← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 54 OF 100

Sashe 54

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

bata   kulani  ba  har  na  dasa aya ta fuskanci  bilkisu  yayinda  gabadaya  yanuwanta   kacokan  suka  maida  hankalinsu Kan  ussein  duk  sun qagu  suga hukunci  mahamud  akan  ussein kasancewarsa  soja ,  hjy  rahma  ta  matso  sosai  kusa da  bilkisu tana cewa  "ba  dai  ni  zaki  wulakanta   akan namiji  ba ? ."babu  irin  rarrashin da ban miki ba ,babu  irin  hakurin da ban baki ba ,me  kike  son  dani  ? "wallahi  zanyi  dake  bilkisu , yau  zaki ga tozarci  ganin  idanunki  tunda kika nemi ki  wulakantani akan wani banza  can  wanda  ba kowan kowa  bane  shi  ,ba kowa bane  iyayensa   a  duk  fadin  garin nan hasalima rayuwarsa  a  banza take ."

"zaki  wulakantani  akan  wani nmj banza da  wofi  wallahi  zanyi  dake muddin  kika  ce  shi  zaki aura sai na  tsine  miki  na  tsinewa  auren ,wallahi auren  bazai  ta'ba  yin albarka tana  mgn  tana   zabga mata  mari a fuskarta da bayan hannunta  , yayinda  azaba tasa bilkisu ta shiga  karewa  dan kar marin yayi mata illa amman matar nan sai zabga mata maruka take kuma a fuska na rantse miki da girman allah maryama tayi mata mari yafi guda tara ajere ana goma ne bilkisu ta rike mata hannu kuma nasan azaba ce tasa tayi haka ,aiko matar nan ta  danneta da iyakacin karfinta ta dinga dukanta  tana cewa ni zaki rikewa hannu in sha allahu kema sai ya'yanki sun miki abinda kika min ,sai sun hanaki kwanciyar hankali kamar yadda kika hanani kwanciyar hankali a karshe  kafa mata hakori a  damtsen  hannunta."

"wani irin  gigitaccen  qara  bilkisu ta saki mai ban  tausayi  tana  kuka  tana neman  d'auki  gashi  babu wanda ya  kwaceta  daga  hannun mahaifiyarta sai dukanta  take tana hadawa  da  zagi  ganin  haka yasa ussein  ya  nufi   hjy rahma cikin tsananin  fushi  kamar mayunwanci zaki  idanunshi  sun kad'a sunyi jajur   yasa  duka hannunsa zai d'agata  daga  Kan  bilkisu ai  ganin ya  ta'ba  mahaifiyarsu  gbdy yan'uwanta  suka yo Kanshi shi da  bilkisu  cike  da  jin haushi suka dinga dukan su  kamar zasu kashesu suna furta mahaifiyarmu zaka  duka ? azahiri gaskiya ba wai dukanta yayi  ba  kawai ceton bilkisu zai yi  daga dukanta, ina kuka ina basu  hakuri ina qoqarin kwatarsa daga hannunsu amman ina sarkin yawo yafi sarkin karfi dan sai suka daina dukan bilkisu suka cigaba da dukansa  shi kad'ai har sanda hjy  ta shigo zubewa tayi kasa tana kuka tana cewa "zaku kashemun d'a ne to wallahi idan kuka kasheshi hukuma ce zata rabamu  daku dan wallahil azim  bazan ta'ba  yarda ba ".

"kar Allah yasa ki yarda daman kece uwar matsiyaci ?  "nice  uwarsa  kuma  gatansa kuma ni d'ana ba matsiyaci bane dan me zaku masa haka ?
"ai yarku zaku jawa kunne ta daina zuwa inda yake shi meye laifinsa ? "laifinsa kulata da yake yi idan baya  kulata bazata zo inda yake ba ,idan yace baya sonta karta sake zuwa inda yake ni nasan bilkisu bazata zo inda yake  ba ki fad'a masa da babban murya ya rabu da kanwarmu  ya zauna lafiya idan ba haka ba zamu 'batar dashi agarin nan ,kina ji kina gani zaki rasa d'anki har abada  "hjy  na fad'a 'yanuwan bilkisu na maida mata martani kuma basu daina dukansa ba ."

"neman layin 'yanuwasa mata na sake yi saadatu na d'auka na saka mata kuka ina cewa "bazaku zo ba sai an kashe maku da'nuwa ?dan girman allah kuzo ku hanzarta karku bari su illatashi "bilkisu cikin kuka ta rarrafa ta rike kafafun mahamud domin duk yafi dukan ussein cikin kuka tace "yaya dan girman allah kayi hakuri ka barshi karku kashe min rayuwata sannna karku rabani da dashi wallahi bashi da laifi nice mai laifi" .

"ya salam! ya furta a matukar fusace "wai bilkisu me ke damunki ne  "?ta girgiza masa kai idanunta na zubar da ruwan hawaye  kuyi hakuri nayi maku alkwarin bazan sake zuwa inda yake ba "muryar hjy rahma ta sake karade d'akin Aisha riko hannun makaryaciya  karta gudu shi kuma sheidani ku fito min dashi yau zan nuna masa koni wacece agarin  nan zanga uban da ya isa ya kwaceka Aisha ta riko hannun bilkisu  gam bisa umarnin mahaifiyarsu sai dai bilkisu ta dinga turjewa nan ma wani marin aisha ta kai mata tuni daman fuskarta ta canza jini ya kwanta a duka idanunta ."

Mahamud kuwa qarasawa  yayi inda ussein yake yace ya kama kunnensa ussein ya kama kunensa cikin kaduwa dan gbdy bai fahimci abinda yake nufi ba mahamud yace "you're very stupid I mean kayi frog jump Aishat ashe ma illiterate ne wallahi ko da wasa naji ka qara shiga harkar bilkisu zan mugun baka mamaki  "mugun ma illiterate katon jahili liability kawai a haka zamu bashi aurenta sai kace kwakwaluwarmu ta juye  ai har abada ,ka wuce dashi kaci ubansa ta yadda ko mai kama daita ya gani da mugun mugu zai arce ."

bilkisu na kuka ussein na frog jump nima ina biye dasu ina basu hakuri haka hjy hakuri take basu hankalinta a tashe muna fitowa kofar gida sai ga saadatu da fatima a rude basu tsaya  neman baasi ba dan na rigada na fad'a masu komai  sausauci suke neman masa amman mutanen nan  suka ki banda cin mutunci babu abinda suke zubawa  unguwa kuwa ya cika makil da jama'a yan kallo kowa na fadin albakacin bakinsu wasu suna ganin daidai ne matakin da suka dauka dayawa kuma laifin bilkisu suke gani  ."

wani abu mai daci yan'uwansa suka hadiye  tare da matsowa  inda mahamud yake yana laftawa ussein belt a gadon bayansa "yanzu ina zaku dashi ?In ji cewar fatima  tayi maganar cikin tsananin fushi "zamu tafi dashi inda zamu sake koya masa hankali,"  ya fad'a cike da gadara da isa "amman yana  da kyau mu san inda zaku da d'anuwanmu kafin ku wuce dashi?  Eh ! yana da kyau sai dai  bani da wannan lokacin  'batawa idan aka koya masa hankali zaa iya sanar  daku kuzo ku d'auki abinda ya saura ajikinsa "

Hjy kuka saadatu kuka haka ma fatima muna cikin wannan halin sai ga gali yace shine yayansa suyi hakuri su bar komai a hannunsa zai sa ya rabu daita rabuwa ta har abada ,mahamud yace "da dai ya fiyye masa  kwanciyar hankali dan wallahi na sake dawowa akan case din nan sai dai ku dauki gawarsa" gali yace "to mun gode komai yazo karshe bilkisu ta bude idanunta da  suka mata nauyi  wani marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka tana kallon kowa wanda ni nasan kukan da take alokacin bai wuce na rabuwa da ussein ba ."

fatima ta watsa mata harara hade da kallon banza tana cewa  "kukan uwar me zakiyi wa mutane duk bake kika jawo masa matsala ba  yana zaman zamansa muguwa  azzaluma kin janyo yanuwanki sun wulakanta mana d'anuwan an tozarshi, tunda muke anan unguwar aka haifemu muka girma mukayi aure baa ta'ba wulakantamu ba sai yau kuma duk akanki ,kinsa ana dukansa kamar an samu ganga na rantse da girman allah  matukar ussein..."

saurin toshe mata baki nayi ina cewa  fatima karki rantse  ,cikin fushi ta cire min hannu "ki barni  aunty nayi magana kalli yadda fuskarsa tayi duk jini saboda Allah yau ayita ta qare ta kama kanta ta daina zuwa inda yake ,yanzu da suka zo suna hargagin banza da wofi da wulakanci shi meye laifinsa? yarinyarsu ya dace suyi wa magana ta daina zuwa inda yake dan muddin ta sake zuwa inda yake kafin ku dauki mataki mu zamu dauka dan ba daga sama ya fado ba azzaluman banza kawai kuma allah ya isa tsakaninmu daku tana fad'a aisha na fad'a."dan girman allah fatima  karki sake cewa komai zo muyi magana na janyo hannunta " babu inda zani aunty ayita ta qare gwama su san muma bama son wannan diyar tasu kuma komai zai faru ..."
na sake toshe mata baki "dan Allah ki bar mgnr nan  sulhu ake nema ."

Cikin ko in kula hjy rahma tace  da wa zakuyi sulhu ?"kema  Kinsan ruwa ba sa,an kwado bane baku kai wannan matsayin ba yanzu ma wannan maganar da nake duk sai na fashesa akan wannan matsiyacin "nayi tsuru tsuru ina dubanta "tsayuwar  me kukeyi ku taho min  dashi da sauri  gali ya qaraso inda take hjy ai mun gama magana da yaronki, dan allah hjy kiyi hakuri ,in sha allahu tunda muka shiga cikin zance komai yazo karshe zanyi magana dashi  "babu irin hakurin da baa bawa hajiya rahma ba amman  tace sam sai an tafi dashi haka muna ji muna gani aka watsa useein abayan boot din mota aka wuce da
ussein ."

Kuka sosai maryama take kamar alokacin komai ya faru Kwantar da kanta umma tayi akan cinyarta tana rarrashinta "tabbas Aunty masoyiya ce ta gaskiya ,ta so mahaifinmu a halin babu ,ta zauna dashi har karshen rayuwarsa wallahi ba kowani d'an mai kudi bane mutumin kirki kamarta ,ta tsaya ta dubi mahaifinmu da kalmar so ta gaskiya
sai dai akwai illa umma Aunty ta jefa rayuwarta cikin matsala wanda a yanzu take shan wahala ".

" tabbas shine gskiyar dana dade ina nuna mata "baa jayayya da iyaye data yi hakuri tabi umarnin iyayenta tabbas zasu sauko dan kansu kasancewar akwai rabo a tsakaninta da mahaifinku ,cikin muryar kuka tace "mune silar jefa rayuwar mahaifiyarmu cikin wahala ko ? ta fad'a tana sheshekar kuka "karki ce haka maryama haka tata qaddarar take ,ita qaddara gata ko arziki ko nasaba bai isa ya canza maka ba ."umma ta numfasa sannan ta cigaba da magana ".

Bangaren su  bilkisu kuwa tunda suka dauki hanya  yan'uwanta suke magana suna zagin ussein cikin kuka bilkisu Ke rikon su "ku sani ussein bai muku laifin komai ba dan allah karku hukuntashi akan abinda bai yi ba"  mari mahaifiyarta ta kifa mata haka ma aisha dan ubanki ki kama mana baki har suka kai gida zaginta suke direba na ajiyesu ya wuce da mahamud da ussein ."
Chapter 54 · 0% Book details