← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 28 OF 100

Sashe 28

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Rai  a matukar bace hjy zulaiheart ta shiga bangaren  ATA   tana gama shiga ta fara zuba masa fad'a " tur da haihuwarka Adam  " ya  waigo a matukar firgice yana zaro Idanu lokaci guda yay fillinging da wayar dake rike a hannunsa ya zube kan gwiwowinsa kasan  a gabanta cikin tsananin tashin hankali muryarsa a shake yace "sweetheart  me nayi ?"dan Allah ki yafe min ,kiyi min afuwa bazan sake ba."

hjy zulaiheart ta nuna sa da yatsa "Kai Adamcy ban ta'ba  sanin baka da hankali da tunani ba sai yau , yau  tsawon shekaru Ina binka akan magana daya amman babu komai na rantse da girman Allah bazan sake maka magana akan batun aurenka ba ka cigaba da rayuwarka  haka har mutuwa ta riskeka  tunda baka san mutuncin kanka ba, ga yarinya yar mutunci yar'uwarka amman dai..."sai tayi shiru tana huci ta kasa cigaba da mgn  sai lokacin ya fahimci laifinsa ."

        ya sunkuyar da kansa kasa yayinda mami  ta cigaba da magana cikin zafin rai "idan baka so maryam ba   wa yakamata kaso?" ba dan maryam na diyar dan'uwana ba tana da nagarta da kamun kan da  kowani nmj zai sota Kuma mahaifinta nada nagarta da zai zama surukinka  "ai ka nuna min ban Isa da Kai ba ko ? to  na gode Allah ya saka da alkhairi Allah ya biya ."

"a'a sweetheart wallahi kin Isa dani sai dai zuciyata ta kasa  ..."mami  tayi saurin  tareshi da cewa ",aikin banza daga yau in nice na haifeka to ka fara shirin aurenka da maryam Koda yin hakan yana nufin rasa komai naka  ATA  ya kalleta da sauri sannan yace "to sweetheart zanyi duk yadda kike so sai dai naso ki dan saueareni kiji ita kanta yarinyar bata ..."

Mami  ta juya a matukar fusace tana cewa  "bazan saurari komai daga bakinka ba ni dai na fad'a maka muddin nice uwarka ka shirya rayuwar aure da mrym idan baka zo ka sameni da maganar aurenta a daren yau ba   na rantse maka da girman Allah sai dai ka nemi wata uwar bani zulaiheart ba kayi abinda nake so shine zaman lafiyarka dani  ta karasa fita tana magana  cikin tsananin fushi da bata ta'ba yin irinsa ba ."

ATA ya rike kanshi tare da furta "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun"shikenan zuciyarsa ta sake shiga rud'ani   kasa ya zame ya zauna  akan capet tare da zabga tagumi tunani yake yi yanxu ya zai yi kenan?"shin ya cigaba da kafewa akan ra'ayinsa ne ko Kuma ya hakura ya aureta  a wuce gurin ?cike da sanyin jikin ya mike ya nufi bangarenta   Yana kokarin shiga part dinta sukayi karo da maryam  itama d'akin hjy zulaiheart zata sakmakon kiranta datayi ."

wani irin gigitacen mari ya ɗauketa dashi Sanna ya rufeta da duka "kina hauka ne da zaki hada jikinki danawa ? kasa tayi dafe da kuncinta tana kallon zara zaran yatsun ka'fafunsa dake jere kowannensu dauke   da kwantaccen gashi ,koina ajikinta rawa yake "mahaukaciya kawai ko ni sa'anki ne ?ta d'ago tana dubansa sai faman huci yake "Maza ki d'auke wad'an nan banzayen idanun naki akaina wallahi ban taba jin na tsani wani halitta ba kamarki har kece zaki bude baki ki fuskanci 'yan'uwana da Kalmar baki sona saboda ke din dakikya ce da bata san hallici ba yasa kafarsa d'aya ya take mata kafa yana watsa mata kallon banza ."

   "ki sani bana sonki kuma har abada bazan soki ba wani abu taji ya caki zuciyarta tare da kafeshi da idanunta da suka canza kala zuwa na bacin rai  yayinda wani bakinciki ya tokare mata kahon zuciya wanda yasa hawayen ya cika  idanunta amman ta danne taki barin su zuba  tunda  take baa ta'ba mata wulakanci irin na yau ba wannan shine karo na biyu da ya daura hannunsa ajikinta ranta yayi matukar baci  tana son ta bar wajen amman bazata iya ba bazata iya ba dan batasan me zai sake biyowa baya ba ,dan haka ta kife kanta akasa kuka take son tayi amman bata son tayi akan wani banza da bai san darajarta ba ..."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
   MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS
AYSHABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

Page 11

"  har tsawon wannan lokacin yana tsaye yana mata kallon kaskanci kafin daga bisani ya d'an motsa labbansa " biyayya   Kawai zan  yiwa  mahaifiyata na aureki   sai  dai  zakiji  jiki  sai   kinyi  da kin sanin  kalmarki  gareni,  zakin san kin  ta'boni   yana  gama   fad'ar   haka ya d'auke   kafarsa  tare da   shure   mata  kafa  ya nufi  cikin part  din  mahaifiyarsa ransa a dagule . 

girgiza  kai  mryam ta  shiga  yi  kafin  daga baya  ta  rarrafa  ta shige  parlour'nsu     ta  ra'be a bakin   kofar d'akin tana  kukan zuci , cikin   yanayi  na tashin   hankali  take  furta    "me  na  tsare maka  ya  adam  ? "me yasa   baka   sona  ? "me yasa   ka   tsaneni hk ? haka tayita  jerowa kanta   tambayoyin da bata da mai bata amsa  sai shi shi din kuma bata isa ta tuknkaresa ba   gbdy  Idanunta   sun canza qala tsabar tashin hankalin data tsinci kanta ."

kuka   take  son yi sai  dai   zafin da zuciyarta    ke yi  yasa  hawayenta yaki diga sai idanuwanta gbdy sun burkice    " baka sona   amman  ya zama   dole  na  jurewa  komai  muddin  ina  son rabuwa da iyayena   lafiya , bazata  manta kalman mahaifinta   ba alokacin da zata dawo daga  abuja   domin sun samu kyakkyawan  mazauni  acikin kwalkwaluwarta "maryam  muddin  ni  ne  wanda   nayi  sanadiyyar zuwanki  duniya  Kuma kina  son  gamawa da duniya  lafiya  ki auri adam  bisa umarnina Kuma ki zauna dashi  zama na amana bisa umarnina , yau ace ba yar'uwata ce  ta nemi wannan hadin ba sam bazan takura miki ba zan barki har sanda zaki kawo min irin mijin da kike so   .."

A  bakin  gado  ya iske hjy zulaiheart   ta  cika tayi bam   ,cikin   sanyi  jikin nan nashi  ya k'araso   ya  zauna  a gabanta   yana  neman gafararta  ,   ko  kallon Inda   yake   bata yi  ba daga   karshe  ma ta  kawar   da   fuskarta  gefe  al'amun  bata  son ganinsa   ya   runtse idanuwanshi  sosai yana sauke  numfashi ,byn  kmr  second biyar ya bud'e  idanunshi  ya fara  Kame  kame  "uhm ammm   kiyi hakuri   sweetheart   , afuwa sweetheart   I will not  do  it  again , inshallahu  I promise  you  zan aureta ."

"hjy zulaiheart taji  dadin jin    furucinsa     har  cikin   ranta  sai  dai ta share  tana  jan tsaki a fili. "ki yarda  sweetheart duk  duniya   babu  wanda  zai  soki  da son farincikinki   kmr ni  ,kiyi  hakuri  bazan  juri  ganin  'bacin   ranki ba   ya fad'a yana riko hannunta ,  naunayen ajiyar zuciya ta  sauke batare  data  fuskancesa ba  ,duk  da  zuciyarta ta d'an  yi sanyi  dan daman fushin na dole ne yanxu kuwa ta   hakura .

damuwarta  daman yayi   aure  tana  son  taga aurensa  taga  ya'yansa  kamar  yadda  taga na sauran  yaranta   amman  duk  da  haka  bazata sakar  masa fuska  ba dan tasan halinsa kamar yunwar cikinta canzawarsa  bai da wuya  ya  d'auki  mintuna masu tsawo  agabanta bata  daga  Kai ta  kallesa ba sai ma  ta mike zata  bar masa  d'akin , ya mike da sauri  jikinsa na kyarma  ya  tareta  dan sosai ya hango  damuwa qarara akan  fuskarta  ya sake kamo hannuwanta  duka cikin nashi  , ta  fizge  a fusace tana watsa masa harara   "sweetheart  kiyi hakuri  dan girman Allah  wallahi  zan  aureta  trust Adamcy  zai  aureta tunda  yace  zaiyi wallahi wallahi zan aureta Koda kuwa  zan rasa rayuwata....."

hannunta d'aya  tasa ta zare  hannunta daga cikin  nashi   ta tsura masa  idanunta  "wallahi  ban  san  Inda ka d'auko halinka  ba ,  sam mahaifinka   ba haka yake  ba  mutumin kirki  ne, mahaifinka baya  uhm  baya  uhm bare miskilanci ,  kullum cikin neman   yadda  zai kyautata  mana daku ya'yansa da  'yan'uwansa yake ,  a kullum mahaifinku  so  yake   ku  zama na gari a rayuwa  sannan  masu  jin  kan iyaye  da tausayi  Allah ya  duba  bayan mahaifinku  cikin kaf  ya'yan  mahaifinka   Kai ne  kawai  ka  fita dabam acikinsu  da wasu halaiya Kai ma  Kuma wannan  halin miskilancin da zafin zuciyar  ne  illarka tun kafin ya  rasu ya fad'a  yace bashi  ka d'auko ba .bari na  fad'a maka gsky  wannan halin naka sam ba  nashi  bane  Kai ka san  Inda ka samo  abunka dan shi ba haka yake yi  ba,  dan ta mahaifinka    duniya  bazai  tashi ba  ,ga rikon addinin  ga  tsananin zumunci da sanyi hali ."

ga lokaci   yazo daya kamata  ka tattara biyayyar  Uba  da  uwa ka had'a   kayi  min amman kullum cikin musguna min  kake akan zance aure  auren da kai ne kaji dadinsa ,  wallahi duk macen  data  samu  miji   irin mai  halin mahaifinka  ta gama dace  a duniya da lahira ni kaina  kullum kukan da nake  yi  kenan mahaifinka  ya bauta mana  ya sangartani   sannan ya bautawa  zumunci  Allah   ya  jikansa yasa aljanna ce makomarsa  ka canja  idan  zaka  canza tana gama  fad'ar  haka ta  fita ta barshi cike da zafin zuciya."

Jiki  a  sanyaye  ya bar d'akin  zuwa nashi  yana shiga   d'akinsa  ya shiga zariya   kwalkwaluwarsa ta  shiga tunani , sai dai  Kansa ya  toshe  ya  cunkushe guri d'aya  ya kasa tunanin  komai ya  zauna a bakin gado ya  had'e  hannunwansa duka  a  ha'barsa  yana  tunanin  can  byn wasu mintuna   ya  mike ya koma  kan  bedside ya zauna  yayi shiru yana kallon  d'akin  ,sake  mikewa  yayi  ya  d'aura Kashi  akan  katifa  yana Jin   quna a ransa.
Chapter 28 · 0% Book details