Sashe 62
Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
Ta riko hannunsa hawaye na zuba daga idanunta ta soma tafiya dashi taku d'aya biyu yayi ya tsaya cak , itama ta tsaya suna fuskantar hisham naunaye ajiyar zuciya ta sauke tana goge hawayen dake tsiyaya ,ahankali ata ya zare hannunsa dake cikin nata ya yarfar sannna ya zura cikin aljihun wondonsa yana jan tsaki "ya hisham! ta kira sunansa a kid'eme "banyi niyyar fito da sirrin dake zuciyata ba amamn ya zama dole na fad'a maka tunda na fad'awa yaya adam babu komai acikin zuciyata sai..." karki kuskura kiyi wannan ganganci dan kome zaki yi tawa zuciyar bazata amince ba "to kuwa gara ka ksheni da hannunka na huta dan nima bazan iya auren yaya hisham ba , yana sona ni kuma kai nake so.."you're very stupid Kiyi maza ki danna madannin gogewa ki gogeni arayuwarki da zuciyarki dan ni mallakin mafarkina ce " yana gama fad'ar haka ya juya ya haye sama yana taka step yana magana " hisham ka manta da shirmen wannan yarinyar ka soma naka shirin domin wannan auren ko zata mutu sai anyisa useless girl kawai ga inda ake sonku aka damu daku amman ku dinga kai kanku inda bazaa ta'ba sonku ba nonsense "
Hisham ya runtse idanuwanshi "kenan hasashensa ya tabbata , zarginsa ya zama gasky kenan akan ata yake shan wulakanci da tsana da wahala a wajenta ? ,"ya kalleta cike da tausayawa yace "daman ata Kike so ?jikinta yayi mugu mugun sanyi ta rasa me zata cewa hisham illa ta runtse idanunta gam tana jin zafi da ciwo mara iyaka a zuciyarta ,ta durkushe qasa tana kuka tana nemawar kanta mafuta dan dole tasan abun yi kafin a had'ata aure da hisham shima ya durkushe gabanta ya dago ha'barta ya sanya kwayar idanunshi cikin nata , tai saurin buge masa hannu tana kallonsa cike da tsantsar tsana "ka kyaleni ni wallahi bana sonka tunda burinka kenan na soka , dan girman allah ka rabu dani ka manta dani, ka manta da maganar ka ta'ba sona arayuwarka , ka mantani ta qarasa fad'ar haka tana fidda huci mai zafi ."
"Dan allah kiyi hakuri nasan irin ciwo da zafin da Kike ji acikin zuciyarki ciwo ne kwatankwacin wanda nake ji acikin zuciyata nasan zafin ciwo da radadin kana son wani baya sonka ,wallahi na tausaya miki amman me yasa nuzla ?"me yasa sai ata zuciyarki zata kamu da so byn ni ina qaunarki ya kai hannunsa yana share mata hawaye"ata bashi da wannan lokacin wahalar da kanki da zuciyarki kawai zakiyi babu wannan tausayin a zuciyarsa a karshe ya rungumeta ajikinsa tsam yana shafa bayanta ahankali ahankali babu yadda ta iya dole ta kasance rungume ajikinsa domin tana bukatar wanda zai rarrasheta kuka take sosai tana rungume ajikinsa "ki daina kuka nuzla dan zuciyata bazata iya ganin hawayenki da damuwarki ina matukar sonki da zaki bani dama da sannu zaki daina son ata ki soni ya fad'a yana qara rungumeta gam ajikinsa ahankali ya mike tsaye tare daita ya nufi kofar fita tun kafin mutane su shigo su fahimci halin da suke ciki ."
Washegarin da misalin karfe tara na dare ata ya shiga d'akin mami sanye cikin fararen kayan bacci wondo da riga , hannunsa rike da black cup dinsa dake dauke da ruwan coffee ,yayinda dayan hannunsa Ke cikin aljihun wondonsa ya samu mami tsaye a gaban wordrobe dinta tana qoqarin rufewa tana ganinsa ta sakar masa murmushi tana cewa "Masha allah adamcy nan ya karfin jikin ?alhamd sweetheart ya qoqari dani ?kwana nawa ya saura ai Allah Allah nike Kayi tafiyar nan ka dawo mu sha biki ranar bani da dama zan aurar da d'a daya tilo ya girgiza kai kawai yana ajiye cup din hannunsa akan bedside dinta ya tsura mata tsumammun idanunshi yana kallonta tmkr wani maraya "yaakayi adamcy nan duk sanda kayi haka akwai abinda kake son fad'a "haka ne sweetheart kin fi kowa sanin halina alfarma nazo nema ."
"Alfarmar kuma ?mami ta maimaita abinda ya fad'a
"Eh ina neman wata alfamar a wajenki sweetheart "ina sauroronka Allah yasa zan iya ,ya marairaice murya sosai kafin ya soma mgn "dan darajan Allah sweetheart ki qara min lokacin auren nan wallahi wallahi wallahi !!! kinji na rantse miki zan auri yarinyar nan zabinki , wasu yan kwanakin kawai zaki qara min har naje na dawo dan zan dauki lokaci a france daga nan ma zan wuce hollond yi wasu abubuwa masu mahimanci a yanzu na samu sauyin lokaci amman kuma idan kina ganin zaa iya yin komai ko bana nan fine na amince a daura auren ayi komai amman da zaa bari na dawo sai nafi farinciki kasancewar ina son a hada auren dana hisham da nuzla yadda take kallonsa ya fahimci kamar bata yarda dashi ba "na rantse fa duk wanda aka rantse wa bai yarda ba shi din bana allah bane nayi miki wannan alqawarin sweetheart zan aureta ".
"naji amman har zuwa wani lokaci ni wallahi zaka sani jin kunya auren sauran kwanaki ace an daga "karki damu sweetheart idan akwai damuwa kawai ayi ko bana nan amman na fi son ina nan ,sai kace wata tsiyar zaka kulla ko kana ?ya dan ciza gefen lips dinsa "bansani ba ko zan iya kulla wani abu a auren da bana só ?kaji dashi tunani tayi karta je a daura yaki dawowa ya bar yar mutane da nauyi akanta gara kawai ta qara masa lokaci idan ya dawo sai ayi"Kwanaki nawa zan qara maka ?uhm ko Kmr wata biyu haka yayi "what ! kai adamcy ban yarda da kai ba ,wallahi ki yarda dani sweetheart bazan baki kunya ba, ba kuma zan saba alkwari ba I promise you ,ka cika alqawari adamcy ,karki damu sweetheart na ranse fa ,shikenan na yarda da kai ta fad'a kafin su fad'a hirar duniya a nan yake bata labarin nuzla murmshi mami tayi tana cewa "adamcy nah mai farinjini ."
Zaune mr ata yake agaban hajiya zulaiheart sanye cikin suit wondo da riga bakake jikinsa na fitar da wani kamshi na daga hankali fuskar nan nashi dake kwance da kasumba tayi fresh tayi kyau tana fitar da wani haske na dabam mai daukar hankali abun ka ga fari mutun sallama ya shigo mata dan sauran awa daya jirgnsa ya daga zuwa kasar france "Allah kiyayya ya tsare min kai , ka kular min da kanka sosai banda wasa da abinci aci abinci akan lokaci kamar yadda doctor ya fada "in sha allahu zan kiyaye sweetheart. Allah ya qara girma,ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani kema ki kular min da kanki "Ameen summa ameen nayi maka wannan alkwarin Allah yayi muku albarka gabadaya ku "inji mami ,sannan taja musu addu'a suka shafa tana shafa masa na hannunta a fuskarshi ."a tare suka mike suka fito inda tawagarsa Ke jiransa a haraban gidan shi kadai ne zaune a bayan motarsa limozin sai driver a mazauninshi, hawaye ya tsiyayowa mami sanda motocinsa suke qoqarin barin gidan sai take jin kamar kar ya tafi amman kamar yau ne zai dawo gareta wannan karan mami ta kasa daurewa sai da tayi qwalla, gefe tayi da kanta tana dauke hawayenta ."
*****
Yau tsawon kwana uku kenan mlm yahuza yana zariyar zuwa gidansu maryama amman kamar kullum bai samu ganinta ba yau ma daga massalaci ya wuto kofar gidansu yana neman yaron da zai aika cikin gidansu ko cikakken minti goma bai yi da tsayuwa ba, sai ga yaya sadam ya fito daga cikin gidan , nan ya mika masa hannu suka gaisa "ina fatan dai lafiya kwana biyu nan kake zuwa gidan nan ?"Lafiya lau wajen maryama nake zuwa sai dai duk zuwan da nake yi bana samun ganinta ,shine dan naci kake ta zuwa ?to ya zanyi sadam tunda zuciyata ta kamu da matsanancin sonta duk da bani da tabbacin ko tana sona amman nasan tana son fitowa inda nake habib ke hanata fitowa yanzu dai taimaka min ka fito min daita dan nasan muddin habib na cikin gidan bazai barta ta fito ba ,murmushi sadam yayi yana cewa "kai habib hukuma ne wannan yaron bari ina zuwa !ya juya ya koma cikin gidan ya shiga side dinsu maryama ."
a parlour ya iskesu gabadaya suna hirar duniya ya zauna yana fuskantar maryama suka gaisa da aunty sannan maryama ta gaishesa haka ma habib ya amsa masu da "lafiya lau cikin sakin fuska ,ya gida da aiki sadam ?Alhamdulillah aunty mun godewa Allah yace yana duban maryama "ga malamin ku yahuza can a kofar gida yana jiranki yau tsawon kwana uku kenan ina ganinsa ashe wai saboda ke yake zuwa amman bakya fitowa."wata irin kunya ta kama maryama ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da zara zaran yatsun hannunta".
"ai ga d'an albarka dake hanata fita nan , ko shi zai aureta bansani ba ?yaro qarami dashi sai aikin nuna isa da iko ita kuma shegen son dan'uwa tana biye masa aunty ta qarashe maganar tana zabgawa habib harara ,habib bai ce komai ba ya tashi ya shige ciki dan matsawar yana zaune a falon bazai iya barin maryama ta fita zuwa koina ba km hakan zai sa yaya sadam yaji babu dadi "ai yahuza mutumin kirki ne kuma ga dukkanin alamun da gaske yake aunty tace "allah yasa shi wai habib dan matsalar daake ta samu akan masu zuwa suna tafiya né yake jin haushi "nima na fahimci haka amman in sha allahu komai yazo karshe dan nasan yahuza bazai mata haka ba nima gsky na yaba da hankalinsa maza tashi kije maryama karki dade maryama bata ji dadi ba ganin habib ya tashi ya barsu km tasan duk akan mgnr fita ne ,amman babu yadda ta iya yaya sadam da aunty suna da karfin iko arayuwarta ta mike ta fita ta bar aunty da yaya sadam suna magana bata san abinda ya cigaba da wakana atsakaninsu ba ."
Hisham ya runtse idanuwanshi "kenan hasashensa ya tabbata , zarginsa ya zama gasky kenan akan ata yake shan wulakanci da tsana da wahala a wajenta ? ,"ya kalleta cike da tausayawa yace "daman ata Kike so ?jikinta yayi mugu mugun sanyi ta rasa me zata cewa hisham illa ta runtse idanunta gam tana jin zafi da ciwo mara iyaka a zuciyarta ,ta durkushe qasa tana kuka tana nemawar kanta mafuta dan dole tasan abun yi kafin a had'ata aure da hisham shima ya durkushe gabanta ya dago ha'barta ya sanya kwayar idanunshi cikin nata , tai saurin buge masa hannu tana kallonsa cike da tsantsar tsana "ka kyaleni ni wallahi bana sonka tunda burinka kenan na soka , dan girman allah ka rabu dani ka manta dani, ka manta da maganar ka ta'ba sona arayuwarka , ka mantani ta qarasa fad'ar haka tana fidda huci mai zafi ."
"Dan allah kiyi hakuri nasan irin ciwo da zafin da Kike ji acikin zuciyarki ciwo ne kwatankwacin wanda nake ji acikin zuciyata nasan zafin ciwo da radadin kana son wani baya sonka ,wallahi na tausaya miki amman me yasa nuzla ?"me yasa sai ata zuciyarki zata kamu da so byn ni ina qaunarki ya kai hannunsa yana share mata hawaye"ata bashi da wannan lokacin wahalar da kanki da zuciyarki kawai zakiyi babu wannan tausayin a zuciyarsa a karshe ya rungumeta ajikinsa tsam yana shafa bayanta ahankali ahankali babu yadda ta iya dole ta kasance rungume ajikinsa domin tana bukatar wanda zai rarrasheta kuka take sosai tana rungume ajikinsa "ki daina kuka nuzla dan zuciyata bazata iya ganin hawayenki da damuwarki ina matukar sonki da zaki bani dama da sannu zaki daina son ata ki soni ya fad'a yana qara rungumeta gam ajikinsa ahankali ya mike tsaye tare daita ya nufi kofar fita tun kafin mutane su shigo su fahimci halin da suke ciki ."
Washegarin da misalin karfe tara na dare ata ya shiga d'akin mami sanye cikin fararen kayan bacci wondo da riga , hannunsa rike da black cup dinsa dake dauke da ruwan coffee ,yayinda dayan hannunsa Ke cikin aljihun wondonsa ya samu mami tsaye a gaban wordrobe dinta tana qoqarin rufewa tana ganinsa ta sakar masa murmushi tana cewa "Masha allah adamcy nan ya karfin jikin ?alhamd sweetheart ya qoqari dani ?kwana nawa ya saura ai Allah Allah nike Kayi tafiyar nan ka dawo mu sha biki ranar bani da dama zan aurar da d'a daya tilo ya girgiza kai kawai yana ajiye cup din hannunsa akan bedside dinta ya tsura mata tsumammun idanunshi yana kallonta tmkr wani maraya "yaakayi adamcy nan duk sanda kayi haka akwai abinda kake son fad'a "haka ne sweetheart kin fi kowa sanin halina alfarma nazo nema ."
"Alfarmar kuma ?mami ta maimaita abinda ya fad'a
"Eh ina neman wata alfamar a wajenki sweetheart "ina sauroronka Allah yasa zan iya ,ya marairaice murya sosai kafin ya soma mgn "dan darajan Allah sweetheart ki qara min lokacin auren nan wallahi wallahi wallahi !!! kinji na rantse miki zan auri yarinyar nan zabinki , wasu yan kwanakin kawai zaki qara min har naje na dawo dan zan dauki lokaci a france daga nan ma zan wuce hollond yi wasu abubuwa masu mahimanci a yanzu na samu sauyin lokaci amman kuma idan kina ganin zaa iya yin komai ko bana nan fine na amince a daura auren ayi komai amman da zaa bari na dawo sai nafi farinciki kasancewar ina son a hada auren dana hisham da nuzla yadda take kallonsa ya fahimci kamar bata yarda dashi ba "na rantse fa duk wanda aka rantse wa bai yarda ba shi din bana allah bane nayi miki wannan alqawarin sweetheart zan aureta ".
"naji amman har zuwa wani lokaci ni wallahi zaka sani jin kunya auren sauran kwanaki ace an daga "karki damu sweetheart idan akwai damuwa kawai ayi ko bana nan amman na fi son ina nan ,sai kace wata tsiyar zaka kulla ko kana ?ya dan ciza gefen lips dinsa "bansani ba ko zan iya kulla wani abu a auren da bana só ?kaji dashi tunani tayi karta je a daura yaki dawowa ya bar yar mutane da nauyi akanta gara kawai ta qara masa lokaci idan ya dawo sai ayi"Kwanaki nawa zan qara maka ?uhm ko Kmr wata biyu haka yayi "what ! kai adamcy ban yarda da kai ba ,wallahi ki yarda dani sweetheart bazan baki kunya ba, ba kuma zan saba alkwari ba I promise you ,ka cika alqawari adamcy ,karki damu sweetheart na ranse fa ,shikenan na yarda da kai ta fad'a kafin su fad'a hirar duniya a nan yake bata labarin nuzla murmshi mami tayi tana cewa "adamcy nah mai farinjini ."
Zaune mr ata yake agaban hajiya zulaiheart sanye cikin suit wondo da riga bakake jikinsa na fitar da wani kamshi na daga hankali fuskar nan nashi dake kwance da kasumba tayi fresh tayi kyau tana fitar da wani haske na dabam mai daukar hankali abun ka ga fari mutun sallama ya shigo mata dan sauran awa daya jirgnsa ya daga zuwa kasar france "Allah kiyayya ya tsare min kai , ka kular min da kanka sosai banda wasa da abinci aci abinci akan lokaci kamar yadda doctor ya fada "in sha allahu zan kiyaye sweetheart. Allah ya qara girma,ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani kema ki kular min da kanki "Ameen summa ameen nayi maka wannan alkwarin Allah yayi muku albarka gabadaya ku "inji mami ,sannan taja musu addu'a suka shafa tana shafa masa na hannunta a fuskarshi ."a tare suka mike suka fito inda tawagarsa Ke jiransa a haraban gidan shi kadai ne zaune a bayan motarsa limozin sai driver a mazauninshi, hawaye ya tsiyayowa mami sanda motocinsa suke qoqarin barin gidan sai take jin kamar kar ya tafi amman kamar yau ne zai dawo gareta wannan karan mami ta kasa daurewa sai da tayi qwalla, gefe tayi da kanta tana dauke hawayenta ."
*****
Yau tsawon kwana uku kenan mlm yahuza yana zariyar zuwa gidansu maryama amman kamar kullum bai samu ganinta ba yau ma daga massalaci ya wuto kofar gidansu yana neman yaron da zai aika cikin gidansu ko cikakken minti goma bai yi da tsayuwa ba, sai ga yaya sadam ya fito daga cikin gidan , nan ya mika masa hannu suka gaisa "ina fatan dai lafiya kwana biyu nan kake zuwa gidan nan ?"Lafiya lau wajen maryama nake zuwa sai dai duk zuwan da nake yi bana samun ganinta ,shine dan naci kake ta zuwa ?to ya zanyi sadam tunda zuciyata ta kamu da matsanancin sonta duk da bani da tabbacin ko tana sona amman nasan tana son fitowa inda nake habib ke hanata fitowa yanzu dai taimaka min ka fito min daita dan nasan muddin habib na cikin gidan bazai barta ta fito ba ,murmushi sadam yayi yana cewa "kai habib hukuma ne wannan yaron bari ina zuwa !ya juya ya koma cikin gidan ya shiga side dinsu maryama ."
a parlour ya iskesu gabadaya suna hirar duniya ya zauna yana fuskantar maryama suka gaisa da aunty sannan maryama ta gaishesa haka ma habib ya amsa masu da "lafiya lau cikin sakin fuska ,ya gida da aiki sadam ?Alhamdulillah aunty mun godewa Allah yace yana duban maryama "ga malamin ku yahuza can a kofar gida yana jiranki yau tsawon kwana uku kenan ina ganinsa ashe wai saboda ke yake zuwa amman bakya fitowa."wata irin kunya ta kama maryama ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da zara zaran yatsun hannunta".
"ai ga d'an albarka dake hanata fita nan , ko shi zai aureta bansani ba ?yaro qarami dashi sai aikin nuna isa da iko ita kuma shegen son dan'uwa tana biye masa aunty ta qarashe maganar tana zabgawa habib harara ,habib bai ce komai ba ya tashi ya shige ciki dan matsawar yana zaune a falon bazai iya barin maryama ta fita zuwa koina ba km hakan zai sa yaya sadam yaji babu dadi "ai yahuza mutumin kirki ne kuma ga dukkanin alamun da gaske yake aunty tace "allah yasa shi wai habib dan matsalar daake ta samu akan masu zuwa suna tafiya né yake jin haushi "nima na fahimci haka amman in sha allahu komai yazo karshe dan nasan yahuza bazai mata haka ba nima gsky na yaba da hankalinsa maza tashi kije maryama karki dade maryama bata ji dadi ba ganin habib ya tashi ya barsu km tasan duk akan mgnr fita ne ,amman babu yadda ta iya yaya sadam da aunty suna da karfin iko arayuwarta ta mike ta fita ta bar aunty da yaya sadam suna magana bata san abinda ya cigaba da wakana atsakaninsu ba ."