← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 53 OF 100

Sashe 53

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Su iyaye ne zasu iya yin komai suci lafiya a yanayin yadda rayuwa tazo miki cike da rudanin  yaci ace zuwa yanzu kin samu y'anci ki tsinci kanki cikin  farinciki da jin dad'in rayuwa kwana uku kawai da baki ga walwalata ba kin daga hankalinki inga bana cikin gidan nan ?"ina ga nabi wani na barki ya zakiji ? wallahi iyayenki suna can cikin tsananin kewarki kwatankwacin yadda kike jin namu da zaki koma garesu zasu karbeki su kuma yafe miki " kiyi hakuri aunty ki daina ganin laifinsu ta karasa fadar haka tana xubda wasu zafafan hawaye hade da rike hannun aunty gam tana me tausayawa rayuwarta ."

"Idan abubuwan dake faruwa suka cigaba da faruwa bana tinanin zuciyar dake kirjina zata cigaba da baguwa ni dai ki koma cikin yanuwanki dan Allah ki roki gafarar iyayenki su yafe miki mu cigaba da rayuwarmu kamar yadda muka saba . ahankali aunty tashiga bubbuga bayanta "kukan ya isa haka
Inshaallahu zan .. zan.. koma garesu da izinin Allah sosai aunty ta dinga rarrashinta da gaya mata maganganu masu dadi da sanyaya rai har  ta soma bacci ajikita cike da samun kwanciyar hankali .

Washegari kowa yasan maryama na cikin kwanciyar hankali wanda hakan ya kwantar da hankalin babib da aunty tare suka ci abinci kamar yadda suka saba ,maryama tana zaune a falo byn tayi wanka ta shirya tana kitsa gashinta gida hud'u sakina ta shigo suka sha hirarsu duk aunty na jinsu sosai taji dadi aranta ganin maryama ta saki ranta ,har sakina ta fita ta dawo "maryama amman yau zaki islamiyya?"eh!zani idan na gama zan biyo miki sakina ta qarasa fita ita kuma ta mike ta shiga daki tai sallah ta qara shiryawa ta dauki alqurani ta fito ta tsaya a bakin part dinsu sakina tana jiranta byn ta gaishe da aunty salma sakina ta fito ta tsaya kusa da maryama tana mata magana kasa kasa aunty salma ta bisu da harara har suka fice ,ta nemi guri ta zauna zuciyarta na tafasa ."

ta rasa yadda zata kawo karshen shakuwar sakina da maryama duk duniya bata da abinda ta tsana tamkar maryama tayi shiru cikin tsanani tunani abubuwa da dama take sakawa in dai da rai da lafiya sai ta rabasu domin itace kadai hanyar da zata nunawa maryama tsangwama da tsanar datayi mata shegiyar yarinya kamar mayya ko aljanna zatace banda abun sakina ai maryama matsala ce arayuwarta, yanzu ko saurayi idan sakina tayi yayi ido biyu da maryama ai tuni zaice shi ga wacce yake so yarinyar ta cika kyau haka kamar ita tayi kanta ta fad'a acikin ranta ta mike tsaye cikin takaici to ko afa zata kaiwa kukanta , zuciyarta ta kawo mata dauki da wannan tunani aikuwa hakan shine mafuta afa shine zai kawo mata karshen komai da karshen wannan shakuwartasu mayafinta ta dauka ta yafa ta fice daga gidan tana surutai ita kadai kamar yadda na shiga na fita na rabaki da duk wanda yazo da sunan yana sonki da aure yanzu ma sai na rabaki da sakina takowani hali ki cigaba da rayuwarki Ke kadai Kmr mayya acikin gidan nan ."

Tayi sallama aka amsa mata daga ciki dan haka ta shiga ta tsaya afa da yake ciki bai amsa ba yayi gyaran murya hakan ya tabbatar mata akwai wani aciki ta dan jira na rabin awa sannan wacce take ciki ta fito suka gaisa ta fice a karo na biyu tayi sallama ta shiga cikin dakin ta durkusa ta gaishe shi yana zaune akan daddumar sallah wani katon tray mai cike da katon kasa da wuri na duba ya amsa mata cike da kulawa "meye ma sunanki yaushe rabon na sakaki a idona ?"Aunty salma tayi murmushi tace afa kenan abine sai ahankali idan ka ganmu tamu ce ta kawo mu yayi murmushi ya dan shafa gemunshi yana lashe lebensa "to ina jinki fara bayanin abinda Ke tafe dake kafin na duba naga gskyar lamari ".

Mmm sudais
💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura wa wannan 0913691 8331  alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

        Page 15

"Aisha ,  saber, da   mahamud ,  ta  gani   tsaye  akansu  suna   huci   kamar   zakuna  cikin  matsanamcin  tashin  hankali   mara misaltuwa  suna   kallonta   kamar   zasu  cinyeta  ai  babu  shiri  daga  bilkisu  har  ussein   suka   mike   daga   jikin   juna  hankalinsu yayi  mugu  mugun   tashi   ."

    bilkisu  ta  tsaya  tana  kalle  kallen   inda  zata  boye  acikin d'akin  tare  da  cure  hannayenta  waje   d'aya  jikinta  na sake d'aukar  rawa  bata  ta'ba   shiga  tashin  hankali  da  nadama  irin  na  ranar  ba domin  har  ga  Allah  bata  ta'ba  tunanin   zasu   bibiyi takunta  ba ."

Nan da  nan  idanunta  ya   kawo ruwan  hawaye ba  tace  komai  ba, ta    durkusa qasa  bisa  gwiwo
winta   dan  tasan  sai   na  lahira  ya  fita  jin  dadi  mahamud  ya  rike  kungunsa  yana  cigaba  da  kallonta  ,mamakinta  kawai   yake  dawainiya   dashi  idan  aka  fad'a   masa  cewar   zata  biyo  nmj   har  d'akinsa   bazai  ta'ba yarda  ba,  watakilla   ma  da  sai  ya  wankawa   wanda  ya  fad'a  masa  hakan   mari  "dan   girman  Allah  kuyi   hakuri   ku  yafe   min  ku rufa  min  asiri   kar  mumy   tasani  ta  karashe   mgnr   tana   kuka  cikin  tashin  hankali mahamud   ya  buga  mata  wata  razananniyar  tsawa  data  hargitsa  mata  lissafi "yi  min  shiru  makira  bana  son   jin  komai  daga  bakinki ."

nan   take   tayi   shiru  kukanta ya  qaru ta   kalli  inda  ussein  yake  tsaye    shima   kana  kallonsa  kasan  baya  cikin natsuwarsa  "mahamud   tsayawa  kayi  kallonta  bazaka   fara cin  ubanta  tun  anan  ba ?  Aisha  ta  fad'a  tana  mata  wani   irin kallo  shi kuwa wanda aka kira  da  mahamud  tunanin yake  idan  yace  zai  ta'bata to  babu  shakka  zata  mutu  idan kuwa bata  mutu  ba  zata  jikata ."

"dan  girman  allah  Aunty ai.."ai  bata  kai  ga  fad'ar  abinda  take  son fad'a  ba  taji  wani   gigitaccen mari   hagu  da dama akan  kuncinta "you  are  very  stupid   bilkisu  , akanki  aka  fara  soyayya?"  kin  haukace  kin  makance  akan  wannan  banzar  ,me  yasa zaki  mance  ko  ke  wacece ?  wato soyayya  tasa  kin  manta  matsayinki ? cikin  muryar  kuka tace " a'a   Aunty  aisha   ban   mance   ba  amman  kuyi  hakuri  wallahi  bazan   sake  ba  "hayaniyar  yan   yan'uwanta  ya sake   d'aga  mata  hankali   shi kuwa   ussein  sunkuyar  da  kanshi. kasa  yayi   yana  tunanin  ficewa ya  bar  d'akin  dan  yasan Allah ne kawai  zai   kwacesa  a  hannunsu ."  

Kai   tsaye   bilkisu   ta  nufi   bayan kofa  ta   boye  jikinta  na  wani  irin rawa  sakamakon   jiyo  muryar hajiya  rahma  tana  cewa "ina bilkisu  take  naga kun  tsaya  jugun   jugun  ko  ta  gudu ne ?  kafin  kace  me  an  samu  wanda   yazo ya  fad'a  mana   halin   da'ake  ciki a guje  na  bazamo  na   bar  hajiya  dan   bazan  iya   jiranta   ba kasancewar  tana  fama da  lalurar  ciwon kafa ."

" ina  tafiya  ina  neman layin  yan' uwansashi   da  kyar  na  samu ta  abban  sadam  yana  gama  jin bayanina  cewa  yayi  babu  ruwansa  dan  yasan  halinsa da tara  yammata , babu  yadda banyi dashi  ba yace  bai  zuwa  koina  ya kashe  wayarsa  jin abinda  ya fad'a yasa  na  kira  yayyensa   mata ."

Ina   shiga   unguwar  naga   jamaa  sun   yi   cirko   cirko!!  ga   manya  manyan   motoci  na  gidansu  bilkisu  jere a  kofar  gidan ,haka  ina  shiga   cikin  gidan  mutane  na gani  makil   kowa  na   fadar  albarkaci   bakinsa ,yayinda  muryar   mahaifiyarta  ya  karad'e  koina   acikin   gidan   "da  gaske  ne  bilkisu   tana  cikin wannna  ru'babben  d'akin ? Aisha ta  nuna  mata   bayan   kofar d'akin  "tana  ciki   kuwa  ga  makira  nan a bayan  kofa   ta  fad'a  tana   zubar  da  hawayen  takaici  ."

"inna  lillahi !  hjy  rahma ta furta  a fili  cikin  tsananin  tashin hankali "kunji   abinda  naji  kuwa  wallahi  ji  nayi   zuciyata  kamar ta  buga ?hankalin  bilkisu  ya bar duniyar da  muke  alokacin  dan  sai  wuri  wuri  da  idanu  take  shi  kansa  ussein kana  kallonsa  kasan  nadama  ne  acikin   ransa  nadama  irin  wacce bata  da  wani rana ."

" amman  bilkisu  bakince  min kin rabu  dashi  ba  ?jikinta  na  rawa ta  shiga  gyada  mata kai  alamun Eh! tana   bawa mahaifiyarta  hakuri  da  wani  irin  fushi  ta  juya  inda  ussein  yake   cike  da  nadama ta shiga  zabzabga  masa  mari  ta koina "bana  ce maka  ka rabu  mun  da  yarinya ba  ? ba  banace karka  sake   shiga   rayuwarta  ba?"Ko kaga  yarinyata   tayi  kalar  wacce  zaka ce  kana so ? ta  juya  zuwa  ga  bilkisu  " Ke yanzu  har  wannan  qazamin  ne  abun  so  a wajenki  ? ta  fad'a tana sake   juyowa ta  d'aga hannu  zata  sake  tsinkawa  ussein  mari  nayi saurin   rike   mata  hannu  ina bata hakuri  "kiyi   hakuri  hjy sam  ussein  bai  kyauta  ba  daya  bawa  yarinyarki damar  zuwa  inda  yake  ,ya  karbi laifinsa  ayi  masa  afuwa   in sha allahu  hakan  bazai  sake   faruwa ba   Kinsan   kowa da irin jarabawarsa  dukkanin  rayuwa  rubutaccen   lamari ne daga  Allah ,kuma   kowani  dan  Adam yasan  da  haka  ,yanzu  tunda  abun  ya  zama  haka ku bamu  dama  sai  mu  turo ayi maganar  aure "."

Wani  irin  kallo  gabadayansu suka  bini  dashi  ,hjy  rahma  tace  "Allah ya  tsareni  na   had'a  zuria da wannan  ta  nuna  ussein  da  yatsanta  tana  hararsa "wallahi   bilkisuna  tafi  karfen  aurensa  ki kalleta  sama da qasa  ki  kallesa ta  ina   hadin yayi daidai  ?  duk  nasan  da  haka  hjy  amman  a wajenta  shine daidai    bugu da qari   rayuwar  yarinyar ku  zaku duba  domin  ita  diya  mace ce zata  iya fad'awa  kowani hali ."

"Ba kowani  hali  zata  fad'a ba ko  mutuwa  zatai  sai dai ta mutu na yarda  na   rasata   gbdy  akan na bawa wannan   matsiyacin aurenta ta  numfasa  tare  da sa  tafin hannunta ta  share hawayen idanunta  "hjy  ki  daina furta  haka  shi  soyayya   allah ne  yake had'awa  , kuma  babu  ruwan soyayya  da  tsiya ko arziki  yarinyar  nan tana  qaunarsa  shima kuma  yana  sonta dan  girman  allah  ki  barsu  suyi  aurensu  kowa ya huta  sannna  babu  wanda  yasan matsiyaci ko  mai arziki  sai Allah  sannan babu wanda  yasan mai gobe  zata  haifar  ku barsu  su  aure juna   domin   samun  kwanciyar hankali ."
Chapter 53 · 0% Book details