← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 45 OF 100

Sashe 45

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Zuciyarsa  na zafi yace tashi muje ka  d'a zaga gari ko jikinta  zai  rage  nauyin  da  yake "ya fad'a yana jin tsantsar soayyarta na  ratsashi  koina  ajikinsa ya mike da kyar "ata  kayi  zauna  gida  wallahi  jikinka babu  kwari   "karka  damu  muje  kawai tunda kana tare  dani  bani  da  wata  matsala ahankali suka sauko falon  qasa   babu kowa a  falonta   farko da alamun mami  tana  falonta  na  uku yaso sheidawa mami  amman  yasan  zata  hanashi  fita  koina  dan  haka   ta  kofar  baya  suka  fice  dan baya son escourt dinsa su  bishi  ya zauna shiru a gefen hisham dake  tuki  yana ciza lip's  dinsa "ina muka dosa "?cewar hisham ".

muje    gra   dan   ina  ji  ajikina a irin  wuraren  nan zamu  samu muguwar yarinyar nan   "hisham  ya kwashe da  dariya  har da  dukan stearing mota shi  kuwa gogan ya hade rai a she a fili   yayi mgn ba "wai muguwar yarinyar nan wallahi ata baka  da dama
,yanzu  dai  wani gra ne  a kusa damu  ?mr ata yayi  masa  banza  ya maida kallonsa  gefen  titi yana kallon mutane da motocin dake kai  kawo "duk  da kaki kayi mgn bari muje ikeja gra nan ma shiru  yayi  yaki  cewa  komai  "gskiy ata ka iya  bada suna pricess ta tashi da  sarauniya  ta  dawo  muguwa"dan  allah  malam  ban son isknaci ka maida hankalinka ga tuki " ya fad'a  yana nuna masa gaban mota da hannunsa  "naji  amman  yanzu ace taki sa'a   ka ganta  a  zahiri zaka ganeta "wallahi  zan  ganeta ". daga haka bai sake yin magana ba  shiru motar tayi babu wanda ya sake cewa komai  har suka d'auki titin  ikeja ."

Ahankali   Ummah  da  aunty  da maryama  suke  tafiya a hanyar   fitowarsu  titin unguwarsu domin su dauki  hanya zuwa marcaz  duba jikin hafsat diyar aunty  fati , maryamah  ta  hango mlm yahuza ya nufo  hnayar  da  suke  da littafi a hannunsa  da alamar islamiyya zashi  tun daga nesa ya fara raragefen  alamun Kamala ya durkusa har kasa ya gaishe da aunty da Ummah tare da cewa "unguwa zaku né ? maryama ta d'an kallesa ta  d'an  basar dan kar aunty da umma su  fahimci akwai wani  abu atsakaninsu tace" rakiya zanyiwa aunty  tare da umma  zuwa bakin titi ."

" allah sarki ya sake durkusawa har kasa ya  gaidai  umma da aunty duk da yasan tahirin rayuwarta amamn  bai  ta'ba  sanya mahaifiyarta  acikin  kwayar idanunshi  ba  amman ya gane aunty ce mahaifiyarta  dan  ko dan yanayin tsawonsu iri  daya ne , mlm yahuza yayi murmushi yace "dan allah ku dan jirani  minti uku kafin ku isa titi ma na dawo amman dan allah karku tafi a kafa  Ummah  ta d'an yi murmushi tace "kada ka damu dan allah , kada ka wahalar da kanka ba  wani  nisa da inda zamu ba mu gode Kwarai da gaske ."

" a dai min Afuwa ina zuwa  yanzu  Ummah  tace tô shikenan mlm yahuza yayi murmushi ita dai maryama ta bisa da kallon mamaki dan bata san me yake nufi da kafin suje titi ya qaraso ba ummah ta dubeta cikin mamaki "wannan kuma wanene ? wallahi malamin mu né na makaranta islamiyya ummah  tayi shiru domin ta danyi zargin son maryama din yake itama dai marayam taso ta fada mata kasancewar bata boye mata komai amman ganin fadar bashi da wani amfani tunda da zarar ta amincewa mutun ya fara zuwa kwana biyu sai ya gudu batare da laifin komai ba ."

suna tafiya suna hira  har suka karaso bakin titin gwagulori wanda ya dawo sabon titi  a yanzu sakamakon gyaran daaka masa suna tsaye kawai sai ga mota ta nufo inda suke maryama tasha jinin jikinta domin dai tasan bashi da mota amman babu mamaki ko ta abokinsa ce yayi burki agabansu ya fito daga cikin motar "umma  ku shigo na kaiku har inda zaku "maryama shiru tayi mamaki ne ya damu zuciyarta tunda take bata ta'ba jin mlm yahuza ya dan burgeta ba sai yau sosai tayi farinciki da abinda yayiwa mahaifiyarta da ummanta ido kawai ta tsura masa ta cikin nikaf dinta tana kallonsa cikin farinciki shi kanshi ya fuskanci  hakan ."

ya zagaya ya bude masu  mota suka  shiga kafin ya zagaya bangaren direba ya jefa mata wani kallo mai nuna tsantsar so kawai itama ta tsinci kanta da mayar masa da murmushi suka wuce ita kuma ta koma gida duk da  abinda yayi mahaifiyata da ummah  a yanzu bata ji ta  fara jin mlm yahuza acikin zuciyarta ba amman  ta kudirce zata danne zuciyarta ta fara sauraronsa ."

Hud'u  daidai  ta shirya zuwa islamiyya bata tsaya jiran sakina ba  ta  kama  gabanta acikin aji sune na farkon zuwa ita da kawarta subai'a wacce suka qare karatu tare ahankali suke hira fitowar result dinsu kafin malamin da zai daukesu darasin qurani ya shigo sosai taso tayi mata hirar mlm yahuza amman ta kasa har aka cika a ajin mlm abbas ne ya shigo nan da nan suka fara karatu ita dai karatun yau dai tazo makaranta tayisa amman zuciyarta fal da walwala da irin farantawar da mlm yahuza yayi mata dan tana matukar qaunar mahaifiyarta da umma duk wanda yaga girmansu kuma ya mutunta matasu tô lallai zai samu wani babban matsayi acikin zuciyarta most especially mahaifiyarta tana tausayin halin data tsinci kanta ciki yana daya daga cikin abinda yasa ta d'auki komai nata da mahimmanci ."

"ta godewa allah ta kuma ta godewa mahaifiyarta da umman tare da  abban sadam domin sun tsaya akan ganin sun ingata rayuwarta da karatun boko da Arabic tun alokacin da take secondary babu wanda yasa rai zata cigaba da karatunta zuwa jamia sai gashi kwatsam allah ya taimakesu ita da subai'a sun samu scholarship daf da zaa tashi ta shigowar mlm yahuza makaranta  ,taso Kwarai ta gansa tayi masa  Godiya ta fito tana duddubawa ko zata gansa amman bata ganshi ba zuciyarta taso ta gansa farincikin da yasa  iyayenta  take son tayi masa godiya dan tasan dole zai ji dadi acikin ranshi ."

Bayan an tashi daga makaranta bai biyota ba kamar yadda ya saba sai dai kafin ta isa gida kanwarsa nafisa tayi saurin isa inda take daman kuma tasanta sai dai ba aji daya suke ba tana gaba daita sosai suka gaisa tare daita suka cikin gidansu inda suka iske aunty salma a tsakar gida  tana zaune tana waya ganinta tare da nafisa yasa aunty salma kashe wayar suka gaisheta suka wuceta suka shiga bangarensu maryama." suna shiga ta nuna mata wajen zama "nafisa ki zauna ga waje tayi murmushi ta zauna akan kujera ita kuma ta shiga dakin aunty ta duba inda aunty tasaba ajiyar kudi taci saa ta samu naira dari ta dauka ta fito tana cewa nafisa "ina zuwa ."

"nafisa ta mike ta biyota ina zaki bari muje tare maryama tayi dan Jim dan taso ta zauna taje ta siyo mata lamurje ta kawo mata amman bata da choice dole ta barta suka sake fitowa tare kai tsaye bangaren aunty hassana suka shiga tayi sallama ta isketa zaune tare da yaranta babu wanda ya amsa sallamarta bare ya kalli inda take bata damu ba dan ta saba "aunty hassana ina yini akwai lamurje?
"Akwai na nawa zaki tsiya "?amm.. na naira dari ne wani dogon tsaki taja "ai nasan bazaki canza zani ba daga na naira darin babu qari kullum ana waje daya baa cigaba ni  bani kudin ki shiga ki dauka ki bace min da gani ."

Zuciyar  nafisa ta cika da mamakin aunty hassana maryama ta mika mata kudin ta shiga ciki ta dauka suka fito ta mikawa nafisa gashi nafisa babu yawa "kai  haba ai babu komai ai danasan ma kashe kudinki zakiyi da tun farko na hanaki " karki damu ai ba wani abu bane maryama ta fada tare suka shiga bangaren Ummah duk inda maryama tasa kafarta nan nafisa take ajiyewa ta share wa umma gida ta gyara mata koina tare da nafisa suka fito zasu wuce aunty salma ta kirata cike da isa ta isa inda take "kije kiyi min shara "

"Shara !"
Maryama ta furta a hankali?eh ko bazakiyi bane kika tsaya kina maimata min abinda na fada ?zanyi ta fada a taikaice tare suka shiga bangaren aunty salma ta fara shara "aunty maryama kawo na share miki da sauri dan akwai abinda ya kawoni "? itama tashi jinin jikinta dan tunda suke da nafisa  bata taba zuwa inda take ba sai yau "no ki barni na share nima yanzu zan gama ta zauna akan kujera sakina da shukura suka shigo shukura  na ganinta ta washe mata hakora "nafisa yau kece agidanmu ?ta tambayeta murmushi ya sake bayyana akan fuskarta "eh nazo wajen aunty maryama ne "aunty kuma ?ta fada a rude "eh mana aunty ce ai maryama tunda zuciyar babban yayanmu ta kamu da matsanancin sonta dan har wani kirki ya kirkirawa kanshi dan kawai ya aikoni wajenta ta fada batare da wani shakka ba ."

shukura  batace komai ba ta zauna kusa da nafisa " inata son nazo gidanku amman ban samu damar zuwa ba saboda makaranta nafisa tayi murmushi "ai kuwa sai ki arawa kanki lokacin ki dinga zuwa gidanmu tunda yayana ya kamu da soyayyar maryama nasan naki  matsayin sai yafi nawa zance bai yiwa shukura  dadi ba dan haka kawai taji bata son wata halaka a tsakanin maryama da mlm yahuza haka kawai take jin rashin jin dadi aranta ."

Maryama tana gama shara ta fara kokarin wucewa yayinda nafisa take qoqarin mikewa shukura  kuma tana janta  da hira "kinga bari na isar da sakon da aka aikoni gobe ma hadu a islamiyya ta tashi tabi bayansa maryama suka jera har cikin falonsu atare suka zauna akan kujera nafisa na cewa "aunty nah "maryama tayi murmushi "kai nafisa da ki daina ce min aunty kullum fa da sunana kike kirana "ai yanzu komai ya canza baki ji yan karin magana ba sunce idan kidi Ya canza dole ma rawa ta canza nafisa ta fada tana dariya "ya karatu yanzu uzukin nawa ?maryama ta sauya magana dan bata son wata maganar soyayya mlm yahuza yayi mata mutunci Kwarai kuma ta yaba masa amman batu na soyayya bata jin zata iya
Chapter 45 · 0% Book details