← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 27 OF 100

Sashe 27

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

  ta d'ago kanta a hankali taga har lokacin kanshi na sunkuye yana danna wayar hannunsa  "ke har kin Isa kice wai bazaki aureni  ba ?tayi saurin   sunkuyar da kanta kasa tana sake jin digar wani abu mai zafi na diga a pent dinta wanda babu tantana jini ne yazo mata a dalilin tashin hankalin daya risketa ne
ya cigaba da magana fuskarsa a d'aure tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa  "daraja kika ci bancin haka har duniya ta nade baki Isa ba , km baki Kai matsayin da zaki zamo mata agareni ba ."

ta  d'an dago kad'an  ta saci kallonsa adaidai lokacin daya dago idanunshi suka tsarke cikin nata wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki wanda babu tantama na tsoro ne  wani irin mugun kallo yake mata mai firgitarwa "Ina  jinki  fad'a  min abinda kika fad'a masu ?"kaga AD  ba dan ka tutsiye yarinyar mutane muka taro anan ba mufi bukatar amincewarta akan komai "no aunty shahida bari ta fad'a  taga yadda zanci ubanta  ".

"nace abar wannan mgn  ta wuce ke  mrym kin amince zaki  auresa ko kuwa  har yanzu baki so dan yau shine final decision domin zamu sanar da mami  komai ? "muryarta na rawa tace "na ...na amince .."
"kin amince da me ya fad'a a tsawace yana zaro mata Idanunshi  "na amince zan..zan  aureka " you are very  stupid ,useless kawai tashi ki 'bace min da ganin  kafin na miki dukan mutuwa ,bana sonki kuma bazan aureki ba daman nasan baki Isa  ki kalleni ki fad'a min abinda kika fada musu ba ,  maza tashi ki bar nan bana son  kallon wannan banzar  fuskartaki ya k'arasa maganar  yana jan tsaki tare  da runtse idanunshi ."

har ta mike zata  tashi  aunty shahida tace  "koma ki zauna tayi saurin  girgiza mata Kai tana duban Inda yake zaune tare da jujjuya hannuwanta cike da tsoro  "nace  ki koma ki zauna a d'ard'ar  ta zauna tana kallon kasa a ranta tace "masefaffe banza kar Allah yasa ka aureni nima ai banasonka .

muryarsa  a kasalance yace "muddin kuna  bukatar na cigaba da zama na saurareku sai wannan yarinyar ta bar falon nan  " shiru falon yayi babu wanda yace uffan gashi babu wanda ya Isa yayi mgn sai aunty shahida ko khadija da yake bi bata isa ba bare zabiba da  kanwa ce ,aunty shahida  ta Kalli maryam tace  "mrym  kin  amince zaki auresa ?tayi saurin gyada mata Kai alamun "eh .!

"Okay tashi ki wuce abunki ta mike da sauri  kmr iska ta bar parlour'n "a gsky Adamcy ban ji dadin abinda kayi ba ,a hankali ake bin komai Kai komai zuciya da zafin rai Allah ya sausauta mk zuciyar nan karta sa wata rana kayi nadama  iska ya furzar "yanzu tunda ta amince shikenan sai mu sanar da mami  aunty shahida ta fad'a tana kallon kannenta mata "eh hk ne suka hada baki gbdy .

"Da izinin wa kenan zaku sanarwa sweetheart .?

"Da fari na amince maku  zan aureta  amman wannan iskancin da tayi yasa na fasa aurenta har abada km  komai zai faru sai dai ya faru amman na fasa "haba yayanmu dan Allah kayi hakuri karkayi haka  tunda ta amince ka aureta kawai a wuce wajen   tsoronka take ji shiyasa kaji ta fadi hk, cewar zabiba "ka taimakemu karka fasa auren nan  kodan mami  kabi komai a sannu please "ai bai ma Isa ba tunda ta yarda dole ya  aureta  ka godewa Allah da kasamu salahar mace mai kamewa kmrta  ."

"bafa zan aureta ba I repeat it I can't marry her ,na aureta na kaita Ina da wannan rashin tarbiyar nata ?"yanzu ku baku ga rashin dacewarmu ba ?A tare suka girgiza masa Kai "mu bamu gani ba sai sam barka .Ya girgiza Kai " matar data Kalli tsabar idanunku tace bata son jininku har abar so ce agurinku  ?yayi musu tmbyr a matukar fusace"

   dukkaninsu kallonsa sukayi yadda jikinsa ke rawa kmr anjonasa masa shocking ."Ku bar ganinta shiru shiru irin wadan nan  mutanen abun tsoro ne wallahi gara a  bani masefaffiya daita  juyin duniya sukayi dashi yace bai sonta km bazai aureta ba  "na yarda ku nemo wasu mata  ku aura min ko guda hudu ne  km a rana daya na amince amman ban da wannan jakar yarinyar mara tarbiya  yana gama fad'ar hk  ya mike ya kama gabansa kallon junansu sukayi na second  goma sannan suka numfasa "yanzu me kuka ga  zamuyi ?inji cewar aunty khadeja "mu fad'awa mami  kawai tasan komai dan boye boye bashi da wani amfani zan fada amnan mu bari zuwa jibi zan san yadda zan fad'a mata  .

atare suka mike suka nufi d'akin hjy zulaiheart tana zaune akan kujera tana duba abubuwan da suka kawo mata  suka shigo jikinsu a sanyaye tana ganinsu ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi  duk suka yiwa kansu mazauni ta kallesu daya byn daya "Allah  dai  ya taimakeku gbdy  yayi muku albarka yadda kuke tsaye akaina da abinda kuke min dukkaninku Kuna min k'okarin gurin yin abubuwa ."

"da wanda ya bani million daya da wanda ya bani dubu dari da wanda ya bani  dubu hamsim dukkaninku abu d'aya ne agurina Kuma inshallahu ladanku daya ne saboda dukkaninku abu d'aya ne
ni dai fatana Allah yayi muku albarka ,kowa yayi abinda zai iya ban da takura kai , Allah ya raya muku zuriarku yadda kuke hidima dani Allah yasa yayanku suyi muku fiyye da haka "Ameen suka had'a baki gurin fad'ar hk.

shiru sukayi babu wanda  ya sake  kokarin fad'a  mata halin da'ake ciki ta d'ago daga duban kayan da suka  kawo mata, shiru tayi tare da tsura musu Ido"ya na ga  kmar bakwa  cikin farinciki alhalin ba haka fuskokinku yake ba a d'azu da kuka zo  ? naunayen ajiyar zuciya suka sauke "ku fad'a  min  idan wani abu ne  ? shiru sukayi kowannensu najin tsoron mgnr ta fito daga bakinsa "Kun min shiru ku fad'a min mana Kun tasani gaba Kuna kallona da kyar  aunty khadeja ta soma bayani "kiyi hakuri aunty shahida zata fada miki komai amman ba yanzu ba ."

"akan Adamcy ne ko ?ta tmby tana dubansu a tare suka girgiza mata Kai  alamun "eh  suka tsinci kansu da bata amsa da haka "yanzu har akwai matsalar da zaku boye min bayan bani da kowa daga Allah sai ku duk abinda ya kunno Kai cikin rayuwarmu tare muke had'uwa muke magance matsalar shine yau zaku barni cikin duhu, shikenan na gode karku fad'a dan ko Kun fada min daga baya bazan gode ba Kuna iya tashi ku kama gabanku ."

zubewa sukayi a gabanta kamar zasuyi kuka "kiyi hakuri mami  zamu fad'a miki a natse aunty shahida ta zayyane mata  komai tun daga ranar da suka fara magana da mrym har zuwa yau din nan "shiru hjy zulaiheart tayi tana sauraron  aunty  shahida  da sauran  yaranta mata  byn ta gama Jin komai ta numfasa  kafin daga  bisani tace "shikenan ku barni dashi zan nuna masa ni na haifesa bashi ya haifeni ba  daman na dade da sanin  baya son farincikina."

nan  suka cigaba da tautaunawa  "Allah  mami   ki bud'e  masa wuta idan yaga kin haukace masa zai yi abinda kike so "ku  barni  dashi a yau din nan zai amince ko kuma ya canza uwa  aunty shahida tace "duk abun bai kai haka ba ki dai bisa a hankali kar komai ya jagule  "babu wani binsa da zanyi ahankali ai shi zuma ne sai ancisa da wuta ake samun kansa daman Ina lallabasa ne na d'auka abun nasa na girma da arziki ne  a she wulakanci ne  tana gama fad'ar  haka ta mike ta nufi d'akinta   .." tana shiga  aunty khadeja ta mike  ta d'auki jakarta ta rataya "ni zan wuce baza'a yi wannan dramar Ina gidan nan ba ,itama zabiba  ta mike jirani mu wuce tare gbdy suka mike suka fito tare  ."
*******
A bangare  mrym kuwa tana shiga d'akinsu  ta fashe da matsanacin kuka nana hauwa'u dake zaune ta zabura ta k'araso Inda take ta rungumeta tsam tana tambayarta sai dai taki bata amsa kuka take sosai zuciyarta na zafi da qunci "me yasa ya Adam bai sona ?me yasa nana hauwa'u fada min aibuna  da yasa baya Sona  ? tayi mgnr hawaye na tsiyayowa daga cikin idanunta ,nan nana hauwa'u ta fahimci dalilin kukanta "Kiyi hakuri marsi baki da wani aibu illa rashin sa'a irin nasa domin sai ya aureki zai san yayi Sa'ar samu mata  mai kyakkyawar zuciya."

       qaruwa kukan marsi yayi ",yadda bai sona
nima bana son shi amman nayiwa kaina alkwarin zan auresa zan rayu dashi muddin rai "  wani murmushin farinciki nana hauwa'u ta saki tare da sake rungumeta ajikinta tana Shirin magana qarar  wayar   yasa tayi shiru sannan  suka saki juna a hankali ta k'arasa ta d'auka tana kokarin fita daga d'akin  mrym ta shige bayi ta kulle ta jingina bayanta da kofar ta sulale  zuwa kasa tare da sakin wani  kuka tana toshe bakinta da sauri nana hauwa'u ta fito zuwa haraban gidan Inda ta iske yayyunta mata da mamaki take kallonsu ",ya haka har zaku wuce ?tafiyar dole ce auta  dan yau bom zai tashi a gidan nan Kuma tashin babba ne gara mu san Inda dare yayi mana "daman na kiraki ne dan kisan yadda zaki kwantarwa mrym hankali tare da bata kwarin gwaiwa ."

"Ga ta can kuwa sai kuka take amman ai ta amince zata auri yaya ? " eh ta amince amnan ai shi uban gayyar yace bai yi inji cewar zabiba "Kai!
ta fad'a tare da dafe goshinta "kiyi kokari ta dawo normal inshallahu zuwa jibi zamu shigo idan munji yarda suka kare da mami   juya sukayi a tare kowace ta nufi motarta tana tsaye direbobinsu suka jasu sannan ta juya da sauri ta koma ciki. koda ta koma d'akin bata ga mrym ba tana toilet ta kunnawa kanta ruwa tana kokarin daidaita natsuwarta da rarrashin zuciyarta, dole tana bukatar ta  rarrashi kanta sannan ta sanyawa zuciyarta hakurin zama dashi ta kowani hali , guri nana hauwa'u ta samu ta zauna abakin gado tana jiran fitowarta ."
Chapter 27 · 0% Book details