← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 34 OF 100

Sashe 34

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

"wannan Kuma  impossible aunty bazata iya ba  " suka ji sautin muryarsa acikin dodon kunnensu a tare suka juyo a firgice  suka  Kalli Inda yake tsaye sanye da farar jallabiyya mai gajeren hannu ajikinsa gashi kan nan nashi sai sheki yake zubawa  tamkar balarabe kallon second biyar mrym  tayi masa tayi saurin  d'auke kanta sakamakon mugun kallo da yake jifanta dashi  .matsowa kusa da aunty shahida yayi sosai  fuskarsa a hade babu alamun murmushi "babu abinda za'a ta iyayi wanda zai dakusa wannan soyayyar dake dawainiyya da zuciyata da gangar jikina   Ina son princess so mai girma sannan gara ki fad'a mata babu iskanci da sakarci a gidana  dan bazan dauka ba ."

Take kwakwaluwar  mrym  ya shiga ceculating abinda mgnrsa take nufi  kenan akwai  wacce yake so  aka takura masa aurenta ?take jikinta ya kama kyarma ya ware hannuwansa duka cikin jin dadi  "okay a she fa bata san da wannan zance ba fa ?"gsky ya kama ta san cewar  akwai wata acikin zuciyar Adamcy Kuma ko ba dade ko bajima muddin na ganta zata kasance cikin rayuwata bukatata na ganta domin nafi bukatarta fiyye da komai  ."

gbdy mrym dake zaune taji babu dadi acikin ranta "tabbas wannan shine dalilin dayasa bai maraba da aurenta  wani bakinci ya ziyarci qirjinta ta mike tsam zuciyarta cunkushe ta nufi kofar fita tana fita aunty shahida ta soma magana cikin fushi "wai me yasa kake yin hk ne sam bai dace ba?  "me Kuma nayi byn gskyr dake cikin Raina na fada gara tasani ?  ''idan kana yiwa mrym hakan bazamu ji dadi ba , rainmu  zai dinga  baci fiye da bacin ran daka gani yanzu acikin kwayar idanuna ,dan bazamu  yarda ka fifita wata banza can akanta ba banzar ma da ba gskiya bace  .

"duk son da nake   maka zan   iya ajjiyeshi gefe   na hukuntaka hukunci mai tsanani akan mryam ,kada  ka sake makamancin wannan maganar a gabanta  wannan ya zamo Karo na karshe  ya jiyo sautin mahaifiyarsa wacce ta shigo byn fitar mrym nunfashi ya fesar yana cewa ''relax  sweetheart  insha Allahu  an gama ya fice ya barsu   "Allah ka shirya Adamcy na rasa meke damunsa "  meke damunsa kuwa ban da iskanci aunty shahida ta katse hjy zulaiheart , nifa wani lokacin sai naji kmr Abar had'in nan kar yazo ya bata zumunci   ."babu wani zumunci da zai bata wannan auren Allah ya rigada ya hadashi tunda gashi har ya amince ayi ,da yarda Allah rayuwar gaba zatai dadi "Allah yasa inji cewar aunty shahida.
Da fari  baba qarami hjy zulaiheart taso ta kira ta sanarwa hukuncin data yanke kasancewar shi yana bangaren baya inda mallakinsa yake sai dai tayi tunanin ta fara sanarwa baba Babba kasancewarsa babba a tsakaninsu a yanzu   saji  daga bakinsa
tayi murmushin Jin dadi dan tasan baba qarami zai ji dadi sosai  idan labarin auren adamcy dan kusan kullum sai yayi mata maganar ."

*****
a natse ta fara  neman   layin qanwarta    hjy nuriyya   wacce ta kasance abokiyar wasanta iyayensu uwa d'aya Uba d'aya Kuma akwai shakuwa  sosai a tsakaninsu tana  zaune  a kasar  london  tun aurenta har zuwa wannan lokacin acan ta haifi yaranta duka iyakarta da naija ziyara ko wani sha'ani mai mahimmam. suka gaisa cike da farinciki  Inda hjy zulaiheart take sanar mata batun hada Adamcy aure da maryam  " Kai  alhamdulillah masha Allah gsky abu yayi kyau  sosai Allah ya sanya alkhairi ya  nuna mana lokaci ,wannan karon zanyi k'okari na shigo kasar  kafin lokacin  domin ayi biki dani ".

Hjy zulaiheart tace "gsky kam anyi  bukukuwa duk baki  samu  damar shigowa  naija ba "haka ne kam  amman inshallahu  zan shigo wannan bikin nayi ne no any excuse ta k'arasa maganar tana murmushi suna cikin hirar hjy zulaiheart  tace "nuriyya wai kuwa  kina jin  labarin bilkisu  ?dip hjy nuriyya  tai tmkr an d'auke wuta nepa tana jin  wani irin daci acikin ranta sai data yi kusan minti biyar sannan tace  "bana Jin labarinta Kuma bana son na  ji labarin Inda take ,  kuma  Ina son ku shareta ku cireta acikin zuciyarku har abada  Kmr yadda mukayi yarinyar data nuna mana bamu Isa daita  ba ,sannan  bata  sonmu  ta zabi rayuwa ko babu mu me yasa zamu damu daita ?

"ni dai duk wanda zai nemata acikinku yaje amman  ni nuriyya bana ciki kuma babu hannuna  babu kafa ta ciki  "naunayen ajiyar zuciya hjy  zulaiheart  ta sauke tana cewa " dan Allah nuriyya kiyi hakuri ko babu komai rayuwarta qaddara ce Allah ne ya d'aura mata wannan rayuwar babu yadda zata gujewa qaddararta ,wallahi  duk sanda ta fado min sai na zubar da hawayen tausayinta , da nasan Inda zanganta  wallahi zan nemota  .
"Kune fa kuka damu daita ko nace ke dan duk  cikinmu babu me zanceta wallahi sai ke ,bata ga wuya bane shiyasa bata dawo ba, wallahi nafi son rayuwa ta juya mata baya ta dawo tana kuka  tana  rokonmu  kullum mummunar adduar da nake mata kenan sannan Ina adduar duk tsanani karta dawo mana da zuria Kmr yadda hhyrmu take addua ."

"wannan addua ta rashin haihuwa a tsakaninsu batayi ba ku daina mata mummunar addua gskiya "ai babu abinda ya kamaceta da wuce mummanar addua " yanzu dai kiyi hakuri  muyita mata addua da fatan alkhairi a duk Inda take lokaci nata tafiya a lisafinsa shekaru ashirin kenan rabonmu  daita , kiyi hakuri dan mu barwa Allah komai sannan muyi mata adduar Allah yasa ta waiwayo mu cikin koshin lafiya naunayen  ajiyar  zuciya hjy nuriyya tayi  sannan tace  "shikenan big sister ai abinda  kikace shi zamuyi  cike da qauna yar'uwarta hjy zulaiheart sukayi  sallama da yaruwanta suna gama wayar uncle Umar ta kira ta sheida masa tana son ganinsa  ."

Ranar asabar   da misalin karfe hud'u na yammaci  baba bAbba   yazo   bisa Kiran da hjy zulaiheart tayi masa , byn sun  gaisa   hjy  zulaiheart ta karanto  masa hukumcinta   akan ATA cike  da farinciki uncle Umar yace "masha Allah wannan hukuncin yayi  Kuma mun gamsu dari bisa dari dan burin mu bai wuce muga adam ya ajiye iyali ba  ,bugu da Qari zaa sake  karfafa zumunci a tsakanin   inshallahu  zan sheidawa sauran yan'uwana sai mu saka ranar da zamu ga alhj saidu  dan  zamu so a daura auren nan  kusa". "wannan  maganar tayi Kuma naji  dadinta  sosai dan  haka a fara sheidawa  baba qarami dan  nasan murnarsa sai tafi  ta kowa domin duk yafi  mu d'auki son ganin  Adamcy  yayi aure ta k'arasa maganar tana murmushin jin dadi  "ai kuwa daga nan ma bangarensa zan shiga na fara sheida masa  Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokaci "Ameen ya Allah,Allah  kadai yasan murnar da zaiyi  idan yaji  ya sha lemu da kayan snaks din da'aka jera masa suka zarce da  tautaunawa  kafin daga bisani sukayi  sallama ."

Baba qarami   na zaune akan  kujera me zaman mutun uku  sai ga baba Babba   wanda ya kasance yaya  garesa Kuma Kani ga   mahaifin ATA yana ganinsa ya saki fuska tare da farincikin ganinsa  ya d'an  mike tsaye cike da girmamawa ya bashi hannu  suka gaisa sannan ya nuna masa mazauni atare suka zauna "sannu da zuwa yaya ! "ya gida da iyalin  fatan  suna lfy?"alhamdulillah kowa Lafiya yake ya naka iyalin  ?"Suna lfy ya bashi amsa yana murmshi ya mike ya  dauko masa abun sha "bazan sha komai ba daga bangaren hjy zulaiheart nake na sha "  .
suka yi shiru na second biyu sannan baba babba ya fara magana a tsanake " kamar yadda na fad'a mk  daga bangaren hjy zulaiheart nake tayi decide ta had'a Adam aure da diyar kaninta abdulrauf " what ?"when ?ya fada a matukar rude yana Jin wani  irin abu ya  caki kahon zuciyarsa , yayi saurin runtse idanuwanshi "zulaiheart na bukatar wannan labarin ya zamo Kaine ka fara jinsa   bisa kokarinka na son ganin adam ya ajiye iyali dan haka nan da sati me zuwa zamu gana da yayan mahaifin yarinya alhj  saidu  ."

shiru  baba qarami yayi har sanda yayansa ya dasa aya  ya mike tsaye"to ni zan wuce duk abinda ake ciki zan kiraka a waya a fusace baba qarami   ya mike Shima  yana cewa "yaya wannan wace irin maganar banza ce kazo min dashi  sannan kana k'okarin sa kai ka wuce ka barni  ? yayi mgnr  a fusace yana sa hannu ya daki center table din dake tsakiyar falonsa wanda ke d'auki da ruwan lemu kala dabam  dabam ,nan take wasu glas cup  suka  tarwatse yana huci yake kallonsu "yanzu ni dana cin burin ya zabi daya daga cikin ya'yana ya aura shine dan munafurci zata hadashi da diyar kaninta saboda son Kai irin nata ?

"ya'yana  yafi  dacewa Adam  ya aura ba wannan yarinyar ba ya sake dukan table wanda hakan yasa gbdy ahlin da ke numfashi a part din suka bayyana" burina bai wuce ya'yana ko jikokina su had'a  iri da dashi ba yayi mgnr yana kallon cikin kwayar Idanu dan uwansa  ."me yasa zaka fadi haka idris?  "eh na fad'a yayi mgnr yana cakunar wuyan dan'uwansa da iyakacin karfinsa  yana maxurai  abinda bai taba faruwa ba a tsakankanisu ,hindatu wacce suke kira da hindu     ta samu guri ta zauna tana kallonsu zuciyarta na rawa dan ta dade a tafkin qaunar ATA mahaifinta ne ya hana a fito da soyayyar a cewarsa yana jiran lokaci yau ga lokaci ya zo masu a wani iri .
sauran kuwa hankalinsu ne yayi kololuwar tashi ganin yadda mahaifinsu ke rike da wuyan dan'uwansa uwa d'aya Uba d'aya .Wallahi yaya Kai kare ne  da bai san ciwon kanshi ba ! "shin ya'yana basu dace dashi bane ka  bani answer ?uncle Umar yayi shiru kawai yana kallon hannun uncle idris dake rike da wuyansa batare daya ce uffan ba.

"me yasa kazo min da  wannan banzar labarin mara dadin ji ?ya k'arasa maganar yana sakar masa wuya yana dubansa yana huci "saboda mu bamu Isa ta hada jini damu ba shiyasa ta za'ba masa acikin dangi ta ?"to me zai faru idan na hana auren ?"zan hana wannan auren ta karfin tsiya yayi mgnr yana d'aga hannunsa sama  sannan  ya dungule ya  naushi bangon  falon sai da gurin ya tsage  ya tsaya yana huci da kallon wani bangare ."
Chapter 34 · 0% Book details