← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 44 OF 100

Sashe 44

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

Maryama  tayi  shiru  kawai  tana bin    shukura  da  kallo "me  kuma  hakan  yake  nufi  dani ? me na yiwa  sakina  ni  kuwa  daga  jiya zuwa  yau  take  fushi  daita  hk ."tayi wa  kanta  tambayar  da  bata  da mai  bata  amsa  sai  sakina  ita  zagin  shukura  bai  dameta  ba kamar  sauyawar  sakina  ta gyada kanta  ta  cigaba  da  shara  tana tunanin  laifin  da taiwa  sakina  har ta  qarasa  ta  wanke  hannunta  da kafafunta  ta d'auki  quraninta ta shiga  d'aki  inda  sakina  take  zaune  akan  gado  tana  cika  tana batsewa  tana  ganin  maryama ta  sake  had'e rai Kmr  taga  mugun  abu  maryama bata damu ba ta zauna  kusa  daita  ta  soma  janta  da mgn taso  tmbyrta  laifin  da  tayi  mata  amman  ganin  yadda  take barsarwa  yasa  tayi  shiru  daga  karshe ta wuce  zuciyarta  cike  da  matsanancin damuwa ."

*******

Da  misalin   karfe  d'aya   na  ranar  laraba  wanda  yayi  daidai  da sauran  kwana uku  jirgin  mr ata  ya tashi   zuwa   france   amman  har  lokacin  jikinsa   sai  a hankali  daga  matsanancin  ciwon  kai  ya dawo  masa  ciwon  gabobin  jiki  dan  ko  miyo  baya iya  had'eyewa  sosai  mami  ta  sauko  daga  saman   d'akin    mr  ata  tare da  likitansa  byn  mami  ta sallame  doctor  rafeeq  ta  dubi  maryam  da  nana  hauwa'u tace   "yayanku  fa  yau   tsawon  kwana   biyu bashi  da  lafiya  ku  shiga  ku  gaishesa  keda maryama  ,jiki  sanyaye  suka  ce" to!  suka  mike atare  suka   hau sama ."

A natse   sukai  knocking  wanda  nana   hauwa'u  ce  tayi   mryam  na  bayanta  ara'be  kusan  second  goma   suka  d'auka  tsaye sannan  ya  basu   damar  shigowa  d,akin  ,da  sallama  suka  shiga  parlour  suka   gansa  kwance   akan  doguwar  kujerar kushin ya   runtse  idanuwanshi  yana   sanye  da  riga  fari  sol  da  gajeren   wondo  iya  gwiwarsa  yayinda   hannunsa  d'aya  Ke  daidai  saitin  zuciyarsa  ya  d'an  bud'e  idanuwanshi  kad'an  ganinsu  yasa  ya    maida  idanuwanshi  ya  runtse  gam."

nana  hauwa'u  tace "sannu  yayanmu  ya jikin  naka kayi  hakuri  walllahi  bamu  san  baka  da  lafiya ba sai  yanzu  da  mami ta sauko  take  fad'a  mana  " shiru  yayi   bai  amsa  mata ba  nan  da nan  maryam ta  shiga  hankalinta  dan tasan  ita  kam  sai ya  had'a   mata  da  tsaki  muddin  tayi  masa  sannu   suna  zaune  shiru  nana  hauwa'u  ta d'an ta'ba maryam  tana  mai  mata  alamar  ta  gaishesa wani abu mai  d'aci  daya  tsaya  mata a  wuya ta had'iye  ta  bud'e  baki  muryarta na  rawa "yaya  sannu "ta fad'a  atakaice  ilai  kuwa  tunaninta ya tabbata  dan kuwa  bai  amsa  ba  sai  ma  tsakin  daya  ja yana  cewa "auta  ya  bani   abun  na  sha a fridge da  saurinta  ta mike ta isa  inda  qaramin  fridge  dinsa   yake  ta  bud'e  donsimo ta  d'auko  masa ta had'a masa  da  ruwa  ta ajiye  masa  akan  table din  dake  gabansa  ."

"gashi  yaya Allah ya  baka  lafiya  ya  d'an  motsa lip's  dinsa  alamun ya amsa ya mike  zaune  da  kyar  batare  daya  kalli  inda  mrym  take  ba  itama bata sake  kallon  inda  yake  ba sai ma fuskarta  dake  kallon  wani   katon hotonsa  dake manne  da bangon falon   sanye  cikin  kananan  kaya  riga  da  wondo  milk  colour  touch  of  black  ya  zura  hannuwansa  duka  cikin  aljihun  wondonsa idanuwanshi manne da  farin  glass  fuskar  nan  tashi  a had'e  Kmr koda  yaushe  "auta  !
Ya  kira  sunan  nana  hauwa'u  ta amsa da "na'am yaya! "shiga  bedroom  ki d'auko  min wayoyina da sauri  ta shiga wayoyin na kan katifarsa ta  d'auko tana  danna  gefen  wayar  inda  nan take wayar ta kawo  haske  screen ta  duba  fusakar  wayar wata kyakkyawar  fuska ta  gani  kanta  babu  d'ankwali gashin  kanta  ya  zubo kad'an ya rufe mata gefen  idanunta ."

ta tsurawa hoton ido sosai nan ta gane zane ne ba asalin  hoto ba ahankali take tafiya tana  kallon  fuskar  wayar  duk  da  zane  ne  ,amman  yarinyar  tayi  matukar  yi  mata  kyau ta kai  masa  tana cewa "yaya  zanen dake  kan screen din wayarka yayi min kyau  sosai wacece ?"tayi  masa tmbyr  tana duban mrym  da  hankalinta baya kansu yana can kallon mr ata , tana kallon kyaun da allah yayi masa ba abinda yafi  burgeta dashi kamar sheidar sallarsa daya fito masa a saman goshinsa yayi baki tmkr tawadar Allah ."

ahankali zuciyar mr ata  ta soma bugawa da karfin gaske  yana jin tmkr ta kunno masa emotion's din da yake ta qoqarin dannewa acikin zuciyarsa nan da nan idanunshi suka canza kala cikin tunanin da maryam take taji yana  cewa "yarinyar mafarkina ce dana  zanata da hannuna, itace  cikar  burina  ce farincikina ina matukar sonta itace mace ta farko da zuciyata take so  .." jin haka yasa gaban maryam  yayi wani mummunar  faduwa sakamakon jin abinda  ya fad'a ta juyo ahankali ta tsura masa idanunta duk da ba karon farko  kenan ya ta'ba fadar haka agabanta ba amman na yau din yasa taji wani iri a gbdy  ilahirin  jikinta  ta lura baya iya boye fellings dinsa  akan  zanen  ."

ina ma zata ga fuskar yarinyar taga dame tafita da har zuciyarsa ta zabeta alhalin ita din ba gsky bace ?tuna zane ce   yasa ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya mai  had'e da  zallar  kishi "ina  matukar  sonta  auta amamn na rasata a yanzu haka ina son raba rayuwata da tunaninta da duk abinda ya shafeta yana  magana yana  kallon  screen din  wayarsa wanda  Ke  dauke   fuskarta "mun dace da juna ko ?ya tambayi  nana  hauwa'u  yana  lumshe tsumammun  idanuwanshi   dake  cike  da  azaban ciwo ."

Nana  hauwa'u  bata  bashi  amsa  tmyr  da   yayi mata  ba  ta kalli  maryam  dake  tsaye  tana  dubansu   idanuwanta  cike  da  kishi  ajiyar  zuciya ta  sauke  tace "yaya  zamu ce allah ya  baka lafiya "na  tambayeki  baki  bani  amsa  ba ya fad'a a mutukar fusace  yana  watsa  mata  harara "me kace ?" shiru  kawai  yayi  tare  da  tsura  mata idanuwanshi   itama  kallonsa  take  tasan   abinda  ya  tsana  kenan  dan  hk  muryarta na rawa tace "kun..." kun  dace  sosai  kawai  dai  matsalar ita din ba   genuine  bace  wani  dogon  tsaki  yaja  yana  cewa "nonsense !"you  and   this  stupid  girl  should  leave  this  room  right  now "ya fad'a  yana furzar da iska mai   zafi  daga  bakinsa  da sauri ta kamo hannun maryama suka  fice  daga  d'akin ."

Bayan  fitarsu  kwanciya  yayi  yana cigaba da kallon hoton screen  din  wayarsa  dayawa daga cikin hotunta ya  konasu  hatta  tsarka  zanenta dake wuyansa always  yayi  flushing  dinsa  ,kadan ne daga cikin zanenta  suke cikin  d'akinsa   sai  na kan screen  din  wayarsa  suma nan kusa yana sa rai zai rabu  dasu  ya  huta  da  tunaninta  sosai  yake kallonta "muguwa "ya  furta a wahalacce   "kin addabi  rayuwata  kin  hanani  zaman  lafiya  ke  wace  irin  muguwa ce  da  zaki  damun  rayuwata ?ya  tambayi  kanshi  yana  mai  kawar da kansa daga kallonta  yana   tunani "anya  bazan  dinga  zagawa cikin  anguwane  anguwani  ba ko allah zai sa na ganta "? wannan ai hauka ne mr ata  kake  shirin yi ,me  yasa  bazaka  yarda  cewar  yarinyar nan ba  gsky  bace  Kmr  yadda  aka  Ke  fad'a  maka ?
shiru yayi  yana  jin  wani  irin  buguwa  da  zuciyarsa ke  yi  akanta  sosai  yake son raba kanshi da tunaninta  ."

Bangaren  maryam  kuwa   suna  taka  step  tana  maseefa "nifa  shiyasa  bana  son  zuwa  inda yake bashi  da  aiki  sai  maseefa  da  disga  mutun sannan wulakancinsa  baya  qarewa akan kowa sai akaina ko ban shiga  tsabgarsa ba sai ya hada dani ni wallahi bana  son  auren  zan dai  yi  ne kawai dan kun dameni , dan  allah  ku raba ni da aurensa na huta tunda ba'ayin  aure  mutun daya  ." murmushi nana hauwa'u tayi  "na lura kishi kike da zane fa  "babu wani  kishi  sister  amman ka auri mutun zuciyarsa na mafarkin wata aljana can wannan ai sai su shafi  mutun  azo arasa meke damuna "hhhhhhh nana hauwa tayi dariya "yarinya kina da aiki kam dan fasa wannan auren sai dai idan daya daga cikinku ne ya mutu  maryam  taja  tsaki ta  d'auki  hanyar  da  zata kai  ta  d'aki  ta  shige  tayi kwanciyarta dan kar mami  tayi amfani da zamanta  a parlour tayita aikenta  d'akinsa  shi  kuma ya samun damar ci mata  mutunci ."

Mr ata  na kwance akai  knocking kofar falon yana daga kwance ya bawa mai yi knocking din izinin shigowa hisam ne ya shigo cike da kulawa ya qaraso ya zauan yana cewa "a she bakaji dadi ba ? ya amsa da  kai kawai "oh my god  amman dai ba matsalar nan  bace ? "no ! wannan muguwar yarinyar ce "
maganar ta daki kunnuwan hisham ya dan tsaya yana kallonsa  yana nazarin maganarsa "yes  muguwa ce  taki  barin na ganta a zahiri  taki barin zuciyata  ta  zauna  yanzu  ko mafarkinta nayi bata min  magana , bata min murmushi this love is so hurt  wallahi  muguwa ce amman har yanzu ina jin sonta hisham na qasa  cireta  araina  ."

ya sake kallonsa ya girgiza kai cike da tausaya masa ya mike da kyar ya shiga bayin dake ciki ya zubar da yawu ya dawo ya zauna ya sake kallon hisham yaga shi yake kallo fuskarsa da mamaki ya sake  girgiza kai dan gbdy ya fahimci wa yake nufi "gsky wannan yarinyar tana baka wahala " ya langwabar da kanshi gbdy  ya koma kalar tausayi "wallahi yau shekara nawa ina faman da soyayyarta amman sam sam yarinyar nan bata tausayina yayi mgnr duk jikinsa ya sake kana kallonsa kasan bashi da lafiya ."

"da  ba dan baka da lafiya  ba  ai da mun dan dinga zagawaya  cikin unguwani ko zamu ganta ko wanda yasanya  nima  nayi  wannan  tunanina  hisham   amman  bazan  iya  ba  ya  fad'a  yana  lumshe  ido yana  jin  wani  d'aci  a bakinsa wanda ya rasa na meye ,"karka ce haka ata  ka bari  idan  ka samu sauki  kaje  france  ka  dawo  lafiya  sai  mu  fara nemanta " nace bazan  iya  ba  wannan  muguwar yarinyar  kona  ganta  damuwa  zata zame min
a  zuciyata ."
Chapter 44 · 0% Book details