← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 47 OF 100

Sashe 47

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Byn mintuna goma maryama ta fito daga dakinta  zuwan dakin aunty  duk jikinta a sanyaye lokacin aunty tana kan dadduma ta idar da sallah tana dai zaune  "aunty sannu da zuwa "yauwa my princess ya zaman gida ?ta gyada mata kai alamun Lfy!"ya na ganki wani iri ko akwai abinda me damunki ne ?tayi shiru kawai tana jin faduwar gaba "kin dan daura mana wani abu kuwa ?ta bude bakinta ahankali tana shirin bawa aunty amsa suka jiyo hayaniya shiru tayi tare da kasa kunne muryar baba gali ne ta mike da sauri jikinta har rawa yake ta nufi kofar fita itama aunty ta biyo bayanta a tsakiyar falon suka gansa tsaye tare da aunty salma da aunty  hassana sai hargagi suke tamkar wasu karnuka yayinda habib ya shiga kitchen ya dauko zabgegiyar takobinsa mai tsine ya koma bakin dakalin kofar fita  ya zauna  yana wasa  takobinsa ,aunty hasana ta nufo inda yake shi kuwa habib kanshi na kasa yana cigaba da wasa takobinsa  jira kawai yake suyi masa wata maganar banza ."

Aunty ta kalli maryama ta kalli habib tana bukatar qarin bayani cikin fusata aunty salma tace babu irin qare maku zagin da wannan tantirin yaron bai yi ba ta uwa ta uba har da ce mana dabbobi jakuna aunty hasana tace "da ubansa yake Shege dan Shegiya "da sauri ya mike yana zagayesu da takobi  kiiiii kake jin tsinin bakin takobi asimintin falon basu ba hatta aunty da maryama sun tsorata "kai ko ka fara shaye shaye ne ko meye ?"da sauri ya juyo kan baba gali da yayi mgn fuskarsa a tsuke alamun bai son ya kawo masa raini "dan ubanka da kake zare masa idanu ka dauka zamu ji tsoronka ne ?"

"a'a nasan bakwa jin tsorona kamar yadda nima yanzu babu wannan tsoron duk wanda ya nemi zaman lafiya ayi wanda yace sabanin haka yake bukata bismillah ni bazan bata bakina ba sassara mutun kawai zanyi na aika sa lahira ."ya fad'a yana tsoka takobi daidai kafar baba gali ."

Da wani saurin gabadayansu suka ja baya suna kallonsa da mamaki kamar yadda aunty Ke kallonsa "tunda ku kun zama ahlin sheidan bakwa jin wani yare sai na dabbobi bismillah  nima zan nuna muku akwai digon wannan dabbar ajikina  ,tunaninku me zakuyi da kuka wani kwaso jiki gbdynku kuka zo ?
"To wallahi  yau koni ko ku duk wanda ya zagi uwata da yaruwata sai na yanke masa harshe byn na raba kanshi gida hudu ."

zaro idanuwa sukayi suna sake ja  baya dan ya daga takobin hannunsa daga aunty hassana har aunty salma suka koma bayan baba gali suka boye cikin  karfin halin yace " bamu bane dabbobi da uwarka kake aiko jin haka Ke da wuya habib yayi kansa gadan gadan  zai sara mata takobi  aunty ta rike masa hannu tana zabga masa mari cikin muryar kuka tace "meke damunka habib ta fad'a tana kwace takobin tayi jifa dashi  "zaka kasheni ne  ?

"Ai da zai kashe dabba irinki da mun samu kwanciyar hankali "inji cewar aunty salma .
aunty kina jinsu ko bani takobina na sassara
shegu yan kutumar uba .."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun allahumma ajirni fi musibatihi   Waklifli khairan minha tana gama fadar haka ta durkushe kasa tana cewa "yanzu habib irin tarbiyar dana baka kenan ?maryama ta durkusa kusa daita tana mai rike hannunta tana ma habib wani irin kallo mai cike da tashin hankali ".

"Me  yasa bazaka koyi danne fushinka ba ?me yasa zaka min haka habib ? me nayi maka dana cancanci haka habib ? "Kuji makira ina allonki allonki yana jahannama ,makira  mata kin gama koya masa yadda zai ci mutunci mutune shine  yanzu kizo kina kukan munafurci yau zamanku ya qare acikin gidan nan ku hada ina ku ina ku ku bar mana gidan nan mun gaji da ganinku daga Ke har wadan nan mataiyatan yayan naki bama bukatarku."inji cewar baba gali ."

nan da nan habib yayi kan baba gali duk da yaso ya rabu dashi ganin mahaifiyarsa tana kuka dan a duniya babu abinda ya tsana sama yaga ana cin mutunci mahaifiyarsa da yar uwarsa baya son ana zagar masa su bare a zagi qaddararta da binta da muyagun kalamai ko zubar hawayenta  ,wuyan baba gali yake shirin damka ya

jiyo sautin muryar aunty cikin kuka tana cewa "wallahi habib idan ka ta'ba shi sai na tsine maka albarka "cak ya tsaya yana kallon baba gali ido cikin ido jikinsa na wani irin rawa tamkar mazari ."

Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access  idan an tura sai a turawa wannan  09136918331  alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

             Page 16

Ahankali   maryama   ta  mike  daga  cinyar  umma   hawaye  ne  sha'be sha'be  akan   kuncinta
ta tsurawa umma  manyan    idanunta  wad'an da   suka   canza   kala  tana kallonta   batare  da   tace  uffan  ba  ,duk  yadda  taso  ta daure  ta  tsaida  hawayenta  kasawa   tayi  hawaye  take   zubarwa  sosai  cikin  tashin  hankali  mai  tsanani ita  kad'ai  tasan  halin  bakinciki  data  tsinci   kanta   ciki   adalilin   jin  labarin   iyayenta ."labarinsu  yayi  matukar  d'aga  mata  hankali "a  she  wahaalarsu  da  tsanar  da'aka yi  musu   acikin  family's  ta  samo  asali  ne  daga  soyayyar  iyayensu ?  haka nan  taji   tausayin  kansu  na   sake  shigarta   . "

     Koina   ajikinta   yayi  sanyi  yayinda   falon  ya  d'auki  shiru  ,yadda  maryama  tayi  shiru tana zubar da  ruwan hawaye  tana sake tariyo  halin  da  iyayenta  suka tsinci  kansu  adalilin  soyayya haka ma  umma  bata  sake  cewa  komai  ba  " ahankali  wani  irin  so  da  qaunar   mahaifiyarta da qaninta  habib   ya  qara  shigarta"  allah  sarki  aunty  "hakika  kinga   rayuwa,  hakika   ahlinki  sun  d'auki  zafi  dayawa  akanki  ."

"hukuncinsu  yayi tsanani  dayawa  domin  allah Ke had'a  soyayya  alokacin  daya so ba  dabarar  mutun  ba  ,ba  son ran mutun  bane  ,domin  kuwa  idan da  dabarar  mutun  ne  ko  son ran mutu da  mutanen  duniya  dayawa  basu  tsinci  kansu  cikn
ta ba ."

a qalla  sun  d'auki  minti  goma a haka  suna  kallon  juna   sannan  maryama ta  lumshe  idanunta da sukai   jajur  alamun  tarin  quna da bakinciki ahankali  umma  ta  numfasa  "maryama !  ta  kira sunanta  a  natse , ahankali  ta motsa  lip's  dinta  alamun ta amsa dan  zafin  da  zuciyarta  keyi  ya danne  fitowar  muryarta "ki  godewa  allah  ba  kuka ya  kamata kiyi   ba  maryama."

    "ki  godewa  allah  daya  qaddara  aure  a tsakanin  iyayenki  da  har  aka sameku  ta  hanyar  sunanh "  "Alhmd!ta  furta  a can kasan   makoshinta   tana  dafe  kanta  dake  sara da mugun karfi "ya  kai  ki godewa  allah  ki  sake  gode  masa  ko  bai  kai ba ? kanta  ta  gyada  mata  alamun "eh!.

"To  ki  manta  da  duk  abinda na  fad'a  miki  muje  Kiyi  sallah  kici  abinci  ki kwanta ki huta "  da  karfi  maryama  ta  fizgo  magana  "bazan  iya manta komai  ba ,a halin  yanzu  ma   ganin  komai   nake kamar   a yanzu  ya  faru  har  nayi  danasani  umma nayi  danasani   jin  wannan  mummunar   labarin  rayuwa  irin  rayuwar   da  iyayena  sukayi  rayuwar kaskanci  ne a wajena."

    "why  umma? "me  yasa  komai yake  faruwa  damu haka ?ahankali  ummah  ta  shafa  kanta
zuwa gadon bayanta  tare da cewa "kiyi  hakuri  maryama kowa da  kalar  irin  tasa  qaddara a yanzu  jajurcewa  zaki qara  akan  wanda  kikayi  har kika samu  cikar  burinki  na  zamowa  cikakkiyar  mai  ilimin  lissafi  ,kiyi  qoqari  ki tsaya  bisa  kafafunki  domin  tallafawa  rayuwar   mahaifiyarki   daya  qaninka   domin  ina  hango  tarin nasara  da  kwanciyar  hankali  atattare  dake , bilkisu  na  bukatar  farinciki  ,maryama  nasan  da sannu  zaki  zamewa  bilkisu  sanyin  idaniya  amman  fa  sai kin manta  komai  maryama  kin rungumi  qaddarar  rayuwarku ."

"Na  yarda  da  qaddara  ummah  domin  yana  daga  cikin cikar  imani  mutun , na yarda da qaddara  amman  umma  aunty  tayi  kuskure  arayuwarta  bance  laifi   bane  dan  taso mahaifina  amatsayin  da  yake amamn  iyaye  fa  umma ? "manzon   sallahu  alaihi  wa salam  yace "ridal  lahi  fi ridal walidaini , wa sakad'ul  lahi fi sakad'il  walidai ."yarda  allah  yana  tare  da  yarda  iyaye, haka zalika fushin  allah yana  tare  da  fushin  iyaye  allah  ya  fifita  iyaye  akan  komai most  especially  uwa ummah ,babu  uwar da  taza ji  dadin irin rayuwar da  aunty  tayi ."

umma  tayi  shiru  kawai  tana sauraronta "misali  na kwatantawa  aunty  irin  abinda  tayiwa iyayenta ya  zataji ? na  kawo  mata  in responsible  man  nace  naji  nagani  sai  shi  duk  tarbiyar da tayi  tsawon  shekaru  tana  bani nasa  kafa na  rugujeta ya zataji ?" magana  ta   gaskiya   iyeyenta  da yan' uwanta   sun d'auki  zafi  dayawa  amman  aunty  ta fisu  laifi  kuma  lallai  ya  kamata  taje  ga  iyayenta  ta  roki  gafararsu sannan  ta  koma  cikin  danginta zuciyarta ta  samu  salama ."

   "wallahi  yadda  nake  jin  habib araina  bazan  iya  barinsa  saboda  wani  ba  bare  iyayena  da suka kawoni duniya ba ,abun  da ciwo  ummah  ba  kamar  yadda  kuka  d'auka  bane  kema  uwa ce ummah , aunty  ta  kona  zuciyar mahaifiyarta   dayawa,  yanzu na gano duk  aunty  ce  silar  shigarmu   cikin   matsala , iyayenta  na  can  suna  fushi daita  har  yau  ta  yaya   kike tunanin zataji  dadi ?"ta  yaya  kike  tunani  zan  iya  bata  farinciki  byn  ga  inda  zata samu  fiyye  da  nawa  ."?

maryama  ta  kalli  umma  cikin  sarewa  ta cigaba  da  magana " umma  abun na  da matukar  ciwo  irin  ciwon  dake  cin  zuciya da  bargo  ,ciwo  ne da  bashi da  magani  da   mafuta  har  sai  ka  had'u  da  mahad'inka , shiyasa a kullum  idan  na  kalli  aunty  sai naji  tamkar  tana  boye  mana  wani  abu  mai  mahimanci  ga  rayuwarta , ashe  gsky  né  hakika bakinta  bazai  iya  furta  mana komai  akan  rayuwarta  ba  matsawar  ita  din  uwa  ta  gari 
ce , dan   allah  umma  Kiyi   min  rai ki  raba  zuciyarta  da  wannnan rayuwar  idan  kuma  baki  yi  ba ni  zanyi  ,zan  rabata da  nauyin  dake   daskare  a  qirjinta ."
Chapter 47 · 0% Book details