← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 60 OF 100

Sashe 60

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

ahankali taji sautin muryarta tana fita  cikin kuka "nayi  kewarka baba , nayi kewarki mamana yanzu ku har yanzu  bakuyi kewata ba ?yanzu ku baku yafe min ba ko nemeni ba? wallahi ina sonku nayi kewarku ,nayi  kewar  kowa da kowa  ta fad'a tana mai daura hoto a saman  qirjinta tana shafawa tana kuka.."

Ahankali maryama ta juya tana zubar da hawaye masu zafi ta koma falo ta zauna kusa da habib tana sheshekan kuka nan take ya birkice ya soma tambayarta "heartbeat me kuma ya fara ?kukan me kike yi ? Ina aunty ?yayi mata tmbyr ajere cikin tsananin tashin hankali tasa gefen rigarta ta goge hawayen "yau aunty ta tuna da iyayenta tana daki tana kallon hotonsu tana kuka ni nasan zuciyarta na cike da qaunarsu shiyasa kaga ina son ta koma garesu ."

"habib  soyayyar  iyaye  da  yanuwa  baa  wasa  dasu wallahi a tsakaninsu soyayya ce mai karfi ka misalta hakan akanmu musan da qaddara  amman an cuci aunty an yi sanadiyyar rabata da kowa nata ,ta bar iyayenta akan soyayya gashi ta rasa soyayya taki bin umarnin iyayenta gashi duniyar taki mata dadi maryama tana kuka habib na rarrashinta har kukan nata ya ragu adaidai lokacin da sukaji tahowar aunty tayi saurin share hawayenta tana cewa ".

karka nuna mata komai da sanyi jiki ta qaraso "kun samo abinda zaku dan ci ?eh mun samu har da cinci tô maza kuci ku kwanta tayi maganr cike da rauni aunty kizo muci tare "aa ku dai kuci ku koshi aa wallahi tare zamu ci habib ya mike ya kamo hannunta ya zaunar daita ya bude kula abinci yana cewa kai abincin nan zai yi dadi maryama ta dauko spoon ta dibi abinci zata kai bakin aunty habib yayi sauri ya kwace spoon "bani ni zan bata da kaina suka sa da dariya ya soma bata abinci abaki yana fada mata kalamai masu sanyi ."

"idan nayi kudi bazan yi nesa dake ba zan kasance tare dake ,dan allah aunty ki daina damuwa akan komai kinji ki dinga tunawa cewa kina damu mu din zamu zame miki farinciki a rayuwarki Wallahi sai mun sa kinyi alfahari damu ki cigaba da addau ga heartbeat nan kwanan nan zata fara bautar qasa yanzu ma ina mata  processing yadda zaa dawo daita lagos né daga adamawa wannan farinciki  ya rage tarin qunar da zuciyar aunty take ciki  tace "allah yayi maku albarka yayiwa rayuwarku albarka in sha allahu bazaku dangwama haka ba allah zai saukaka maku rayuwa ,Allah nake roko ya daukaka min ku na yafe  maku duk abinda kuka min da wanda nasani da wanda ban sani ba suna cin abinci suna debewa juna kewa ."

******

da misalin karfe 9:00 na washegarin ranar lahadi mr ata ya fito  parlour'n  mami  ,duk  jikinsa yayi sanyi har wata  katuwar  rama  yayi  daman ya lafiyar kura ?ba wani jikin kirki bane dashi  kusantowar aurensa da maryam yasashi jin    kmr  ana  fixgar  ransa  ,shiru ne  ya  ziyarci  parlour'n yana tunane  tunane yana jin kamar idan ya tafi france  kar  ya  dawo  domin a lissafinsa sauran kwanaki goma cif a daura masa aure da yarinyar daya tsana fiyye da komai arayuwarsa   byn  kmr  mintina goma mami  ta qaraso  da kanta ta  had'o masa abun kari , chips  da soyayyen kwai  da  ruwan tea mai kauri , ta janyo qaramin table  gabansa ta  ajiye kana ta zauna kusa dashi ta tsura masa ido tana kallonsa batare datace komai ba ."

ya dauki cup din tea ya kai bakinsa ya kurbi kadan yana mai runtse  idanunshi  shiru har wasu mintuna suka shude yana zaune itama tana zaune tana kallonsa da kyar ya bude baki "sweetheart! "kaci abinci first before anything adamcy , sannan kar naji  kayi  magana  kaci abinci  kawai yaushe rabon ka sanyawa cikinka  abinci  bare a samu magani yayi aiki ajikinka ? ji yadda ka dawo acikin kwanaki uku kacal  ka taimakeni kaci wani abu  kanshi  kawai ya iya d'aga mata batare da ya kalli inda abinci yake ba, saboda sam  baya jin cikinsa  zai iya amsar komai  shima da zata taimakesa da tasa an fasa auren nan da yarinyar an hadashi da wata zai hakura da princess dinsa ya amshi koma wacece  duk da zuciyarsa princess kawai take so da son gani numfashi ya dinga  saukewa ."sweetheart  dina me yasa  kika  manna min wannan auren  haka?
" sweetheart  zaki  kasheni da kanki wallahi at least ki sake gara min dama koda  na  tsawon wata guda ne  ."

"to me  zan  maka adamcy nah daya wuce haka ?
"me  kake  son  nayi  idan  banyi maka  haka ba ?
gani nayi  kana  neman hargitsa min kwakwaluwa da qarar da rayuwarka a banza "me kake tunani mutane zasu ce idan   bakayi aure adaidai wannan lokacin ba ? wallahi zaka shiga zargin mutane ,mutun har mutun kamamme kamar ka ka zauna babu aure ko kana neman mata ne adamcy bansani ba da kake gudun aure ."

wani  irin kallo yayi mata mai nuna mata bayayi "to idan bakayi me kake jira ?maryam  yaruwarka ce fa "yanzu kai kafi son ka dauko min suruka daga waje alhalin ga wacce tasan darajata take sona nake sonta diyar danuwana yanzu idan an fasa auren nan  me kake son na cewa mutane da yan'uwana ,dan Allah dan annabi in banda   da rigima irin naka ba me ye laifin maryam ..?

"wani far yayi da idanu zuciyarsa na dokawa  da numfashinsa da yayi kokarin d'aukewa yayi saurin dawowa dashi gangar jikinsa sannan yace "sweetheart  ni bance tana da laifi ba amman  ki duba lamarin da  kyau  tunda nace bana sonta ai  sai a  hakura kawai  kowa ya kawo zabinsa . "kai rufe min baki ban son shirme banza, ka daina ganin ka had'a komai kana da kudi  kayi tunani zaka iya  juya ni  ."Wannan  aure sai  anyi shi muddin ina raye ."

ya marairace muryarsa  sosai  tmkr  mai shirin zubar da hawaye sannan yace "wai sweetheart me yasa kike ganin kmr  wannan yarinyar ce kawai zata iya kulawa dake  ? Allah  sweetheart ki daina mata kallon haka  saboda irinsu sune masu bawa dangi kunya  wallahi duk lokacin da naji kince min itace zata san darajarki  bakinciki nake ji kmr na kashe kaina saboda ni duk macen dana kawo miki dolenta ta soki tayi miki biyayya bama Ke ba sweetheart hatta yayyuna biyu din nan dolenta ta bisu  lalacewar mace daga miji ne  ni kuma bazan ta'ba bada wannan damar ba .. "

"Sauran kwanaki  goma a daura maka aure da maryam  a lissafina gobe  ko jibi jirginka zai cale zuwa qasar  france  fatana allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya shahida ta  gama shirya komai na aure  fatan alkhairi da dawo da niyyar  angeancewa lafiya and if you do anything  stupidty I will del with you kai ma kasani ina sonka fiyye da tunaninka amman hakan baya hana idan kayi ba daidai ba naki hukuntaka tana qoqarin mikewa hisham ya shigo ya gaishe da mami cike da girmamawa sannan ya zauna kusa da ata  daya   runtse tsumammun idanunsa tun byn da mami ta soma magana "yaakayi mutumina ya karfin jikin hope you are getting better?"numfashi kawai ya sauke wanda Ke nuna masa alamun ya amsa hisham ya cigaba da magana "har yanzu sultan da fahad basu dawo da komai ba fa  Kmr ma sun dauki abun matsayin shiririta tsabgogin gabansu kawai suke."

"ina sane da komai kai kasan bana canza maganata ina jiran na dawo daga france ne suna zaune suna hira mb ya shigo haka ma yaya Ibrahim ya shigo duba jikin mr ata tare da aunty abida har da yesmin wacce ta dane jikin mr ata haka ma yammatan gidan
d'aya byn daya  suka dinga shigowa suna gaisheshi da kyar yake bude bakinsa   yana amsa musu cikin rashin sakin fuska , cikin wasu  mintuna  aka cika gaban mr ata  da kayan motsa baki , amman babu abinda yaci  illa coffee daya dinga  tsiyaya a  cup yana  kurba ahankali ahankali   shima yana  sha ne kawai saboda  sabon da yayi dashi ."

Parlour'n ya dan rage mutane  ya saura daga hisham sai ata   nuzla da diyana  har ma da mrym da nana hauwa'u suka  shigo parlour'n bakinsu  d'auke  da sallama hisham na ganin nuzla ya saki fuskar  ganin masoyi yarsa  gbdy suka hada baki wajen yi ma mr ata ya jiki  banda nuzla  Kmr koda yaushe da kyar ya amsa  masu hisham  yana kallon fuskar nuzla yayinda  nuzla taja ta tsaya daga gefe can ta jingina bayanta da bango ta rungume hannuwanta duka bisa kirjinta tare da tsura ma mr ata  fararen idanunta tana kallonsa cike da matsanancin soyayyarsa  yadda ko kallon mrym da zai aura bai yi ba  abun yayi mata dadi sosai yadda bai son mrym abun na mata dadi har yana bata kwarin gwiwa dan tun daga ranar daaka saka ranar aurenau take jin haushinta sannan take cikin damuwa mai tsanani  ."

ahankali ta bud'e bakinta tace "yaya  sannu ya jiki banza yayi mata Kmr bai ji ba nan kuwa yaji sarai hisham yayi qasa da murya  yace "ata ana maka sannu da jiki "naji !ya fad'a atakaice  dan ya fahimci wani abu a attare daita ba tun  yau ba  yana hankalce da irin kallon da take masa a duk sanda zasu hadu tun a office din aunty shahida yaso yaci ubanta allah ya taimaketa "take gabanta ya shiga fad'uwa sbd fargaba dan ganin ko kallon inda take tsaye bai ba illa kur'ban ruwan coffee  daya cigaba dayi kuma taji amsar daya bawa hisham kuma tasan sauran ma
sunji abinda ya fad'a  ."
Chapter 60 · 0% Book details