← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 38 OF 100

Sashe 38

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Ya mike  tsaye   ya  qarasa inda  d'an  qaramin fridge dinsu  thermocool yake wanda ya gaji dan murfin ma ya balle idan an bud'e da kyar ake maidashi a rufe ya ciro pure watar mai sanyi ya ajiye akan hannun kujera ya maida murfin  fridge  din da kyar ya qaraso inda take "heartbeat ga ruwa ki sha  "yauwa after dad  na gode  sosai  ya koma Kan kujera daya tashi yana cewa "ya exam din fatan yazo da sauki ?sai data zuke ruwan sannan tace "babu wani sauki amman muna fatan samun nasara daga Allah bata sake cewa komai ba sannan bata zauna ba ta qaraso bayi ta dauro alwala ta fito ta d'auki wani dadduma sallah daga inda suke ajiyewa ta shimfida kusa da mahaifiyarta dake zaune har lokacin tana kaiwa allah kukata akan yaranta most especially maryama wacce ta fita jarabawar karshe ta tada sallah a natse ."

Bayan ta idar da sallah  ta mike tsaye  tana  ninke sallayar ta samu waje ta zauna kusa da habib tana sauke numfashi "kai wallahi ban ta'ba gajiya irin na  yau ba wannan hanyar ta yanoba akwai matukar wahala alhamdulillah  daga yau dai mun huta bata gama  rufe  bakinta   ba taji an bako kofar shigowa falon nasu  da  karfi atare suka kallo kofar kaulat ce tare  da mahaifiyarta tsaye suna huci Aunty hassana tace "yauwa gara da Allah yasa na sameku  gbdy uwa da ya marasa  mutunci  to wallahi na gaji  ki jawa wannan tantariyar yartaki mai  suffar  manufukai kunne ta shiga  hankalinta  bata tashi dawowa  gidan nan daga yawon karywancinta  sai yamma tayi lokacin  da manema  auren yarana suke zuwa ta dinga wannan yar iskar tafiyar tata  simi simi kmr macijiya dan kawai ta dauki hankalin samarin  ya'yanmu to wallahi kinyi kadan  bake  ba hatta uwar  data kawoki  duniya ga tanan tayi kad'an bare Ke karan  kada miya ,ko su sukayi koba dinki?

" ko su sukace maza su dinga gudunki  ?ko Kuma su suka sanya mugun balai ajikinki da maza ke gudunki ? babu daya da sukayi aciki dan haka daga yau banason sake ganin gyallinki idan bilal yazo gidan nan  aikin banza  kawai kyau  har kyau amman bashi da amfani , ana  fakewa da karatu ana  yawon karuwanci "tana kawo nan habib ya zabura ya mike jikinsa na rawa  tare da daga hannu zai zabga ma Aunty hassana mari...."

aunty  wacce ta mike tsaye tun fara maganr Aunty hasana tayi  saurin rike masa hannu tana cewa " qul  habib  karka fara ko ka manta wacece ita da matsayinta agurinka?  "amman male  bakiji kalmar da take fad'awa heartbeat ? "an fada Kuma an sake fada dan uwarka da ubanka kayi duk abinda zakayi karya na fada ba yawon karuwanci take ba ?" idan bashi take ba me yasa samarinta suke gudu su barta ?idan baka sani ba kasani daga yau ai raba masu kanta take kmr MTN shiyasa suke gudu suna barinta  jairi kawai da wani katon kanka can shegu marasa mutunci jinin marasa mutunci ai da bakayi haka ba bazansa kayi gadon dangin uwarka ba masu arziki amamn matsiyatan mutane  ."

Tunda ta fara magana hanakalin maryama yay  kolowar tashi sosai ta firgita da kalaman aunty hassana  ba idanuwanta suka cika da ruwan hawaye ta kalli inda kaulat take da kyar ta bude baki cikin sanyayyar muryarta mai tsananin kashe jiki "mama Ke kanki sheida ce akaina Kinsan bazan ta'ba aikata wani abu da zai 'bata sunan ahlina ba ,walalhi bana aikata komai karatu kawai nake zuwa  sannan mama ko babu komai ni din diyar d'anuwanki ce kuma abar tausayi a irin wannan rayuwar da muke wacce babu wani yanci acikinsa sai tsabar kaskanci kece mutun ta farko da daya kamata ki cetomu amamn sai gashi kece mutun ta farko dake bibiyarmu da mugun alkaba'i  ta sake kallon inda kaulat take tsaye tana zabga mata harara."

"ga kaulat nan idan zata fadi gsky babu wani abu danayi hassalima ko magana banyi ba ta gefensu na raba zan .." dakata dan Allah malama  banson manufarci bangane atambayeni ba ta fad'a cikin zafi rai kafin daga baya  ta dawo gabanta ta tsaya "duk abinda mama ta fad'a gsky ne kisa kunnen baseera ki  ji abinda aka fad'a miki ,ki tsaya iya matsayinki ki kiyaye shigowa alokacin da bilal yake zuwa tana magan tana nuna maryama da yatsan hannunta "idan karuwanci zakiyi sai ki san inda zakiyi ba ..." tas tas !! habib ya dauketa da gigitaccen mari "da uban wa kike wannan maganar ?da ubanka nake banza kawai mara kunya  ta fad'a tana dafe kuncinta .

  "idan kika sake zagina ko zagin yaruwata wallahi sai nayi miki jina jina anan shegiya yar iskar banza kakar  ubanki ce karuwa..."ai bai gama rufe baki  ba Aunty hassana ta sauke masa nashi mari ji kake tas tas !! sau biyu ajere "dan uwarka a gabana zaka mari yata ?" jakar gidan uwarka ce da zaka mareta ?"
habib ya bude baki zai sake yin  magana aunty ta sake dakatar dashi" karka Kara cewa komai wannan idan da sabo tuni princess ta saba  dan haka komai hassana zata fada akanta  banason ka  sake cewa  uhm bare uhm uhm dan yarta ce halak malak idan karuwa ce ita tayi silar zuwanta duniya ."

aikuwa ransa yayi massefar bacci ya dinga Jin wani tuttukin bakinciki na taso masa "ke ai da kin kuskura ya sake ta'ba min lafiya 'ya wallahi da yaga aika aika da yau mun kwashi Yan kallo dake dan kece saar yina basu ba habib bai daddara ba  yace "allah Aunty  ki kama girmanki Kafin na miki abinda bakya tunani koda yake ai ba girma atare dake mahaifiyarmu tafi karfinki sai dai Kiyi damu ba arabi ba boko shiyasa baki san haramcin abinda kikeyi ba "da uwarka da dangin uwarka kake ba dani ba tana gama fadar haka taja hannun kaulat suka nufi kofa tana cewa"dan kutumar uba kawai ."

Kuka  maryama  take  sosai  a wajen  tamkar ranta zai fita  aunty  ta qaraso  wajen da take tsaye  tare da dafa maryama  me ye kuma na kuka  bayan wannan ba sabon abu bane ? Kuka taci gaba dayi  habib ya matso "dan allah heartbeat ki daina kuka idan ba haka ba nima zanyi kuka tana kuka habib na kuka nan da nan aunty ta samu waje ta zauna ta d'aura kanta a hannun kujera itama kukan take da karfi
A hankali suka qaraso suka durkushe kasa kusa da kafafun Aunty tare da daura kansu a saman cinyarta  suna  cigaba da rera Kuka    wanda har  umma ta shigo   basu saniba" umma  ta qarasa shigowa da sauri  tare da dafe qirji  bilkisu  me ya faru Kika tasa yara gaba kuka ? Kuka  suka  ci gaba dayi ba tare da sun bata amsa   ba..."Ke maryama taso muje ki gayamun me yafaru da ke  da mamanki da kaninka haka  kuke kuka ? ."

hannunta umma  ta riqo suka nufi bangarenta Aunty salma  dake tsaye taga wucewarsu maryama na goge kwalla tasan ba lafiya ba  ta biyo bayansu da sauri umma   ta zaunar da ita  a Kan kujera ,a lokacin kukan nata ya fara raguwa"me ya sameku  haka kuke wannan uban kuka haka maryama ? Jin shirun da tayi ne yasa aunty  Salma   ta tunzura "wani mahaukacin tsawa ta sakar mata wanda sai  da ta burkice  "wai  ba magana ake miki ba ne?sai lokacin umma tasan da shigowarta ta dago tana kallon tana mamakin hali munafurci irin nata ko wa ya kirata data shigo ? umma ta hade rai tana cewa    "a'a salma   ba haka akeyi ba ki barni daita kawai karki hargitsa mata lissafi ki barta zatai magna."

"uhm ina jinki maryama fad'a min damuwarki cikin sheshekar kuka ta zayyanewa umma komai da ya faru naunayen ajiyar zuciya ta sauke "gsky bata kyau ba , amman  Kiyi  hakuri ita rayuwa ta gaji haka komai da  kika gani  kafin a samu nasara sai anyi  hakuri   in sha allahu wata rana zai zama labari ,ku ya kamata ku dinga kwantar wa da mahaifiyarku hankali ba wai ku dinga tayata kuka ba yi hakuri kinji maryama   Ki bar komai a wajen Allah in sha allahu sai kin zama madubi abar dubawa acikin gidan nan masu takaki wata rana sai  sun zama fadawanki "wallahy aunty aseeya  har da laifinki wajen iskanci yarinyar nan kawai daga yar wannan mgnr zasu zauna suna kuka Kmr mutuwa akayi ke km   sai  ki zauna kina  bata lokacinki ."

" babu ruwanki dole na rarrashi diyata  mikewa tayi ta fice cikin fushi umma tabi bayanta da kallo karki qara damuwa da sharrinsu idan kina kuka suna ganin rauninki to kin shiga matsala dan kullum da abinda zasu dinga miki amman idan kika jajurce kece zaki ga rauninsa ta fad'a hk tana goge mata fuska da gefen zaninta  "kin ci abinci ma kuwa ?ta girgiza kai alamun a'a to maza jeki ki rarrashin mahaifiyarki da danuwanki ki dawo ga abinci kizo kici ta mikar daita ta rakata har bakin kofar fita  da kyar ta fito zuwa bangarensu wanda lokacin tuni aunty ta daina kuka suna zaune da habib  tana gama shigowa taji  saurin muryar Aunty  "my princess taho kici abinci nasan kina tattare da yunwa."

Babu yadda ta iya ta sakar mata murmushin gefe baki  tana dubanta tace  "kamar kin sani Aunty gbdy suka qarasa  zuwa Kan kujerun roba dake zagaye da qaramin table wanda shima din na roba ne aunty na zaune tare da yaranta suna cin abinci amamn ita  tayi shiru tana tunani  ta kasa cin abinci "male kici abinci mana ta dago ta kalli habib maryama ta ajiye spoon din hannunta ta soma magana a tsanake kamar ba yanzu ta gama kuka ba."
Chapter 38 · 0% Book details