← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 8 OF 100

Sashe 8

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 7 min read

Ahankali mr ATA yake daga kafafunsa batare da ya sake yin wata magana ba dan idan yace zai cigaba da magana sai dai d'ura masu zagi , yana tafiya yana sake jin bacin rai duk wanda ya gansa yasan yana cikin damuwa ,dan haka masu kula da lafiyarsa duk suka shiga hankalinsu kowa na taka tsantsa ,da sauri escort dinsa suka biyosa cikin kamewa da taka tsantsan  kiyaye aikinsu , dan duk lokacin da ransa yake a bace yafi dakatar da mutun daga aiki ."
muhd bello ya biyosa suka jero tare zuwa Inda akayi parking din motocinsa escort suna kokarin bude musu murfin mota yayinda hisham ya juya ya nufi gidansu ."mr ATA na qoqrin shiga mota Kira ya shigo wayarsa ya tsaya cak hade da tura hannunsa cikin aljihunsa ya ciro wayar yana dubawa sunan aunty shahida ya gani yana yawo akan screen din wayar ya furzar da iska me zafi sannan ya danna koren maddanin ya manna wayar a kunnensa yayi shiru yana sauraronta "

can bangaren aunty shahida ta fara magana saboda tasan ba magana zai yi ba "kana Ina yanzu ? shiru ya cigaba da yi yana ciza lips dinsa na kasa sai data sake maimatawa sannan ya bude bakinsa da kyar "Ina shirin barin gida yanzu "to karka kuskura ka bar gida batare da kabawa mami hakuri ba "naji zan dawo anjima da daddare dan tayi fushi sosai yanzu yayi maganar yana runtse idanunshi zuciyarsa na suya "no kaje yanzu saboda nasan ranta yayi mugun 'baci shiyasa kaji nace haka Kuma bana son tayi fushi da kai adam kasan mami na matukar hakuri damu most especially kai tana hakuri da kawaici akan komai, wannan ma ka kaita makura ne "to ni yaya kuke son nayi da rayuwata ne ?

"hakuri sannan kabi umarninta ta fada atakaice "shikenan haka ni rayuwata zata qare cikin kunci Kunki ku tsaya ku fahimceni ? "Wani fahimtarka Kuma zamu tsaya yi tunda an baka lokaci Kaki kayi komai akai ?"fatanmu kayiwa mahaifiyarmu biyayya ka rike mana amanar maryam karka cutar daita sannan na tabbatar maka zakaji dadin maryam dan .."Kinga shahida karki dameni da wani amana ko zan ji dadinta kar in cutar daita "yayi saurin katseta ta hanyar fadar haka " kanku kawai kuke dubawa baka duba halin da zan shiga akan auren nan haka kawai zaku cutar dani akan wani auren baza "shahida kai tsaye ko adam ? "ta tambayesa numfashi ya sauke bai ce komai ba " kiran sunana yau babu ladabi ba komai ba ?"share wannan maganar raina ne ya baci zan zo office din na sameki idan na gama da sweetheart mu tautauna wasu abubuwa daya shafeni ,"

"karka sake Adam kazo min da wani tsari ko rashin kunya dan ba zan tsaya naji raayinka ba sannan kasani bazan dauki raini ba ,dan iskanci tun yaushe ake fama da kai ? shekara biyar kenan ana fama da kai ka fito da mata Kaki kullum ka zaunar da mutane kana masu karyar baka samu tru love ba ,haka kawai kanata batawa kanka lokaci abanza,tukun nama kana wannna iskanci na ji da kai da fadin rai yaushe zaka samu tru love ."?" kai wace shegiyar ce ma zata dauki wannan wulakanci da ji da Kan da kake fama dashi ? ai daman karshenka kenan ayi maka auren dole kaje can ka karata kowa ya huta dan .."bai tsaya Jin abinda zata sake cewa ba ya sauke naunayen ajiyar zuciyar yay disconnecting din Kiran Yana adduar samu sausauci daga gurin mahaifiyarsa ."

ya maida wayar aljihunsa ya koma cikin gidansu a Inda ya bar sweetheart dinsa anan ya isketa zaune gefenta maryam ce ke matsa mata kafafu suna hira cike da tsantsar biyyaya kyakkyawar datjijuwa me tsananin kyau da nagarta da sanin ya kamata da son zaman lafiya da lumana ta d'ago a natse idanunta sanye da farin glass wanda da gani na Kara lafiyar idanu ne ta zuba masa Ido tana mai tsananin qaunar d'anta ."kamshin dadd'adan turarensa (Reed ) mai sanyi da sanyaya zuciya tare da Kashi jiki da sace zuciyar duk wanda sautsayi yasa ya shaka yasa maryam ta fahimci ya sake dawowa falon ,a hankali ta bar abinda take ta dago idanunta dan tabbatarwa kanta shi din ne ko kuwa , ai ganinsa tsaye kikam kamar wani jami'in tsaro ba dan kasuwa ba yasa nan take qirjinta ya shiga dokawar daya Saba a duk sanda zata d'aura idanunta akanshi sannan ta dinga kokuwa da numfashinta kenan har sanda zai bar gurin ."

Ahankali idanunsu ya tsarke cikin juna wani irin kallon banza me hade da harara ya sakar mata babu shiri ta zare hannunta daga kafafun Mami ta mike tayi dakinsu ,Koda ta shiga dakin ma kasa samun natsuwar zuciya tayi ta rasa dalilin da yasa take tsatsanin Jin tsoronsa haka da Jin faduwar gaba akansa sannan ta rasa dalilin dayasa ya tsaneta haka koda bai fada mata ba tasan baya qaunarta dan tana ganin tsanarta acikin kwayar idanunshi ."
bayi ta bud'e ta shiga qirjinta na dokawa ta kulle kanta dan ganinta shine Inda yafi mata saukin zama ta rarrashi zuciyarta shiru tana tunanin ta nesanta kanta dashi zai samammata kwancinyar hankali, sai dai ina hakan ma ba mai yuwa bane domin mami bazata yarda ba wani sabon tashin hankali ya caki zuciyarta nan take faduwar da gabanta ke yi ya qaru ya wuce misali hattar cikinta sai kadawa take tayi Imani a lokacin da tana da ciki tsab zai fice ya barta ."

cike da ladabi da biyayya ya dan saki rashin kadan ya k'araso ya durkusa a gaban mahaifiyarsa kmr zai mata sujjada "Sweetheart! ya kira sunanta bata amsa ba ta cigaba da kallonsa "kiyiwa Allah kiyi hakuri ki bar maganar nan a tsakankanimu karki bayyanata bare kowa ya sani ita kanta yarinyar idan ta sani sannan taji rashin amincewata zataji babu dadi a ranta ," shiru hjy zulaiheart tayi taki cewa uffun har sanda ya dasa Aya " Allah ya huci zuciayrki hjy sweetheart dan nasan zuciyarki na tattare da fushina amman kiyi hakuri ki yafe min abinda nayi " yana gama fadar haka yaja bakinsa ya sake yin shiru yana sauke numfashi ,hjy zulaiheart ta kafeshi da idanunta sosai ta cigaba da kallonsa taso ya fadi fiyye da abinda ya fad'a idan ma da hali yace "ya amince da umarninta amman sai sa'banin haka yake furtawa ,ya tsaya a iya hakuri kawai da kin amincewa ."ta rasa wace irin zuciya ga Adam sam idan ya kafe akan abu ya kafe kenan is very hard ya canza ra'ayinsa wannan halin kawai tafi tsana a rayuwarsa tun yana yaro tayi iyakar kokarinta akan wannan hali abun ya cutura sai dai akan wannan lamarin ta rantse ko zai rasa ransa sai ta canzasa Kuma sai yayi abinda take bukata ..

ya d'auki tsawon minti goma yana durkushe yana bawa mahaifiyarsa hakuri wanda ita ba hakuri tafi bukata daga tillon dan nata ba amincewarsa tafi bukata ,naunayen ajiyar zuciya ta sauke da karfi sannan tace "shikenan komai ya wuce na yafe maka amman ka San da sanin bazan taba janye maganata ba tunda na baka lokaci mai tsawo ka kawo min wacce kake so Kaki kullum da dramar da kake bullowa daita ayi mgn kace tru love kake jira ,dan haka bazan zuba maka Ido ba kayita zama babu iyali ba "Kai yanzu sbd Allah baka jin kunya ?duk sa'aninka sunyi aure har da yayansu abun sha'awa ? amman Kai baka wannan kasar baka wancan kasar , Neman kudi kawai kasa a gaba to meye amfanin kudin da Babu magada ? Kai da mahaifinka bai haifeka ba ka gaji tarin dukiyar daya bari ?yayi shiru yana riko tafukan hannuwanta cikin nashi dan bashi da amsar bata " ni dai gaskiya na gaji da zaman ka haka babu iyali Ina bukatar ganin ya'yanka idan Kuma kafi bukatar sai na mutu kayi auren shikenan sai na hakura na daina maka maganar amman fa kasani muddin nayi shiru yana nufi babu ni babu kai har abada ko mutuwa nayi zan bar wasiha kar abarka ka ta'ba ga....."

"Dan Allah Dan girman Allah kiyi hakuri Sweetheart ki daina ambato mutuwar Nan ki rufa min asiri idan kika mutu duniyar fa bazata min dadi ba , kece duniyata, ke kike sakani farinciki idan nayi cikakken awa daya banji muryarki ba Ina rasa gane kaina inaga baki duniyar ...?"kiyi hakuri inshallahu zaki ga aurena nida auta kmr yadda kika ga na saura yanuwanmu amman ki dan bani lokaci zan kawo miki wacce nake so nan kusa ,sai byn da yayi maganar ya fahimci maganarsa ta fito ne ba a yadda ya dace ta fito ba dan ta Ina zai fara ...?
"Wannan lokacin ya Kure Maka Adam har abada Babu wani sauran lokaci da zan sake baka kaje ka fara shirin aurenka da maryam kawai , tana gama fadar haka ta kawar da fuskarta gefe dan idan ba haka tayi ba zuciyarta zatayi sanyi akan tillon danta har ta fasa aiwatar da nufinta akanshi tsam ya Mike ya soma kokarin barin falon zuciyarsa na tafarfasa da tuttukin bakinciki dan yasan tunda ta kafe ta nace Babu wani sausauci baya ga amincewa kudirinta ."
Chapter 8 · 0% Book details