← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 35 OF 100

Sashe 35

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Baba babba ya tsaya abayansa hankalinsa a matukar tashe  " maganarka gaskiya yayanmu suka fi dacewa da aurensa   sai dai kayi hakuri dan'uwana bana tunanin da wata manufa zulaiheart ta had'a  wannan auren   ,idan baka manta ba  shekara nawa ana fama da yaron nan akan ya fitar da mata yayi aure  bana  tunanin zata ki had'a  zuria da daya daga cikinmu  sannan da kasan kana da wannan burin me yasa baka fito dashi ba ?

Baba qarami bai ce uffan ba illa numfashi da yake sauke da sauri sauri gumi na karyo masa  "dan   haka kayi hakuri karka bari wannan matsalar ta zamo Silar da za'a samu matsala ka bar  wannan burin  bayan anyi wannan auren sai ayi maganar a had'ashi da daya daga cikin yaran".
"Kai kare idan ka sake yin min  wannan maganar  banzar sai  na datseka gbdy Komai naka   banga ta yadda nawa burin zai zama daga baya ba muddin d'aya daga cikin yarana basu yi nasarar shiga sawun farko ba babu wacce ta Isa ...."
"kayi hakuri ka yafe min ban  fad'i  haka dan quntata  maka ba ya fadi hk kasancewarsa me saukin Kai sannan marason tashin hankali  yafi son yayi rayuwarsa cikin  salama  duk maganar da baba babba yake sam baba qarami bai juyo ba  ",shi wannan  Karen  zai  wuce sai kaji daga garesa sai dai  ya kamata ka sakin ranka dan wata rana ....saurin d'aga masa  hannu baba qarami   yayi still bai juyo ba sai dai  qirjinsa sai faman bugawa yake  Uncle Umar  ya juya cike da matsanacin firgici da  yanayin dan'uwan nasa ."

sai lokacin  baba qarami ya juyo yabi bayansa da wani  irin  mugun Kallo   Idanunsa a waje  har sanda takunsa ya kai uku bai juyo ba haka  shima baba qarami   bai daina kallonsa  ba .a sanyaye  fahad dansa   yabi bayan baba babba zuciyarsa na rawa dan shi kansa ya koka da  abinda mahaifinsa yayi  ya raka uncle Umar  sai dai bai Kai shi har bakin get ba a tsakiyar hanya ya barshi yana bashi hakuri "karka damu fahad na gode allah yayi maku albarka ya amsa da Ameen ya dawo part dinsu da sauri  .

falon ya d'auki shiru na tsawon lokaci yana tsaye yana  tunanin  bayanin daya samu daga bakin dan'uwansa  a yanzu   wanda  yake jinsa tamkar dalma acikin zuciyarsa , "uhmmmm yanzu dai ta  nuna mana cewa itace  uwar  Adam  Kuma ita  kadai ke da iko akan shi ?sai mugani  idan shi din d'an mace ne  Baba qarami yay  maganar yana jan tsaki a fili tare da watsa katuwar harara da mugun kallo kamar  tana gabansa fahad     ya  d'auki farin  glass cup ya tsiyaya masa   tattacen  ruwan inibi  ya mika masa "kasha baba kaji sanyi a ranka  yasa hannu ya Kar'ba ya  rike shi gam a hannunsa  sai dai bai sha  ba haka zalika bai ajiye ba."

"zan iya kasheki akan wannan haukan da kika yi zulaiheart  domin Ina da tanadi da buri akan adam ya karasa maganar yana filinging da  cup din hannunsa a fusace Wanda yasa take  yaransa maza da mata tare da matarsa suka sake  shiga rud'ani   cike da matsanacin firgici suna kallonsa gabansu na faduwa ban da   Hindu    data samu  guri ta kame akan kujerar da mahaifinta ya tashi  zuciyarta tafi ta kowa zafi da tuttukin bakinciki tare da shiga tashin hankali" Fahad ...." !
  ya kira sunan dansa Wanda aka kira da hkn   ya d'ago ya kallesa a matukar  tsorace batare da yace komai ba "abinda na fada Ina nufi har cikin zuciyata gara ta bar duniya ko ita yarinyar ta bar duniya akan rasa burina yayi maganar yana nuna sa da d'an yatsansa "wannan shine Karo na sau babu adadi da take kawo mana tashin hankali tun dan'uwanmu na raye dan haka Ina son kasheta na huta da ganinta a doron duniya  muddin ba daya daga cikin ya'yana  adam zai aura ba ."

daya bayan daya suka shiga kallon junansu cike da mamakin jin furunci mahaifinsu hatta hindu wannan karon atsorace take kallon mahaifinta  ta gigita kwarai  da gaske "a kullum kokarina naga na kawar daita a duniya darajan halakar da nake son qullawa adam yasa na barta  ya karasa maganar a kausashe .yayi taku daya biyu ya tsaya gaban hindu   yana kallonta "kece ya kamata ace kin auri adam ba wannan yarinyar ba kije kiyi rayuwa tamkar sauraniya   a gidansa ki taka kowa yadda kike so sannan ki juya duk Wanda kika ga dama  wannan hannun nawa babu abinda yasani a halin yanzu kamar ya wahalar da zulaiheart  ya gigita ta hanyar azabtuwa mai muni  ,ya matso kusa da hindu   Sosai suna fuskantar juna "wannan karon fuskarsa da murmushin mugunta akanta  "ke hindu ko zakiyi iya karfin halin kashe min zulaiheart?

Wani sanyayyayen murmushi ne ya bayyana akan fuskarta wanda mahaifinta ne kawai ya fahimci manufarsa ganin yadda ahlinta suke kallonta a tsorace yasa tayi saurin waskewa  tace "baba me yasa kake mgn fiyye da kaida ?gsky sam sam hakan bai dace ba tayi maganar tana kawar da idanunta gefe al'amun bata ji dadi ba  gumin da ya tsatsafowa   sauran yanuwanta suka shiga  gogewa suna sauke numfashi da ajiyar zuciya atare  Jin abinda tace daman km ita kad'ai ke iya fadawa mahaifisu mgn kai tsaye batare da shayi komai ba , a hankali ya juya yana taku cikin tsananin damuwa da tashin hankali   suka juya gbdy  suna kallon bayansa har ya shige bedroom dinsa yana shirya yadda zai kawar da hjy zulaiheart ko mrym daga doron duniya   .."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

               Page 13

"Baba   qarami  na  kwance har  kusan   tsakiyar  dare  ya kasa runtsawa  dan  sam bacci yaki  zuwan  masa sai  faman  juyi  yake  akan  makeken  katifarsa  ,yayinda matarsa   hjy  aljannatu  ke d'akinta  kwance   tana  sharar  bacci  amman  shi  kuwa  baba  qarami sai  tufka  yake  yana  warwara ya d'an  zabura  ya  mike  zaune  daga kwanciyar  da  yay, ya  had'e hannunwansa  duka  waje  d'aya "babu  tantama  hjy zulai tana da manufar  had'a  wannan  auren  yasan  tayi  haka  ne dan  kar wani acikinsu  yaci arzikin   d'anta , kunga   idan  ta had'asu  aure  da  diyar   d'anuwanta dole dai  arzikinsa yana tare  daita , dan da  zarar mrym  ta  haihu dashi   komai  na adam zai  dawo  nata  gbdy  zuwa yanzu dai  bai san abinda ya kamata  yayi  ba  ko hanyar  da   zai  bullo  masu   a maida auren  Kan  diyarsa ."

Sosai  kwakwaluwarsa  tayi  zurfi cikin  tunani  neman  mafuta har bai  san  sanda  hindu ta shigo d'akin  ba ,  ta  matso  kusa dashi ta tsaya tana  jijjiga baba  qarami  wanda  yayi  nisa cikin  duniyar  tunani "baba  baba !! " ta  kira  sunansa  har  sau biyu  ajere   sannan  yayi  firgigib  ya dawo haiyacinsa " wai meye haka  baba?" me yasa  zaka  damu  kanka akan   wannan 'yar qanqanuwar matsalar ?"  baba qarami  bai  iya amsa wa  ba sai  zuba  mata rinannun  idanunshi  da yayi yana dubanta   har  lokacin yana maimaita  abinda  ta  fad'a " ai a wajensa  wannan  ya wuce gagarumin  matsala  ba qanqanuwa ba  ko ita  kanta  tasan da zaman  haka  ta  dai  fad'a ne  dan  kwantar  masa da hankali  shi  kuwa  hankalinsa  bazai  ta'ba  kwanciya ba  matukar  ba  ganinta  yayi a matsayin matar adamu ba ."

"Dan   girman  Allah baba ka kwantar da hankalinka  mubi  komai a hankali  idan  muka  bari suka fahimci wani  abu  attare damu bazamu iya  nasara  akansu  ba "  cikin wani irin murya  mai  gyaraye da tashin hankali  had'e  da rud'ani  yake furta  "bazan  iya  ba hindatu , bazan  iya kwantar da hankalina  ba muddin  ba  ganinki  a gidan  adamu  nayi a matsayin  matarsa  ba  ,maganar  aurensa  da  mrym    ta dokeni  fiyye da tunaninki  ,Allah Allah nake gari ya   waye  naje  ga  zulai ayita ta qare  domin   kece kika fi dacewa da  Adam  ba wannan yarinyar ba dan  wannan  tsantsar muguta ne  kawai  take  son  nunawa"kai dai  baba ka  dan  boye damuwarka baba" .

    D'akin  ya  d'auki  shiru  tamkar  babu  wasu halitta  acikinsa   sai  na  qara  ac  dake  aiki  da kuma saukar  numfashinsu  haka  zalika baka  jin  motsin  komai  daga  sai  na  tsuntsaye   dake  shawagi  kasancewar  a  gra suke  hindu ta sauke numfashi tana mai kamo  hannunta  mahaifinta  cikin  nata "idan  kaje  me  zaka  cewa  mami  akaina ? " zan so nasan   abinda  zakace  baba  idan  ma  hali  kaje tare dani  ayi  komai  akan  idanuna  shekaru  sha biyar kenan ,  tun   inada  shekaru  sha  shida  nake  dakon soyayyarsa  bazan  iya  jurar  rasashi  ba, bazan zuba idanu  wata ta mallakesa ba "zan fad'a mata komai akan  soyayyarki  ni   ko  ta  biyu ce kizo  bazan damu   ba  burina  ki  kasance matsayin   mata  acikin  gidansa , ki zama tmkr sauraniya, ki yi yadda kike so  nima  nayi  yadda  nake só da  kamfanunuwansa  ."" nan  take ta  had'e  fuska  tamkar  dariya ba  muryarta  a  kausashe  ta  cigaba da mgn "muddin  a ta  biyu  zanzo  nasan   bazai ta'ba aurena ba , ya  adam  fa yana da tsari  acikin  rayuwarsa  shi  din ba mutun bane  kamar sauran mutane bashi da raayin tara mata "wa yace  miki  bashi  da  raayin haka ? zai yi raayi   dan uwarsa  Allah dai ya kai mu gobe tare zamu wajen  uwarsa  kafata  kafarki ."

Baba  qarami ya   mike  tsaye ya goya  hannunwansa abaya  yana  girgiza  kai yana duban hindu kafin daga  bisani  ya matso kusa daita sosai  ya  soma mgn   can  kasa kasa  kusan mintuna goma yana mata  mgn murmushin  jin dadi  né ya  bayyana akan fuskarta " idan bata  yarda ni na zama  matarsa  ba  I will  killed mrym  idan ni ban samesa  ba  to babu wacce  zata mallakesa anan  gidan  duniya yadda take  mgnr zaka fahimci da gaske  take  kuma  har cikin ranta abinda  take nufi  kenan ganin byn maryam ."
Chapter 35 · 0% Book details