← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 64 OF 100

Sashe 64

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Shigowarta  kenan  daga  wani  kamfani  kai  zanenta domin  tallatawa  ,da  baba gali ta soma ci karo "yar gwal  idan kin huta ina son magana dake dam taji gabanta  ya  fadi  tun da take arayuwarta bata jin ranar da baba gali yace yana son magana makamanciyar   haka  ba  km  wai  yar gwal  yana son  magana  daita  tabbas  akwai  mahimmiyar magana , bata kawo komai aranta ba sai tunanin watakilla ko mgnr mlm yahuza ce tayi karfi tunda ya sha fad'a mata yana son manya su shiga ciki ta nufi bangarensu ta kammala komai nata  a natse ganin shima ya fita masaalaci tayi sallah har ishai sannan ta dawo parlour ta zauna zuciyarta na tunanin akan maganar da baba gali zai yi daita duk da bata san abinda zai sanar daita ba amman sai maganar ta tsaya mata arai cike sa  fargaba ."

Karfe tara daidai  umma ta aiko  a kirata  ita da aunty   nan fa   gaban  maryama   ya cigaba  da fad'uwar da yake , tare suka  fito  da aunty  alokacin shukura ta shigo daga zance tuni aunty ta wuce dan har ta kusan  isa  bakin side din  umma, haka nan ta kalli shukura dake  zaune  kusa da aunty salma dake cin abinci  atsakar gida ta sake gaishe da aunty salma ta wucesu ta shiga bangaren umma ta gaisheta cike da girmamawa  umma taji dadi sosai ta tmbyi lafiyar habib ."

shiru ne ya biyo  baya har na kusan mintuna asirin sai ga aunty salma da aunty  hassana sannan byn an gaisa umma  ta numfasa tace "Maryama wata tmby nake son nayi miki game da yaron nan dan gidan lawan yaro ?"dam  taji bugawar da qirjinta yake ya qaru , tayi shiru domin bata damar tmbyrta ta cigaba da magana "tsakanin keda shukura wa yace yana só né ?"

Maryama  tayi shiru lokacin da maganar ta doki dodon kunneta wannan  wace irin magana ce akwai abinda  umma batasani ba a tsakaninta dashi ?amman  dai koma menene  batasan abinda yasa take mata  wannan tmbyr ba, ta bude baki zata bata amsa abinda Ke tsakaninsu sai kunya ta hanata tayi kasa kawai  idanuwanta "Maryama tmbyrki nake baki ce komai ta  sake yin  shiru a karo na biyu tana son jin ba kece wacce kuka fara son juna ba har yake zuwa zance wajenki ba ? ta sake yin shiru tana son bata amsa sai dai bazata iya sanar daita ba tunda gashi ita da kanta tasani   kuma tana da masaniyar wajenta yake zuwa, ita me yasa umma zatayi mata wannan tmbyr akan abinda ta rigada tasani tunda sau tari ita ke cewa taje  idan yazo bata son fita ."

"Abinda yasa na kiraki nake tmbyrki shine dazu da yamma byn fitarki kai  zane  yan gidansu sunzo domin auren diya a gidan nan kuma sun bayyana wacce suka zo nema ni da azatona kece yahuza yake zuwa wajenki ashe yaruwarki shukura  yake so ."
ba idanuwanta  ba hatta numfashinta da kwakwa luwarta sai da suka daina aiki wani tsayawa tayi na wani lokaci kafin ta sauke naunayen ajiyar zuciya  ta juya idanuwanta kana  tashiga   tunani da kwakwa luwarta batace komai ba saboda tashin hankali daya risketa ta sunkuyar da kanta qasa kawai  tana jin damuwa mai tsanani "

"Magana nake maryama kinyi  shiru daman bake yake nema ba yauruwarki yake nema ?ta qara yin mata tmbyr bata san abinda zatace ba ganin zata batawa kanta lokaci da jama'ar dake wajen yasa ta dago kanta tace "tunda shi da kanshi ya sanar da wacce yake nema ai babu laifi umma , umma tayi shiru kawai tana dubata ina son gane abun ne domin ni a tunanina Ke din ce  yake zuwa wajen ki kawai ta dago tace "ba wajena yake zuwa ba wajenta yake zuwa tana gama fadar haka ta mike da sauri dan zamanta a waje zai yasa ta zubar da hawaye ta bayan bangarensu inda aunty Ke aiki ta labe tana kuka mara sauti dan kar wanda ya ganta ta tsaya anan ta rarrashin kanta ne dan karta dagawa  danuwanta hankali."

Sai datayi mai isarta sannan  ta fito ta shiga falo kai tsaye  ta wuce habib  dake  zaune yana  kallon ball dakinta ta shiga ta kwanta lamo akan katifa ahankali kalaman mlm yahuza daya dinga furta mata suka dinga dawo mata cikin kwakwaluwarta  da taimakonsa  gareta  hakika  bazata   ta'ba  mantawa dashi  arayuwarta ba ta  dinga  girgiza kai shikenan shima ta rasashi  ,hawaye  suka dinga zuba daga idanunta bata san tana shesheka ba sai dataji muryar  habib  yana cewa "kamar shesheka nake ji heartbeat  tayi  saurin  gyara kwanciyarta tayi shiru tare da lullube kanta tana tunani abinda ya kamata ta fad'a masa  idan ya qaraso gareta domin dai abinda yake gudar mata kenan gashi ya faru daita  ta runtse idanunta sosai alamun ta fara bacci ganin hk habib ya juya ya koma falo ."

Bangaren umma kuwa gyara zama aunty  tayi ta kallesu "hakika  bakuyi adalci ba  saboda ni nasan wannan yaron wajen maryama yake zuwa me zai sa shukura zata qaunaci wanda yake son maryama har ku iyayenta kusan hanyar da kuka bi kuka raba maryama dashi ?mgnr  tayiwa ummah dadi ko babu komai yau zata gwada kunjinta akan damuwarta
Aunty salma ta gyara zamanta itama tasoma magana Kmr tana jira "kada a kawo maganar rainin hankali acikin maganar nan kina tunanin shukura zatace tana son shi ne ?".

"to kisani diyata bazata ta'ba cewa tana son wani ba shine da kanshi yace yana sonta kuskure yayi yace yana son maryama dan kawai ya samu hanyar da zai ce yana son shukura bude kunnuwanki da kyau yahuza ya dade da soyayyar shukura acikin ranshi nauyinta kawai yake ji dan hk ya fara gwada soyayyar daga kan maryama ganin bata da wani matsayi da aji ya dawo hanyar madaidaiciya ba kuma diyata tace tana son shi ba idan kuma har abun ya dameki sai kisa diyarki ta sameshi kice ya daina son shukura ya dawo kanta."

"Uhm kawai aunty ta furta a fili  sannan a fili   tace allah kai ne allah kai ka kawo ma maryama yahuza amatsayin wanda yake sonta  byn ta rasa sauran kuma na tabbatar yahuza yana son maryama da gsky Allah kai kasan abinda akayi  aka shiga tsakaninsu ya Allah kayi mata sakayya  nasan zaka kawo mata wani wanda ya fishi   komai   "Wai me maganarki take nufi ?kina nufin an kwacewa maryama saurayi ne ko me ?"wannan ai gskyr da kowa ya rigada yasani ce maryama  yake so kuma dan ita yake zuwa gidan nan ,na rasa wannan maseefar babu damar aga maryama da cigaba duk yadda zaa yi sai anyi an rabata dashi ".

"Dakata dakata!!  su waye dasu waye idan zakiyi mgnrki Kiyi mgnrki a inda bazai zame miki damuwa ba , ina maryama take ?me ye tafi sauran mata  da idan ta samu cigaba ake rabata dashi ?ita din gwal ce ko me ? inji cewar aunty hassana "tunda yaro yace ga wacce yake so ai magana ya qare sai ayi shirin aure "a'a hasaana wannan ba magana bace  allah baya son zalinci kuma baya son wani bawan yayi ,hakika idan akayi auren nan an zalici maryama "umma ki rabu dasu hassada ke damunsu akan maryama ,amman maryama din da kuke gani tafi gwal wallahi kuma kaf zuriarku babu macen data kaita allah na tuba idan nayi alfahari  ka yafe min ba alfahari nayi ba gsky na fad'a ."da sannu  hassadar  zata cinyeku  ni natashi  allah ya bamu alkhairi  allah yayi mata zabin abinda yafi zama alkhairi arayuwarta da izinin allah maryama sai ta kawo maku wanda bazaki iya kwacewa ba tana gama fadar haka ta mike ta bar falon ."nan fa hayaniya ta kaure aunty hassana na zaginta aunty salma na qarawa ummah kuma tana basu rashin gsky ."

Aunty ta  shigo  parlour'n  tana  kuka  nan da nan hankalin habib ya tashi ta wuce shi ta nufi dakin maryama tana kwance  har lokacin tana zubar da hawaye  tana tuno daddan kalaman mlm yahuza gareta atare suka fad'a  dakin  ta qarasa ta zauna bakin gadon ta kamo hannun  maryama ta damke cikin nata jikinta  har ya  dauki  zafi  ta fashe da wani sabon kuka wanda yasa kukan maryama ya fito fili ta yunkura ta mike zaune  cikin  mawuyacin  hali tana cewa "why aunty ?me yasa kike asarar hawayenki akan dan wannan abun ? "duk fa abinda kaga  allah bai baka ba to ba rabonka bane Kiyi hakuri ki daina kuka  please cikin rawar muryar habib yace "aunty meke faruwa ,abinda kake gudu dai ne ya sake faruwa sun rabata da yaron nan yahuza yaron kirki "what !?"

"Wallahi habib sun rabata dashi wai shukura zai aura ba maryama ba amman babu komai  akwai allah  wani  irin ihu yayi yana kurma uwar ashariya  ya juya  maryama tayi saurin durowa ta rike masa hannu  ya juyo ya kalleta "ki sakar min hannu heartbeat  ba shukura ba hatta shi kansa mlm yahuza sai naci ubansa yau koni koshi girgiza masa kayi tayi "bashi da laifi nasan akwai abinda akayi masa domin da kunne naji  komai nan ta zayyana masu hirar aunty salma da yayanta akan  mlm yahuza, dan haka kasani mlm yahuza baya cikin haiyacinsa ,mlm yahuza mutumin kirki ne idan nace banji zafin rabuwa dashi ba nayi karya jikinsa a matukar sanyaye ya zame a zauna qasa ya dafe goshinsa da  hannunsa  daya  yana jin ciwon abinda ya faru" yanzu abinda shukura tayi mana kenan ya fad'a cikin jin haushin ,to ya zamuyi mu mun dogara da allah  aunty ta sake riko hannun maryamu "Allah yayi maku albarka a rayuwarku  ,allah ya baki miji na gari,  idan da rabo Allah ya juyo da hnkln yahuza  ya dawo gareki  ya kula dake ."
Chapter 64 · 0% Book details