← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 9 OF 100

Sashe 9

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Kai tsaye mota ya shiga muhd bello na ganin haka Shima ya shiga bangaren daya shiga ya zauna suka bar gidan har suka hau kan titi nasiha m b ke masa me kwantar da hankalinli da ratsa zuciya sai dai ko Daya Adam bai jin zai iya saduda da auren maryam gabadaya ya maida idanunshi yana kallon motocin dake gudu akan titi yayinda kwakwaluwarsa ke tunanin neman mafuta dan dole yasan abun yi kafin ayi masa auren dole da yarinyar nan "
"Adam ......"!
M.b ya kira sunansa ko gezau bai yi ba bare ya nuna alamun mutun na kusa dashi bai tsaya jiran jin amsarsa sa ko akasin hk ba ya cigaba da magana "ka kasa fahimtata amman kayi hakuri kasanyawa zuciyarka sallama ,na fahimci yadda kake ji amman me kake son nayi daya wuce na tayaka yiwa mahaifiyarka biyayya ? yayi maganar kmr zai yi kuka dan ya tsani yaga damuwar amininnasa ya dafe kanshi da hannunsa daya yana dukar da kanshi tausayinsa ya kama Adam ya furzar da iska me zafi daga bakinsa sannan ya soma magana .

"MB nima ka kasa fahimtata ne amman Ina da ra'ayina akan mace da nake son na ajiye agidna , muddin na auri Maryam ya zama dole na qara aure abinda bazan so faruwarsa kenan ba bama haka ba ni bani da ra'ayin ajiye mace sama da daya a gidana ."to meye dan ka ajiye sama da daya ? ka Kara mana tunda kana da abinda zaka iya rike mata ko sama da goma ne ba biyu ba ."
tsaki Mr ATA yaja a lokacin da direbansa ya karya kwana yana cigaba da tukinsa ,motar tayi shiru can ya sake motsa bakinsa "mb kasan komai akaina sai dai abinda bakasani ba ni bana son auren farar mace, nafi son mace chocolate colour ita ba fara ba ita ba baqa ba sannan mara kiba wace matakin karatunta iya diploma ne sannan doguwa daidai kafad'ana ba guntuwar mace ba "Kai yanzu me zakayi da doguwa har kafad'arka sbd Allah? " yar daidai fara kmr maryam ai ta isheka rayuwa sannan a matsayinka me zaka yi da mai iya karatun diploma ga mai digree har biyu "

"Zanci master's ne ? yayi masa tambayar a matukar fusace "yariyar nan babu abinda ta iya common ruwan zafi sai an daura mata ga balain son social media ,Kai ni duk bama wannan ba na tsani farar mace arayuwata ni dai chocolate itace type dina kasan Allah dana yi rayuwa da farar mace sol irin yarinyar nan gara na mutu ban yi aure ba saboda na tsaneta "subhanallah ATA ka daina fadar haka dan allah , dukkaninsu halittar Allah ne , da baki da fari duk Allah ne ya haliccesu ya tabe baki kawai yana furzar da hucin numfashi mai zafi haka suka cigaba da tafiya m.b na nusarsheshi ."

Maryam yan'uwa ne da adam, da mahaifin maryam da mahaifiyar adam uwa daya uba daya maryam ce babbar diya agurin iyayenta sai kanwarta Faiza ,islaha manir , Abusufyan , Salman sai auta izzatu wacce suke kira da izza suna zaune a Abuja yayinda adam suka kasance su biyar agurin mahaifiyarsu aunty shahida itace babba Kuma ma'aikaciyar likitanci ce a babban asibitn gwanaty dake jahar lagos a ikeja ,sai aunty khadeja wacce ta kasance maaikaciyar zenith ,sai adam wanda ya kasance dan boko Kuma rikakken dan kasuwar da duniya ke ji dashi,sai aunty zabiba wacce ta kasance lactura ce a lagos state university, sai auta nana hauwa'u wacce tuni itama ta gama karatunta a London tare da maryam akan harkar compurte science , a london akwai tsananin shakuwa atsakanin nana hauwa'u da maryam Hakan yasa sanda suka kare karatu maryam ta kasa zama tare da iyayenta ta dawo suka cigaba da rayuwa gabadaya dangin mahaifiyarsu da mahaifinsa babu baki duk wanda kagani fari ne sol babu mixed ."

Direban mr ATA bai tsaya akoina ba sai a haraban asibinti da aunty shahida ke aiki yana parking ya fito da sauri ya Bude masa murfin mota mr ATA ya yunkura da kyar ya fito yana gyara zaman rigarsa "friend ka bani minti ashiri yanzu zan dawo "na baka awa daya ma har ya juya m.b yace " , dan Allah friend karkayi wata ja inja da aunty kawai kace mata ka amince wani banzar kallo mr ATA ya juyo ya banka masa sannan ya juya cigaba da tafiya ."
m.b yayi murnushi dan daman yasan sai ya samu tsaraban wannan kallon daga gurinsa kai tsaye office dinta ya nufa cikin takun nan nasa mutane sai kallonsa suke saboda hotunansa sun qarade koina na matsayinsa na dan kasuwar da duniya Ke ji dashi wasu kuwa tsananin kamaninsa da yaruwarasa yasa suka dinga kawo masa gaisuwa wasu ya amsa Wasu ya share barin ma idan ya fahimci yanmata ne , ya tsaya a bakin office dinta yayi knowking ta bashi izini ya shiga yana taku da kyar yana furzar da iska ."

ta dago da sauri ta kallesa tana nuna masa gurin zama Dan tasan Halinsa ba karamin aikinsa bane zuciya tasa ya juya ya kama gabansa "zauna na Dan karasa abinda nake zama yayi ya daura kafarsa Daya akan Daya Yana ciza gefen lips dinsa daya zame masa jiki .byn kmr minti biyu ta tsaida abinda take ta sake dagowa ta zuba masa idanunta "Ina sauraronka wani taimako zan maka ?"kisa a fasa auren nan kawai shine babban taimako da zakiyi min ". "me yasa kake kin auren marym? shin kana da wacce kake so ne data fi Maryam komai ?ya gyada mata Kai alamun "eh ! Yana lumshe idanunsa "a Ina take Kuma su waye iyayenta ?wani mataki iyayenta suke dashi a kasar nan ko ....."? Ki tsaya iya haka ma ya isa dan ban San komai daya shafeta ba sbd ban San komai nata ba , Ina take a ina zan ganta duk bansani ba ina dai kan nemanta sai ki tayani da addua Allah yasa na ganta nan kusa kuyi min auren soyayya idan ma soyayyar zanyi kenan ."

"aunty shahida na San idan na fada miki komai zaki fahimceni sbd akwai fahimta a tsakankanimu shiyasa kika ji Ina maganata Kai tsaye dake , a zahirin gsky matar da nake so na aura ni kaina na dade Ina nemanta sai dai har yanzu ban ganta ba ......"nifa ban gane nufinka ba Adam , " I mean matar da nake so ban San Inda take ba ya sake maimaita mata abinda yace "Amman dai ku bani lokaci zan cigaba da nemanta idan na ganta zan kawo muku ita ya karasa maganar tare da fito da pendat din sarka dake makale da wuyansa wanda ke hade da hoton zannen yarinyar ya nuna mata ."

Shiru tayi tana kallonsa da kallon zanen yarinyar kyakkyawa ce chocolate colour " kinganta aunty ita ce rayuwata , ni dai kaina na zanata akanta na koyi Zane , ta miki kyau ko ?yayi mata tmyr yana sakar mata tsadaddaden murmushinsa wanda ba ko yaushe yake yi ba "subhanallah Adam kana hauka ne ko me ?" Taya zaka kamu da soyayyar macen da baka San Inda take ba hasalima baka taba ganinta ba ....?"Haka ne aunty Amman ta shiga zuciyata ta samu kyakkyawa mazauni acikinta shekara goma sha biyar kenan nake nemanta aunty babu Inda ban nemi yarinyar nan ba acikin garin Nan har ma da kasashe da garuruwan da nake zuwa Amman ban sameta ba ,Kai ko me kama daita Bangani ba "shine Kuma Dan hauka ka cigaba da Sonta? "ya lumshe idanunshi tare da cewa "ya zanyi haka tawa qaddarar ta kasance itama ba wai ina sonta bane amman muddin zanyi aure ita zan aura".

"ka manta wannan shirmen dan har abada bazaka ganta ba dan dayawa mafarki ba gsky bane "wallahi aunty jikina na bani tana Nan a duniyar Nan shiyasa kika ga bana son na karbi auren yarinyar Nan mrym gbdy aunty shahida ta dauke maganarsa a matsayin shirme ta cigaba da kallonsa kmr wani sauna ,Taya zai ce yayi mafarki da mace Kuma Yana Saka ran tana Nan acikin duniya Kuma zai aureta sai Kuma tayi tunanin ko aljanu sun shafesa ne a take agurin tace "Adam ka sausarareni da kyau mafarki baya zama gsky ..."no aunty wannan zai zama gsky yayi mgr a fusace .... "
jikinta yayi mugun mugun sanyi ta ajiye nata damuwar ta fara lallabashi dan taga alamun idan ta cigaba da mgn komai zai iya faruwa dan ya zurfafa soyayyar yarinyar sosai ya mike tsaye "ki taimakeni ki fahimtar da sweetheart ku tayani da adduar samota "aikuwa zan fada mata, a ranta tace babu adduar da zamu tayaka tunda mun san abinda muke yi har ya bar office din bata dauke idanunta akansa ba ...."

Washegari aunty shahida ta shirya ta samu hjy zulai "ta Koro mata duk halin da adam yake ciki" mu tashi da addua mami saboda Adam yayi nesa cikin wata duniya ,hjy zulai ta gyada Kai cike da matsanacin fargaban tace "Allah kyauta inshallahu zan tashi tsaye da addua da Kuma sadaka lallai da alamun aljana ta auresa idan ba haka ba ga lafiyyayar yarinya me zai Yi da wata a mafarki "shine abinda nayita kokarin na fahimtar dashi yaki yarinyar Nan tunda ta taso bata da matsala ke din mahaifiyarta ce zamu shiga gidansa a duk sanda ranmu yaso, Kuma zamuyi abinda muka ga dama tunda ta muce ita ."
"Allah yasa ya gane alkhairi ake binsa dashi "Ameen aunty shahida ta fada tare yiwa mami sallama har wannan lokacin Babu Wanda ya sanarwa Maryam batun aurenta da adam ana jiran sai ya amince sannan a tunkareta da batun cikin saa da jajicewar mahaifiyarsa da yayarsa mr ATA ya amince a wanni yammaci sun dade a dakin suna tautaunawa ya numfasa idanunshi a runtse ya cigaba da magana "Amman fa duk sanda na samu yarinyar da nake nema zan Kara da daita "ai wannan ba wata damuwa bane inji cewar aunty shahida ta fadi haka ne sbd tasan da wahala ya samu yarinyar mafarkinsa ita kuwa mami shiru tayi tana kallonsa a karshe ta girgiza Kai tana masa addua acikin ranta ."
Chapter 9 · 0% Book details