← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 59 OF 100

Sashe 59

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

aunty  ta  kallesu  ta  girgiza  kai "wallahi  wannan ba rayuwa bace kin  wani  zauna  ya  tasaki  gaba  yana  miki  zakin  baki  ,wallahi ki daina  biye  masa  Ke  macece dole  kina  bukatar  Kiyi  aure shifa nan  gaba  kad'an  zai  ce  zai  yi aurensa  dan  wannan  da  son girman  tsiya  nasan .."no no aunty karki  hadamu da  heartbeat  babu wani  aure  da  zanyi  na  barta  idan  dole  sai  tayi  aure  ni  zan kawo  mata  miji  wanda  zai  dinga kwantar  mata  da  hankali  duk ranar da  yayi  gangancin ' bata mata  rai  na  zage  naci  ubansa ".

"Lah  lah  lallai  habib  abun  naka babba  ne  "allah  aunty  sai ma ya cika  qaidodina  sannnan "wannan  ai  gara kuje  kuyi  auren  kotu  ku  huta maryama  tai  murmushi  tana jin dadin  yadda  dan'uwanta  ke tsananin   qaunarta  "babu kotun da  zamu amman dole a kular min  da  heartbeat ko kuwa a tashi mutun aiki "uhm  kaga   tashina  ta  mike  tsaye  "  bari  naje na bawa  baba  gali da hassana  hakuri na dawo ."

"haba  aunty  ai  komai  ya  rigada ya wuce  wani  hakuri  kuma  zaki basu   salon  su  samu  damar ci miki  mutunci  "? A'a  sai  naje  zaman  lafiya  yafi  zaman dan sarki  ina  zan  iya  dasu  gara dai naje ."Yauwa  aunty  kije  ki basu hakuri  wannan  ai ba komai bane wata  rana  sai  labari  kai ma ya kamata  ka bita  kabasu hakuri wani  irin kallo ya watsa mata  yana cewa "allah  kiyaye ai ni .."sai  kuma  yayi  shiru  sakamakon tuna alkwarin  da  yayiwa  mahaifiyarsu ."

"ai  babu  abinda  zai  sa  naje da habib  sai ya  qara  dagula  lissafi sunan wani police a isokoko ni na wuce sai  na   dawo "to  aunty sai  kin  dawo  tasa kai ta fice daga dakin  ta barsu suka cigaba da hirarsu mai  cike  da  kulawa da soyayya shi kam mlm yahuza tsawon mintuna nan duk yana tsaye  yana jira   Fitowar maryama ya  duba  agogon  dake  daure da  taintsiyar  hannunsa  yaga lokaci  ya  tafi  daman  kuma  yaron daya  aika  ya  sheida  masa komai  dan haka a natse ya juya sai dai ya kudurce aransa  zai  dawo  gobe."

Ahankali  aunty  take  tafiya  tana tunane tunane abinda zatace idan ta isa gaban baba gali a natse tayi sallama  cikin  bangaren  nasu  basu amsa  mata sallamar ta  ba  dan haka  taji  gabanta ya shiga faduwa  kafin ta kai ga yin wata  magana taji aunty salma ta hau surfa mata maseefa  kamar kullum "me ya  kawo  bangarenmu  "ba komai bane  hakuri nazo baku akan  abinda  habib  yayi ,ya gama ci mana mutunci a gabanki shine  dan  munafurci  kika kwaso  jiki   bayarwa  , shegiyar  munafuka kin wani marairaice  fuska    bayan kin gama zuga d'anki yayi mata walima ta uwa da uba zaki wani kwaso jiki to yanzu hakurin  me kika zo bamu  ?".

Numfashi aunty ta sauke ta samu waje ta zauna kusa da baba gali da ko kallon inda take bai yi ba a tun sanda ta shigo "kuyi hakuri gabadayanku in sha allahu nayi maku alkawarin wannan shine karo na farko da karshe da hakan zai faru ...."dakata  bana son jin komai daga  bakinki  dan duk abinda zai fito daga cikinsa karya ne ni dai abinda nake buqata "ki dauki yayanki ku bar mana gidanmu tunda ussein yake raye bai tsina mana komai ba sai tujara gashi nan ya barwa dansa tsaraba har kamar ni wannan yaron zai dinga gasawa magana kuma a gabanki kina kallo  yaron da ya kamata kiyita dukansa har sai kin kusan auna shi lahira amman kika zauna dan tsabar son ya'ya kina kallonsa yana surfa mana zagi ta uwa da uba  ai wallahi bazai yuwu ba ."

Sake durkushewa tayi Kmr zatayi kuka batare da tasan abinda zata sake fad'a ba sai dai ita kanta a halin yanzu tana mai bakincikin hada  zuria dasu tsaki aunty salma  taja tana cewa "munafukar banza  munafukar wofi sai anyi magana ki wani  durkushewa mutane  "ni dai ba wani tashin hankali nazo dominsa ba nazo ne dan na baku hakuri dan nasan danku bai kyauta ba "ni wannan yaron ba d'a bane domin kuwa d'ana bazai min haka ba hakuri aunty  tayita basu da kyar baba gali yace komai ya wuce amman tajawa habib kunne aunty salma dai ce taki  hakura   ta mike tana masu sallama "sai da safenku allah kuma ya huci zuciyarku babu wanda ya kulata acikinsu har ta fice zaginta aunty salma take cikin tsananin tsana  ."

Daga bangaren baba gali na aunty hassana ta shiga itama dai  tujara  tayi  mata  ta uwa da uba kaf danginta  babu  wanda ta  bari  bare iyayenta zuciyarta  tayi  nauyi  kamar an d'aura mata dotse da kyar ta yunkura ta mike ta fito tana tafiya zuciyarta na  kokawa. a inda aunty ta fita ta bar yaranta anan ta dawo ta samesu zaune  suna  hira "har  kin  dawo  aunty  ?suka  had'a baki murmushi  tayi  tare da d'aga  mata kai  alamar" eh! my princess na dawo ".

"Yaya  kuka  qare fatan sun hakura "Eh to  sun hakura my  princess!ta fad'a zuciyarta cike da raunin kuka dan shi take bukatar yi a halin da take ciki  shi kam habib bai ce uffan  ba  illa  ya  cigaba  da  sauraronsu"my princess Kinga dare yayi  bamu  samu  girka komai  a gidan nan  ba ni yanzu ban san me zamu dan girka muci  ba "wallahi  aunty amman bari naje wajen Ummah watakilla bazamu rasa abinda zamu ci ba maryama  ta fad'a  idanun  habib  yana  kanta "ko  zaka   raka ni ne? ta  fad'a tare da miqewa..."Muje ! kawai abinda ya fad'a kenan maryama tayi murmushi "makalema kawai  "kima  ce  bita zai zai  ki  huta  gbdy muje  suka jera ."

Suna  fita suka had'u da yaya sadam  ya  fito  daga side d'in  din baba gali zai shiga side din ummah cike da farinciki habib ya qarasa suka gaisa! "A she rabon mu had'u ne yaya yasa heartbeat tace nayi mata rakiya ."ai ko baka fito ba  yanzu  nake  shirin  zuwa  tambayarka a wajen  aunty !Ya mika masa hannu ya kwana biyu  ina  fata dai komai  lafiya? "Lafiya  lau  habib  kawae aiki ne ya  boye  ni 2days ya karatu ?yace "alhamdulillah.!"

maryama ta bude baki da kyar ta gaishesa ya amsa mata cike da sakin fuska "Lafiya  su aunty maryam"ji tayi kunya ya kamata da kirata aunty da yayi ! Ya gida da karatu ?Alhmdllh! ta fad'a  cikin jin kunya"kema dazu   nake tambayarki  wajen Ummah take bani labari mai dadi lallai kin fita zakka acikin matan gidan  nan kin tsaya kinyi karatunki yadda ya kamata allah yasa muji sakamakon mai kyau you're  the  best  maryama  duk nmj daya sameki a matsayin mata baqaramin dacewa yayi  ba Allah yasa sawa karatu albarka dad'i maryama  taji sosai  dan duk cikin yanuwanta sadam ne kawai sai habib Ke mata fatan alkhairi idan wani abun farinciki ya sameta tace "na gode  sosai yaya ."

Habib yace "a she dai yaya  ka  gane  shiyasa sai  na zaba mata na durje mata  miji  dan ita din ba kalar kowani nmj bace "kaga yaya karka kulashi  mu je ciki  mu  qara gaisawa "wucewa sadam yayi side d'in Ummah  maryama da  habib  na biye da shi sunata hiran duniya..."

Zama sukayi a parlour'n  sadam ya fara kiran  "Ummah  Kina ciki ne? Eh! Ganin nan  zuwa dan albarka har ka dawo ne? sadam yace" eh ! gashi na  kawo  miki maryamarki "ban gane ka kawo min maryama ba maryama da muke yini tare dan gulma zakace ka kawo min ita Bari dai nazo ganin nan fitowa ."

Bata  wani bata  lokaci ba ta fito cikin  doguwar riga  qaton  tray ta aje  a gaban sadam  na fruits bismillah  sannu da zuwa yau har da habib  to duk sannuku "Ina yini "Habib  yace " lafiya lau  habib Ummah ta kalli sadam ta kalli maryama  sai taga sun maseefar dacewa ina ma su kasance maaurata suna hirarsu gwanin ban shaaawa  habib ya fahimci  maryama kunyar sadam take ji sosai dan taki fad'ar abinda ya kawo su gashi shi yunwa yake ji ."

Maryama  tace after dad  ya kamata mu wuce dare nayi  "a'a  har  zaku  tafi kenan maryama  to ai  bakuci  komai  ba "karki damu Ummah  "ban  gane  karta  damu  ba kinga nifa banason kunyar nan  take wai ma wa Kike jin kunya anan  umma  ko  yaya  sadam ,?maryama tayi shiru tana mai sunkuyar da kanta qasa tana wasa da yatsun hannunta "kinga  Ummah  nan ya fad'a  mata abinda ya kawosu "kai maryama  amman shine zaki jashi ku wuce to  kuci me idan kun wuce?  allah ya kyauta wannan kunyar taki  kaga habib bari nazo ta fad'a tana mikewa tsaye ta nufi kitchen ".

Bata wani bata lokaci ba ta dawo hannunta d'auke da wani madaidaicin kula cike da abinci sannan da wata leda cike da su cincin  wanda tayiwa sadam ta miqa ma maryama tace gashi  kai km habib ka  rike kula " mungode Ummah !Suka fito maryama nayi masa mitar abinda  yayi  dariya kawai  yayi yana cewa "ina ganin gara  kawai  ayi yar gida mu huta da samari masu  mana patrol  "kai dai kasani  ni nasani ko gaskiya suna tafiya suna jan juna har suka qaraso falonsu  habib ya zauna yana kiran "washhhh allah maryama ta cire hijab dinta ta ajiye  akan kujera  tace "habib bari na kira aunty  kanshi kawai ya gyada mata ."

Ahankali ta shiga d'akin sai dai abinda yayi matukar daga mata hankali shine ganin mahaifiyarta kwance rigingine akan katifa hannunta rike da wani hoto tana kallon hoton hawaye na zuba daga idanunta  tana tuna irin rayuwar dadin da tayi ada kafin shigowar ussein rayuwarta ,bata haskowa kanta irin rayuwar da take ba sai data hadu da ussein soyayyarta ta gurba tunaninta ."

yayinda maryama ke kallon mahaifiyarta da ita kadai ta rage mata a duniya yanzu a natse ta qara taku biyu domin son ganin hoton waye a hannunta take kallo tana kuka  wasu mutane tagani guda biyu cikin shiga na alfarma suna cikin koshin lafiya da farinciki ko baa fada mata ba tasan hoton iyayenta take kallo cike da nadama lumshe idanunta tayi "iyaye ba abun wasa bane , aunty iyaye suna da kimar da darajan da  bazaa iya mantasu ba ."
Chapter 59 · 0% Book details