu da qari baya son a shiga rayuwarsa a barshi da damuwarsa kawai sannan abar shi ya sha giyarsa da sigarinsa son ransa domin a halin da yake ciki su kad'ai ne abinda suke rage masa rad'ad'in damuwarsa ."