Sashe 38
Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
Ya mike tsaye ya qarasa inda d'an qaramin fridge dinsu thermocool yake wanda ya gaji dan murfin ma ya balle idan an bud'e da kyar ake maidashi a rufe ya ciro pure watar mai sanyi ya ajiye akan hannun kujera ya maida murfin fridge din da kyar ya qaraso inda take "heartbeat ga ruwa ki sha "yauwa after dad na gode sosai ya koma Kan kujera daya tashi yana cewa "ya exam din fatan yazo da sauki ?sai data zuke ruwan sannan tace "babu wani sauki amman muna fatan samun nasara daga Allah bata sake cewa komai ba sannan bata zauna ba ta qaraso bayi ta dauro alwala ta fito ta d'auki wani dadduma sallah daga inda suke ajiyewa ta shimfida kusa da mahaifiyarta dake zaune har lokacin tana kaiwa allah kukata akan yaranta most especially maryama wacce ta fita jarabawar karshe ta tada sallah a natse ."
Bayan ta idar da sallah ta mike tsaye tana ninke sallayar ta samu waje ta zauna kusa da habib tana sauke numfashi "kai wallahi ban ta'ba gajiya irin na yau ba wannan hanyar ta yanoba akwai matukar wahala alhamdulillah daga yau dai mun huta bata gama rufe bakinta ba taji an bako kofar shigowa falon nasu da karfi atare suka kallo kofar kaulat ce tare da mahaifiyarta tsaye suna huci Aunty hassana tace "yauwa gara da Allah yasa na sameku gbdy uwa da ya marasa mutunci to wallahi na gaji ki jawa wannan tantariyar yartaki mai suffar manufukai kunne ta shiga hankalinta bata tashi dawowa gidan nan daga yawon karywancinta sai yamma tayi lokacin da manema auren yarana suke zuwa ta dinga wannan yar iskar tafiyar tata simi simi kmr macijiya dan kawai ta dauki hankalin samarin ya'yanmu to wallahi kinyi kadan bake ba hatta uwar data kawoki duniya ga tanan tayi kad'an bare Ke karan kada miya ,ko su sukayi koba dinki?
" ko su sukace maza su dinga gudunki ?ko Kuma su suka sanya mugun balai ajikinki da maza ke gudunki ? babu daya da sukayi aciki dan haka daga yau banason sake ganin gyallinki idan bilal yazo gidan nan aikin banza kawai kyau har kyau amman bashi da amfani , ana fakewa da karatu ana yawon karuwanci "tana kawo nan habib ya zabura ya mike jikinsa na rawa tare da daga hannu zai zabga ma Aunty hassana mari...."
aunty wacce ta mike tsaye tun fara maganr Aunty hasana tayi saurin rike masa hannu tana cewa " qul habib karka fara ko ka manta wacece ita da matsayinta agurinka? "amman male bakiji kalmar da take fad'awa heartbeat ? "an fada Kuma an sake fada dan uwarka da ubanka kayi duk abinda zakayi karya na fada ba yawon karuwanci take ba ?" idan bashi take ba me yasa samarinta suke gudu su barta ?idan baka sani ba kasani daga yau ai raba masu kanta take kmr MTN shiyasa suke gudu suna barinta jairi kawai da wani katon kanka can shegu marasa mutunci jinin marasa mutunci ai da bakayi haka ba bazansa kayi gadon dangin uwarka ba masu arziki amamn matsiyatan mutane ."
Tunda ta fara magana hanakalin maryama yay kolowar tashi sosai ta firgita da kalaman aunty hassana ba idanuwanta suka cika da ruwan hawaye ta kalli inda kaulat take da kyar ta bude baki cikin sanyayyar muryarta mai tsananin kashe jiki "mama Ke kanki sheida ce akaina Kinsan bazan ta'ba aikata wani abu da zai 'bata sunan ahlina ba ,walalhi bana aikata komai karatu kawai nake zuwa sannan mama ko babu komai ni din diyar d'anuwanki ce kuma abar tausayi a irin wannan rayuwar da muke wacce babu wani yanci acikinsa sai tsabar kaskanci kece mutun ta farko da daya kamata ki cetomu amamn sai gashi kece mutun ta farko dake bibiyarmu da mugun alkaba'i ta sake kallon inda kaulat take tsaye tana zabga mata harara."
"ga kaulat nan idan zata fadi gsky babu wani abu danayi hassalima ko magana banyi ba ta gefensu na raba zan .." dakata dan Allah malama banson manufarci bangane atambayeni ba ta fad'a cikin zafi rai kafin daga baya ta dawo gabanta ta tsaya "duk abinda mama ta fad'a gsky ne kisa kunnen baseera ki ji abinda aka fad'a miki ,ki tsaya iya matsayinki ki kiyaye shigowa alokacin da bilal yake zuwa tana magan tana nuna maryama da yatsan hannunta "idan karuwanci zakiyi sai ki san inda zakiyi ba ..." tas tas !! habib ya dauketa da gigitaccen mari "da uban wa kike wannan maganar ?da ubanka nake banza kawai mara kunya ta fad'a tana dafe kuncinta .
"idan kika sake zagina ko zagin yaruwata wallahi sai nayi miki jina jina anan shegiya yar iskar banza kakar ubanki ce karuwa..."ai bai gama rufe baki ba Aunty hassana ta sauke masa nashi mari ji kake tas tas !! sau biyu ajere "dan uwarka a gabana zaka mari yata ?" jakar gidan uwarka ce da zaka mareta ?"
habib ya bude baki zai sake yin magana aunty ta sake dakatar dashi" karka Kara cewa komai wannan idan da sabo tuni princess ta saba dan haka komai hassana zata fada akanta banason ka sake cewa uhm bare uhm uhm dan yarta ce halak malak idan karuwa ce ita tayi silar zuwanta duniya ."
aikuwa ransa yayi massefar bacci ya dinga Jin wani tuttukin bakinciki na taso masa "ke ai da kin kuskura ya sake ta'ba min lafiya 'ya wallahi da yaga aika aika da yau mun kwashi Yan kallo dake dan kece saar yina basu ba habib bai daddara ba yace "allah Aunty ki kama girmanki Kafin na miki abinda bakya tunani koda yake ai ba girma atare dake mahaifiyarmu tafi karfinki sai dai Kiyi damu ba arabi ba boko shiyasa baki san haramcin abinda kikeyi ba "da uwarka da dangin uwarka kake ba dani ba tana gama fadar haka taja hannun kaulat suka nufi kofa tana cewa"dan kutumar uba kawai ."
Kuka maryama take sosai a wajen tamkar ranta zai fita aunty ta qaraso wajen da take tsaye tare da dafa maryama me ye kuma na kuka bayan wannan ba sabon abu bane ? Kuka taci gaba dayi habib ya matso "dan allah heartbeat ki daina kuka idan ba haka ba nima zanyi kuka tana kuka habib na kuka nan da nan aunty ta samu waje ta zauna ta d'aura kanta a hannun kujera itama kukan take da karfi
A hankali suka qaraso suka durkushe kasa kusa da kafafun Aunty tare da daura kansu a saman cinyarta suna cigaba da rera Kuka wanda har umma ta shigo basu saniba" umma ta qarasa shigowa da sauri tare da dafe qirji bilkisu me ya faru Kika tasa yara gaba kuka ? Kuka suka ci gaba dayi ba tare da sun bata amsa ba..."Ke maryama taso muje ki gayamun me yafaru da ke da mamanki da kaninka haka kuke kuka ? ."
hannunta umma ta riqo suka nufi bangarenta Aunty salma dake tsaye taga wucewarsu maryama na goge kwalla tasan ba lafiya ba ta biyo bayansu da sauri umma ta zaunar da ita a Kan kujera ,a lokacin kukan nata ya fara raguwa"me ya sameku haka kuke wannan uban kuka haka maryama ? Jin shirun da tayi ne yasa aunty Salma ta tunzura "wani mahaukacin tsawa ta sakar mata wanda sai da ta burkice "wai ba magana ake miki ba ne?sai lokacin umma tasan da shigowarta ta dago tana kallon tana mamakin hali munafurci irin nata ko wa ya kirata data shigo ? umma ta hade rai tana cewa "a'a salma ba haka akeyi ba ki barni daita kawai karki hargitsa mata lissafi ki barta zatai magna."
"uhm ina jinki maryama fad'a min damuwarki cikin sheshekar kuka ta zayyanewa umma komai da ya faru naunayen ajiyar zuciya ta sauke "gsky bata kyau ba , amman Kiyi hakuri ita rayuwa ta gaji haka komai da kika gani kafin a samu nasara sai anyi hakuri in sha allahu wata rana zai zama labari ,ku ya kamata ku dinga kwantar wa da mahaifiyarku hankali ba wai ku dinga tayata kuka ba yi hakuri kinji maryama Ki bar komai a wajen Allah in sha allahu sai kin zama madubi abar dubawa acikin gidan nan masu takaki wata rana sai sun zama fadawanki "wallahy aunty aseeya har da laifinki wajen iskanci yarinyar nan kawai daga yar wannan mgnr zasu zauna suna kuka Kmr mutuwa akayi ke km sai ki zauna kina bata lokacinki ."
" babu ruwanki dole na rarrashi diyata mikewa tayi ta fice cikin fushi umma tabi bayanta da kallo karki qara damuwa da sharrinsu idan kina kuka suna ganin rauninki to kin shiga matsala dan kullum da abinda zasu dinga miki amman idan kika jajurce kece zaki ga rauninsa ta fad'a hk tana goge mata fuska da gefen zaninta "kin ci abinci ma kuwa ?ta girgiza kai alamun a'a to maza jeki ki rarrashin mahaifiyarki da danuwanki ki dawo ga abinci kizo kici ta mikar daita ta rakata har bakin kofar fita da kyar ta fito zuwa bangarensu wanda lokacin tuni aunty ta daina kuka suna zaune da habib tana gama shigowa taji saurin muryar Aunty "my princess taho kici abinci nasan kina tattare da yunwa."
Babu yadda ta iya ta sakar mata murmushin gefe baki tana dubanta tace "kamar kin sani Aunty gbdy suka qarasa zuwa Kan kujerun roba dake zagaye da qaramin table wanda shima din na roba ne aunty na zaune tare da yaranta suna cin abinci amamn ita tayi shiru tana tunani ta kasa cin abinci "male kici abinci mana ta dago ta kalli habib maryama ta ajiye spoon din hannunta ta soma magana a tsanake kamar ba yanzu ta gama kuka ba."
Bayan ta idar da sallah ta mike tsaye tana ninke sallayar ta samu waje ta zauna kusa da habib tana sauke numfashi "kai wallahi ban ta'ba gajiya irin na yau ba wannan hanyar ta yanoba akwai matukar wahala alhamdulillah daga yau dai mun huta bata gama rufe bakinta ba taji an bako kofar shigowa falon nasu da karfi atare suka kallo kofar kaulat ce tare da mahaifiyarta tsaye suna huci Aunty hassana tace "yauwa gara da Allah yasa na sameku gbdy uwa da ya marasa mutunci to wallahi na gaji ki jawa wannan tantariyar yartaki mai suffar manufukai kunne ta shiga hankalinta bata tashi dawowa gidan nan daga yawon karywancinta sai yamma tayi lokacin da manema auren yarana suke zuwa ta dinga wannan yar iskar tafiyar tata simi simi kmr macijiya dan kawai ta dauki hankalin samarin ya'yanmu to wallahi kinyi kadan bake ba hatta uwar data kawoki duniya ga tanan tayi kad'an bare Ke karan kada miya ,ko su sukayi koba dinki?
" ko su sukace maza su dinga gudunki ?ko Kuma su suka sanya mugun balai ajikinki da maza ke gudunki ? babu daya da sukayi aciki dan haka daga yau banason sake ganin gyallinki idan bilal yazo gidan nan aikin banza kawai kyau har kyau amman bashi da amfani , ana fakewa da karatu ana yawon karuwanci "tana kawo nan habib ya zabura ya mike jikinsa na rawa tare da daga hannu zai zabga ma Aunty hassana mari...."
aunty wacce ta mike tsaye tun fara maganr Aunty hasana tayi saurin rike masa hannu tana cewa " qul habib karka fara ko ka manta wacece ita da matsayinta agurinka? "amman male bakiji kalmar da take fad'awa heartbeat ? "an fada Kuma an sake fada dan uwarka da ubanka kayi duk abinda zakayi karya na fada ba yawon karuwanci take ba ?" idan bashi take ba me yasa samarinta suke gudu su barta ?idan baka sani ba kasani daga yau ai raba masu kanta take kmr MTN shiyasa suke gudu suna barinta jairi kawai da wani katon kanka can shegu marasa mutunci jinin marasa mutunci ai da bakayi haka ba bazansa kayi gadon dangin uwarka ba masu arziki amamn matsiyatan mutane ."
Tunda ta fara magana hanakalin maryama yay kolowar tashi sosai ta firgita da kalaman aunty hassana ba idanuwanta suka cika da ruwan hawaye ta kalli inda kaulat take da kyar ta bude baki cikin sanyayyar muryarta mai tsananin kashe jiki "mama Ke kanki sheida ce akaina Kinsan bazan ta'ba aikata wani abu da zai 'bata sunan ahlina ba ,walalhi bana aikata komai karatu kawai nake zuwa sannan mama ko babu komai ni din diyar d'anuwanki ce kuma abar tausayi a irin wannan rayuwar da muke wacce babu wani yanci acikinsa sai tsabar kaskanci kece mutun ta farko da daya kamata ki cetomu amamn sai gashi kece mutun ta farko dake bibiyarmu da mugun alkaba'i ta sake kallon inda kaulat take tsaye tana zabga mata harara."
"ga kaulat nan idan zata fadi gsky babu wani abu danayi hassalima ko magana banyi ba ta gefensu na raba zan .." dakata dan Allah malama banson manufarci bangane atambayeni ba ta fad'a cikin zafi rai kafin daga baya ta dawo gabanta ta tsaya "duk abinda mama ta fad'a gsky ne kisa kunnen baseera ki ji abinda aka fad'a miki ,ki tsaya iya matsayinki ki kiyaye shigowa alokacin da bilal yake zuwa tana magan tana nuna maryama da yatsan hannunta "idan karuwanci zakiyi sai ki san inda zakiyi ba ..." tas tas !! habib ya dauketa da gigitaccen mari "da uban wa kike wannan maganar ?da ubanka nake banza kawai mara kunya ta fad'a tana dafe kuncinta .
"idan kika sake zagina ko zagin yaruwata wallahi sai nayi miki jina jina anan shegiya yar iskar banza kakar ubanki ce karuwa..."ai bai gama rufe baki ba Aunty hassana ta sauke masa nashi mari ji kake tas tas !! sau biyu ajere "dan uwarka a gabana zaka mari yata ?" jakar gidan uwarka ce da zaka mareta ?"
habib ya bude baki zai sake yin magana aunty ta sake dakatar dashi" karka Kara cewa komai wannan idan da sabo tuni princess ta saba dan haka komai hassana zata fada akanta banason ka sake cewa uhm bare uhm uhm dan yarta ce halak malak idan karuwa ce ita tayi silar zuwanta duniya ."
aikuwa ransa yayi massefar bacci ya dinga Jin wani tuttukin bakinciki na taso masa "ke ai da kin kuskura ya sake ta'ba min lafiya 'ya wallahi da yaga aika aika da yau mun kwashi Yan kallo dake dan kece saar yina basu ba habib bai daddara ba yace "allah Aunty ki kama girmanki Kafin na miki abinda bakya tunani koda yake ai ba girma atare dake mahaifiyarmu tafi karfinki sai dai Kiyi damu ba arabi ba boko shiyasa baki san haramcin abinda kikeyi ba "da uwarka da dangin uwarka kake ba dani ba tana gama fadar haka taja hannun kaulat suka nufi kofa tana cewa"dan kutumar uba kawai ."
Kuka maryama take sosai a wajen tamkar ranta zai fita aunty ta qaraso wajen da take tsaye tare da dafa maryama me ye kuma na kuka bayan wannan ba sabon abu bane ? Kuka taci gaba dayi habib ya matso "dan allah heartbeat ki daina kuka idan ba haka ba nima zanyi kuka tana kuka habib na kuka nan da nan aunty ta samu waje ta zauna ta d'aura kanta a hannun kujera itama kukan take da karfi
A hankali suka qaraso suka durkushe kasa kusa da kafafun Aunty tare da daura kansu a saman cinyarta suna cigaba da rera Kuka wanda har umma ta shigo basu saniba" umma ta qarasa shigowa da sauri tare da dafe qirji bilkisu me ya faru Kika tasa yara gaba kuka ? Kuka suka ci gaba dayi ba tare da sun bata amsa ba..."Ke maryama taso muje ki gayamun me yafaru da ke da mamanki da kaninka haka kuke kuka ? ."
hannunta umma ta riqo suka nufi bangarenta Aunty salma dake tsaye taga wucewarsu maryama na goge kwalla tasan ba lafiya ba ta biyo bayansu da sauri umma ta zaunar da ita a Kan kujera ,a lokacin kukan nata ya fara raguwa"me ya sameku haka kuke wannan uban kuka haka maryama ? Jin shirun da tayi ne yasa aunty Salma ta tunzura "wani mahaukacin tsawa ta sakar mata wanda sai da ta burkice "wai ba magana ake miki ba ne?sai lokacin umma tasan da shigowarta ta dago tana kallon tana mamakin hali munafurci irin nata ko wa ya kirata data shigo ? umma ta hade rai tana cewa "a'a salma ba haka akeyi ba ki barni daita kawai karki hargitsa mata lissafi ki barta zatai magna."
"uhm ina jinki maryama fad'a min damuwarki cikin sheshekar kuka ta zayyanewa umma komai da ya faru naunayen ajiyar zuciya ta sauke "gsky bata kyau ba , amman Kiyi hakuri ita rayuwa ta gaji haka komai da kika gani kafin a samu nasara sai anyi hakuri in sha allahu wata rana zai zama labari ,ku ya kamata ku dinga kwantar wa da mahaifiyarku hankali ba wai ku dinga tayata kuka ba yi hakuri kinji maryama Ki bar komai a wajen Allah in sha allahu sai kin zama madubi abar dubawa acikin gidan nan masu takaki wata rana sai sun zama fadawanki "wallahy aunty aseeya har da laifinki wajen iskanci yarinyar nan kawai daga yar wannan mgnr zasu zauna suna kuka Kmr mutuwa akayi ke km sai ki zauna kina bata lokacinki ."
" babu ruwanki dole na rarrashi diyata mikewa tayi ta fice cikin fushi umma tabi bayanta da kallo karki qara damuwa da sharrinsu idan kina kuka suna ganin rauninki to kin shiga matsala dan kullum da abinda zasu dinga miki amman idan kika jajurce kece zaki ga rauninsa ta fad'a hk tana goge mata fuska da gefen zaninta "kin ci abinci ma kuwa ?ta girgiza kai alamun a'a to maza jeki ki rarrashin mahaifiyarki da danuwanki ki dawo ga abinci kizo kici ta mikar daita ta rakata har bakin kofar fita da kyar ta fito zuwa bangarensu wanda lokacin tuni aunty ta daina kuka suna zaune da habib tana gama shigowa taji saurin muryar Aunty "my princess taho kici abinci nasan kina tattare da yunwa."
Babu yadda ta iya ta sakar mata murmushin gefe baki tana dubanta tace "kamar kin sani Aunty gbdy suka qarasa zuwa Kan kujerun roba dake zagaye da qaramin table wanda shima din na roba ne aunty na zaune tare da yaranta suna cin abinci amamn ita tayi shiru tana tunani ta kasa cin abinci "male kici abinci mana ta dago ta kalli habib maryama ta ajiye spoon din hannunta ta soma magana a tsanake kamar ba yanzu ta gama kuka ba."