← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt Local reading mode
READING PART 37 OF 100

Sashe 37

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read

    "me yasa ?saboda me kar aje neman auren  ?"
Meye  damuwarki da aurensu ? kanta ta rike da duka hannuwanta ta fuskancesa cikin sanyin murya tace "sbd sultana né bazan só ATA ya auri wata ya bar sultana ba "ita sultana tana son shi ne ?eh ammm daman umma ce ke ...."sai km tayi shiru ta kasa qarasa mgnr. "auren nan fa kamar anyi shi an gama domin babu wani abu ko mahalukin daya isa ya hana wannan auren mami da kanta ta hadata wannan auren ,ATA nason yarinyar ko baya sonta wannan shine bansani ba amman zuwa neman aure wannan dole ne gara ma ki binne duk abinda ke ranki karki shigo da wata magana da zata janyo matsala cikin jin haushi tace "idan kuma rabon sultana né fa ?har ya bude baki zai bata amsar tmbyrta  wayarsa ta sake daukar  qara ya dauka yana duba screen din wayar sunan ATA yaga yana yawo cikin sauri ya mike ya dauka ya soma mgn yana juyawa zuwa kofar fita tana ganin fitarsa ta  mike tsaye ta soma zagaye falon tana maimaita abinda  ya  fada mata ashe kuwa zaayi wulakanci acikin gidan nan ko ta wani hali koda tsiya koda tsiya tsiya sai tayi duk abinda zatayi sultana ta shiga gidansa koda ata biyu ce ."

*****
  "Maryama kyakkyawar budurwa ce mai   kyan  gaske  doguwa ce sambal dan tsawonta bai sa  ta  rankwafa ba sai dai ita din ba fara  bace haka zalika baza'a  kirata  da baka kirin ba  chocolate colour ce  tsayinta ya fito  sosai  domin irin matan nan ne masu  shape din cocakola  tana da siririn  hanci  da manya  idanuwa masu  matukar d'aukar hankali  dan duk wanda tsautsayi yasa ya kalli  cikin kwayar idanunta sai ya kusan  suma saboda wasu sirrika da Allah ya hallita acikinsu masu kallon cikinsu  ne kawai zasu iya karar da yanayin da suke tsintar kansu ."

idan tayi murmushi kuwa zaka ga siraran wushiriyarta sama da kasa sun bayyana wanda  sune suke  qara  haskaka  kyawunta  ,ga gaban  goshinta kwance suke  da suma  luf luf !! duk  da kanta a daure  yake a koda yaushe da d'ankwali  amman kallo  daya  zaka  mata  ka  gano irin matan  nan  ne  masu  yalwan  gashi  sannan tana  da  kafa  mai kyau haka ma   yatsun  kafafunta zara zara ne  lullube  da farata masu matukar haske haka zalika muryarta idan tana  magana dan dole ka tsaya ka saurareta  kuma dole ka kalleta ."

Maryama ta  samu tarbiya mai kyau  daga  gurin  mahaifiyarta tayi  karatunta na   primary  har zuwa  matakin  jami'an  acikin jahar lagos  kuma   duk  akarkashin kulawar  gwanaty  , haka bangaren karatun  alqurni  baa  barta abaya ba  domin tun tana primary ta sauke alqurni  km hakan bai sa ta daina zuwa islamiyya ba idan kaga bataje ba sai dai wani aiki ne ya sha kanta ."

    kyawun maryama mai  tsayawa ne arai sai dai duk da wannan kyawu  nata bata da wani  tsayayyen saurayi  duk wanda yazo  neman aurenta dayazo sau d'aya zuwa sau biyu zai daina zuwa  batare da wani dalili ba  koma  karshe  taga  ya koma gurin kaulat diyar  kanwar   babanta  Aunty  hassana  gata   da kyau sosai na bugawa a jarida amman  mutane  na  mata  kallon  mai bakin  jini  abun yana d'an  damunta  sai dai bata nunawa dan ba samari bane a gabanta karatunta  ya fiyye mata  komai mahimanci  koda yaushe ka kalli fuskar maryama  zaka ganta a daure sakamakon rashin farinciki shiyasa  mutane  suke mata kallon mai  tsananin girman  kai   ."

Sannu  ahankali  maryama take tafiya tamkar tana  jin tausayin qasa  ko  macijiya dan babu wani karfi  a tattare daita cikin shiga ta Kamala  riga da sket dinki zamani da  kuma  dogon  hijab  mai  hannu  har  qasa  fuskarta  manne yake da bakin  nikaf  kalar hijab din jikinta wanda ya zame mata jiki a duk sanda zaka ganta a waje ko a makaranta   da wannan nikaf din zaka  ganta  sam bata yarda ta fita koina   batare dashi  ba  a cikin gidansu ne kawai zaka iya ganinta sadaka  yayinda  kafad'arta Ke makale da  jaka baka mai dogon igiya ,a zahiri kana kallonta kasan a matukar gajiye take dan yanayin tafiyarta ma ya qara yin slow sa'banin na sauran lokuta  sakamakon ranar data kwaso  gefe da gefenta  qawayenta ne  subai'a  da sumaiya ne suka sakata a tsakiyarsu ."

   Tafiya  suke  a natse  suna hirar  yadda  jarabawar su ta qarshe  ta kasance adaidai jeaction din ummahani street   suka rabu da kawarta  sumaiya tayi hanyar hagu da zai kaita unguwar daji suka cigaba da takawa da subai'a itama dai tafiya kadan sukai tayi dama wato markaz ya saura ita kadai ta cigaba takawa zuwa  unguwarsu market street batayi  wani  doguwar tafiya ba ta  qaraso  unguwarsu bata tsaya akoina ba sai   kofar  qaramin  get din gidansu  wanda  kallo daya zaka masa  kasan na masu rufin asiri  ne  dan bazaa kira gidan da gidan mai kudi ba haka zalika bazaa kiran gidan  da gidan  talaka fútik ba daidai misali  gidansu   ginin  da ne kuma ginin kasa ne  filasta  ne ya rufawa ginin gidansu asiri da kuma jamar dake rayuwa  acikin  gidan ."

a natse ta  shigo  haraban gidan nasu idanunta ya sauka akan kaulat  wacce  ta sha kwaliya cikin atamfar  chiganvy gold black touch of milk  ,kallo daya tayi masu  ita da wanda ta gani tsaye ta dauke   idanuwanta  zuwa wani bangaren  tana cigaba da tafiya dan wanda suke tsaye  da kaulat din ba bako  bane a wajenta tasha ganinsu tare  ."duk da   bilal  baya ganin faukarta amman  duk  sanda ya ganta yana rasa natsuwarsa a kullum burinsa yaga fuskarta yaga yaya take ,kasa cigaba da motsi yayi  daga inda yake tsaye  yabi tafiyar maryama da wani irin  kallo  komai nata a natse  most especially tafiyarta abun burgewa shi kam ina ma zata yarda ko sau d'aya ta bude nikaf din  yaga fuskarta yasan zatai kyau duk da  bai  ta'ba ganin  fuskarta ba."

Kaulat  na ganin irin kallon da yake mata  taja  dogon  tsaki yayinda maryama bata sake  duban inda suke tsaye ba ta cigaba da tafiya zuciyarta na matukar jin tausayi kaulat dan babu abinda tasa gaba sai  aikin tara masu samari  marasa inganci  a gida  maimakon tai concentrate akan  karatunta da kullum yake yin baya   sai ta maida hankalinta ga tara  samari  marasa amfani , tare suka  shiga  jss one  ,sukai  jss1 tare, sukai  jss 2 tare  sukai exam na zuwa  jss3  ta barta suka  wuce ss 1  ita  da sakina itama sakina lokacin  da zasu shiga ss2 tayi fail ta  wuceta  sai dataje ss3  sannan  kaulat   taje  ss1 sakina taje ss2   gashi  ita  yanzu daga rubuta jarabawar karshe ta fito  amman  ita  kuma har kullm cikin repeating take a qalla a tunaninta tayi repeating  ya kai sau hudu   allah yayi  mata jarabawa ta rashin ilimin  dan  babu  abinda tasani  daga bokon  har islamiyyar zero ce amman  ita da mahaifiyarta kullum cikin cin zarafin mutane suke barin ma ita  da tarasa dalilin dayasa suka  tsaneta suka tsani ganin wani  tare daita  duk wanda zasu gani tare daita wala mace wala nmj sai  sunyi qoqarin rabasu "

"Wai bilal meye haka ne ? ka wani karkace  kai kana kallon maryama gbdy ma ka manta ina tare da kai idan kasan ba wajena kazo ba na qara gaba dan na fahimci duk sanda kaga wucewarta sai ka maida attention dinka wajenta ko zuciyarka na kanta ne sai kayi min bayani  nasani ba wai ka raba hankalinka gida biyu ba alhalin ina tare da kai  "?

"wallahi da tun  asali ita na fara gani  to da babu abinda zai kawoni wajenki  yayi mgnr  acikin zuciyarsa  amman a zahiri cewa yayi  "meye laifi dan kalli halitta mai  natsuwa  ?  ta zaro idanuwata waje  tana masa wani irin kallo kafin  daga baya cikin d'aga murya cike  da  maseefa tace "ko zaka koma  wajenta ne ko me kake nufi da wannan maganar ?da zan samu haka  wallahi da naji dadi sosai "ya sake  fad'a acikin ransa "ai daman haka halinku maza yake da zara kunga mata sai kama 'bare 'bare  to du ka gama 'bare 'barenka ka hakura dan ita wannnan dai ko ka  koma wajenta ma dole ka gudu da kafarka dan idan kasan akanta matsalar  duniya ta qare, kana fara soyayya  daita  komai  daka mallaka  zai  qare idan kayi sa'a ma wani  mummunar bala'i bai sameka ba  tayi samari day day sun kai guda hud'u kuma duk da aure suke sonta amman da zarar sun fara zuwa zance wani mummunar bala'i Ke samunsu ganin ta inda take shiga ba nan take fita ba yasa ya matsota sosai ya rage murya ya soma magana  ."

"Haba kaulat banda sharri fa dan kawai mutun yace yana sonta sai wani mummunar bala'i ya samesa sai kace wata annoba ,wannan ai tafi annoba "to  ko zaki hadani daita kawai ina son naga tasirin bala'in dake tattare daita ?tayi shiru kawai tana nazarin maganarsa idan zata kintata daidai son maryama yake cikin karayar da murya kaulat tace "me kake nufi da wannan mgnr ?ya tsura mata idanunshi kawai "kaga bilal banason wannan maganar karka qara min  hk da kuka ta qarasa maganar dan duk cikin samarinta tafi qaunar bilal "ya salam !meye kuma abun kuka anan daga wasa ?kuka kaulat take sosai ganin haka hankalinsa ya tashi sosai "kinga wallahi ni wasa nake ya ciro hankacip ya mika mata "wip your tears karki min asarar hawayenki da kyar ya samu ya rarrasheta ta daina kuka ."

Da sallama  maryama ta shiga part dinsu inda ta iske habib na  zaune akan wata tsohuwar kujera mai zaman mutun uku  yana ganinta ya saki fuska yayinda aunty ke zaune akan daddumar sallah  , " heartbeat sannu da zuwa "yauwa after dad  ta fad'a tana  cire  nikaf din fuskarta da hijab din jikinta " yau baka fita bane na ganka a gida ?"wallahi na fita ban dai  jima  bane  saboda  ranar  daake  yau  tayi zafi da  yawa "gsky  kam  yau  an zuba   rana ga doguwar tafiyar  mun   kwaso  wallahi a matukar gajiye   nake  da kyar na  qaraso  gida , kasan tun daga dopemu da kafa  muka  shigo agege ya zaro ido yana cewa "halan matsalar mota ?ta gyada masa kai tana rausayar da kwayar idanunta ."
Chapter 37 · 0% Book details