Sashe 37
Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel.txt · about 8 min read
"me yasa ?saboda me kar aje neman auren ?"
Meye damuwarki da aurensu ? kanta ta rike da duka hannuwanta ta fuskancesa cikin sanyin murya tace "sbd sultana né bazan só ATA ya auri wata ya bar sultana ba "ita sultana tana son shi ne ?eh ammm daman umma ce ke ...."sai km tayi shiru ta kasa qarasa mgnr. "auren nan fa kamar anyi shi an gama domin babu wani abu ko mahalukin daya isa ya hana wannan auren mami da kanta ta hadata wannan auren ,ATA nason yarinyar ko baya sonta wannan shine bansani ba amman zuwa neman aure wannan dole ne gara ma ki binne duk abinda ke ranki karki shigo da wata magana da zata janyo matsala cikin jin haushi tace "idan kuma rabon sultana né fa ?har ya bude baki zai bata amsar tmbyrta wayarsa ta sake daukar qara ya dauka yana duba screen din wayar sunan ATA yaga yana yawo cikin sauri ya mike ya dauka ya soma mgn yana juyawa zuwa kofar fita tana ganin fitarsa ta mike tsaye ta soma zagaye falon tana maimaita abinda ya fada mata ashe kuwa zaayi wulakanci acikin gidan nan ko ta wani hali koda tsiya koda tsiya tsiya sai tayi duk abinda zatayi sultana ta shiga gidansa koda ata biyu ce ."
*****
"Maryama kyakkyawar budurwa ce mai kyan gaske doguwa ce sambal dan tsawonta bai sa ta rankwafa ba sai dai ita din ba fara bace haka zalika baza'a kirata da baka kirin ba chocolate colour ce tsayinta ya fito sosai domin irin matan nan ne masu shape din cocakola tana da siririn hanci da manya idanuwa masu matukar d'aukar hankali dan duk wanda tsautsayi yasa ya kalli cikin kwayar idanunta sai ya kusan suma saboda wasu sirrika da Allah ya hallita acikinsu masu kallon cikinsu ne kawai zasu iya karar da yanayin da suke tsintar kansu ."
idan tayi murmushi kuwa zaka ga siraran wushiriyarta sama da kasa sun bayyana wanda sune suke qara haskaka kyawunta ,ga gaban goshinta kwance suke da suma luf luf !! duk da kanta a daure yake a koda yaushe da d'ankwali amman kallo daya zaka mata ka gano irin matan nan ne masu yalwan gashi sannan tana da kafa mai kyau haka ma yatsun kafafunta zara zara ne lullube da farata masu matukar haske haka zalika muryarta idan tana magana dan dole ka tsaya ka saurareta kuma dole ka kalleta ."
Maryama ta samu tarbiya mai kyau daga gurin mahaifiyarta tayi karatunta na primary har zuwa matakin jami'an acikin jahar lagos kuma duk akarkashin kulawar gwanaty , haka bangaren karatun alqurni baa barta abaya ba domin tun tana primary ta sauke alqurni km hakan bai sa ta daina zuwa islamiyya ba idan kaga bataje ba sai dai wani aiki ne ya sha kanta ."
kyawun maryama mai tsayawa ne arai sai dai duk da wannan kyawu nata bata da wani tsayayyen saurayi duk wanda yazo neman aurenta dayazo sau d'aya zuwa sau biyu zai daina zuwa batare da wani dalili ba koma karshe taga ya koma gurin kaulat diyar kanwar babanta Aunty hassana gata da kyau sosai na bugawa a jarida amman mutane na mata kallon mai bakin jini abun yana d'an damunta sai dai bata nunawa dan ba samari bane a gabanta karatunta ya fiyye mata komai mahimanci koda yaushe ka kalli fuskar maryama zaka ganta a daure sakamakon rashin farinciki shiyasa mutane suke mata kallon mai tsananin girman kai ."
Sannu ahankali maryama take tafiya tamkar tana jin tausayin qasa ko macijiya dan babu wani karfi a tattare daita cikin shiga ta Kamala riga da sket dinki zamani da kuma dogon hijab mai hannu har qasa fuskarta manne yake da bakin nikaf kalar hijab din jikinta wanda ya zame mata jiki a duk sanda zaka ganta a waje ko a makaranta da wannan nikaf din zaka ganta sam bata yarda ta fita koina batare dashi ba a cikin gidansu ne kawai zaka iya ganinta sadaka yayinda kafad'arta Ke makale da jaka baka mai dogon igiya ,a zahiri kana kallonta kasan a matukar gajiye take dan yanayin tafiyarta ma ya qara yin slow sa'banin na sauran lokuta sakamakon ranar data kwaso gefe da gefenta qawayenta ne subai'a da sumaiya ne suka sakata a tsakiyarsu ."
Tafiya suke a natse suna hirar yadda jarabawar su ta qarshe ta kasance adaidai jeaction din ummahani street suka rabu da kawarta sumaiya tayi hanyar hagu da zai kaita unguwar daji suka cigaba da takawa da subai'a itama dai tafiya kadan sukai tayi dama wato markaz ya saura ita kadai ta cigaba takawa zuwa unguwarsu market street batayi wani doguwar tafiya ba ta qaraso unguwarsu bata tsaya akoina ba sai kofar qaramin get din gidansu wanda kallo daya zaka masa kasan na masu rufin asiri ne dan bazaa kira gidan da gidan mai kudi ba haka zalika bazaa kiran gidan da gidan talaka fútik ba daidai misali gidansu ginin da ne kuma ginin kasa ne filasta ne ya rufawa ginin gidansu asiri da kuma jamar dake rayuwa acikin gidan ."
a natse ta shigo haraban gidan nasu idanunta ya sauka akan kaulat wacce ta sha kwaliya cikin atamfar chiganvy gold black touch of milk ,kallo daya tayi masu ita da wanda ta gani tsaye ta dauke idanuwanta zuwa wani bangaren tana cigaba da tafiya dan wanda suke tsaye da kaulat din ba bako bane a wajenta tasha ganinsu tare ."duk da bilal baya ganin faukarta amman duk sanda ya ganta yana rasa natsuwarsa a kullum burinsa yaga fuskarta yaga yaya take ,kasa cigaba da motsi yayi daga inda yake tsaye yabi tafiyar maryama da wani irin kallo komai nata a natse most especially tafiyarta abun burgewa shi kam ina ma zata yarda ko sau d'aya ta bude nikaf din yaga fuskarta yasan zatai kyau duk da bai ta'ba ganin fuskarta ba."
Kaulat na ganin irin kallon da yake mata taja dogon tsaki yayinda maryama bata sake duban inda suke tsaye ba ta cigaba da tafiya zuciyarta na matukar jin tausayi kaulat dan babu abinda tasa gaba sai aikin tara masu samari marasa inganci a gida maimakon tai concentrate akan karatunta da kullum yake yin baya sai ta maida hankalinta ga tara samari marasa amfani , tare suka shiga jss one ,sukai jss1 tare, sukai jss 2 tare sukai exam na zuwa jss3 ta barta suka wuce ss 1 ita da sakina itama sakina lokacin da zasu shiga ss2 tayi fail ta wuceta sai dataje ss3 sannan kaulat taje ss1 sakina taje ss2 gashi ita yanzu daga rubuta jarabawar karshe ta fito amman ita kuma har kullm cikin repeating take a qalla a tunaninta tayi repeating ya kai sau hudu allah yayi mata jarabawa ta rashin ilimin dan babu abinda tasani daga bokon har islamiyyar zero ce amman ita da mahaifiyarta kullum cikin cin zarafin mutane suke barin ma ita da tarasa dalilin dayasa suka tsaneta suka tsani ganin wani tare daita duk wanda zasu gani tare daita wala mace wala nmj sai sunyi qoqarin rabasu "
"Wai bilal meye haka ne ? ka wani karkace kai kana kallon maryama gbdy ma ka manta ina tare da kai idan kasan ba wajena kazo ba na qara gaba dan na fahimci duk sanda kaga wucewarta sai ka maida attention dinka wajenta ko zuciyarka na kanta ne sai kayi min bayani nasani ba wai ka raba hankalinka gida biyu ba alhalin ina tare da kai "?
"wallahi da tun asali ita na fara gani to da babu abinda zai kawoni wajenki yayi mgnr acikin zuciyarsa amman a zahiri cewa yayi "meye laifi dan kalli halitta mai natsuwa ? ta zaro idanuwata waje tana masa wani irin kallo kafin daga baya cikin d'aga murya cike da maseefa tace "ko zaka koma wajenta ne ko me kake nufi da wannan maganar ?da zan samu haka wallahi da naji dadi sosai "ya sake fad'a acikin ransa "ai daman haka halinku maza yake da zara kunga mata sai kama 'bare 'bare to du ka gama 'bare 'barenka ka hakura dan ita wannnan dai ko ka koma wajenta ma dole ka gudu da kafarka dan idan kasan akanta matsalar duniya ta qare, kana fara soyayya daita komai daka mallaka zai qare idan kayi sa'a ma wani mummunar bala'i bai sameka ba tayi samari day day sun kai guda hud'u kuma duk da aure suke sonta amman da zarar sun fara zuwa zance wani mummunar bala'i Ke samunsu ganin ta inda take shiga ba nan take fita ba yasa ya matsota sosai ya rage murya ya soma magana ."
"Haba kaulat banda sharri fa dan kawai mutun yace yana sonta sai wani mummunar bala'i ya samesa sai kace wata annoba ,wannan ai tafi annoba "to ko zaki hadani daita kawai ina son naga tasirin bala'in dake tattare daita ?tayi shiru kawai tana nazarin maganarsa idan zata kintata daidai son maryama yake cikin karayar da murya kaulat tace "me kake nufi da wannan mgnr ?ya tsura mata idanunshi kawai "kaga bilal banason wannan maganar karka qara min hk da kuka ta qarasa maganar dan duk cikin samarinta tafi qaunar bilal "ya salam !meye kuma abun kuka anan daga wasa ?kuka kaulat take sosai ganin haka hankalinsa ya tashi sosai "kinga wallahi ni wasa nake ya ciro hankacip ya mika mata "wip your tears karki min asarar hawayenki da kyar ya samu ya rarrasheta ta daina kuka ."
Da sallama maryama ta shiga part dinsu inda ta iske habib na zaune akan wata tsohuwar kujera mai zaman mutun uku yana ganinta ya saki fuska yayinda aunty ke zaune akan daddumar sallah , " heartbeat sannu da zuwa "yauwa after dad ta fad'a tana cire nikaf din fuskarta da hijab din jikinta " yau baka fita bane na ganka a gida ?"wallahi na fita ban dai jima bane saboda ranar daake yau tayi zafi da yawa "gsky kam yau an zuba rana ga doguwar tafiyar mun kwaso wallahi a matukar gajiye nake da kyar na qaraso gida , kasan tun daga dopemu da kafa muka shigo agege ya zaro ido yana cewa "halan matsalar mota ?ta gyada masa kai tana rausayar da kwayar idanunta ."
Meye damuwarki da aurensu ? kanta ta rike da duka hannuwanta ta fuskancesa cikin sanyin murya tace "sbd sultana né bazan só ATA ya auri wata ya bar sultana ba "ita sultana tana son shi ne ?eh ammm daman umma ce ke ...."sai km tayi shiru ta kasa qarasa mgnr. "auren nan fa kamar anyi shi an gama domin babu wani abu ko mahalukin daya isa ya hana wannan auren mami da kanta ta hadata wannan auren ,ATA nason yarinyar ko baya sonta wannan shine bansani ba amman zuwa neman aure wannan dole ne gara ma ki binne duk abinda ke ranki karki shigo da wata magana da zata janyo matsala cikin jin haushi tace "idan kuma rabon sultana né fa ?har ya bude baki zai bata amsar tmbyrta wayarsa ta sake daukar qara ya dauka yana duba screen din wayar sunan ATA yaga yana yawo cikin sauri ya mike ya dauka ya soma mgn yana juyawa zuwa kofar fita tana ganin fitarsa ta mike tsaye ta soma zagaye falon tana maimaita abinda ya fada mata ashe kuwa zaayi wulakanci acikin gidan nan ko ta wani hali koda tsiya koda tsiya tsiya sai tayi duk abinda zatayi sultana ta shiga gidansa koda ata biyu ce ."
*****
"Maryama kyakkyawar budurwa ce mai kyan gaske doguwa ce sambal dan tsawonta bai sa ta rankwafa ba sai dai ita din ba fara bace haka zalika baza'a kirata da baka kirin ba chocolate colour ce tsayinta ya fito sosai domin irin matan nan ne masu shape din cocakola tana da siririn hanci da manya idanuwa masu matukar d'aukar hankali dan duk wanda tsautsayi yasa ya kalli cikin kwayar idanunta sai ya kusan suma saboda wasu sirrika da Allah ya hallita acikinsu masu kallon cikinsu ne kawai zasu iya karar da yanayin da suke tsintar kansu ."
idan tayi murmushi kuwa zaka ga siraran wushiriyarta sama da kasa sun bayyana wanda sune suke qara haskaka kyawunta ,ga gaban goshinta kwance suke da suma luf luf !! duk da kanta a daure yake a koda yaushe da d'ankwali amman kallo daya zaka mata ka gano irin matan nan ne masu yalwan gashi sannan tana da kafa mai kyau haka ma yatsun kafafunta zara zara ne lullube da farata masu matukar haske haka zalika muryarta idan tana magana dan dole ka tsaya ka saurareta kuma dole ka kalleta ."
Maryama ta samu tarbiya mai kyau daga gurin mahaifiyarta tayi karatunta na primary har zuwa matakin jami'an acikin jahar lagos kuma duk akarkashin kulawar gwanaty , haka bangaren karatun alqurni baa barta abaya ba domin tun tana primary ta sauke alqurni km hakan bai sa ta daina zuwa islamiyya ba idan kaga bataje ba sai dai wani aiki ne ya sha kanta ."
kyawun maryama mai tsayawa ne arai sai dai duk da wannan kyawu nata bata da wani tsayayyen saurayi duk wanda yazo neman aurenta dayazo sau d'aya zuwa sau biyu zai daina zuwa batare da wani dalili ba koma karshe taga ya koma gurin kaulat diyar kanwar babanta Aunty hassana gata da kyau sosai na bugawa a jarida amman mutane na mata kallon mai bakin jini abun yana d'an damunta sai dai bata nunawa dan ba samari bane a gabanta karatunta ya fiyye mata komai mahimanci koda yaushe ka kalli fuskar maryama zaka ganta a daure sakamakon rashin farinciki shiyasa mutane suke mata kallon mai tsananin girman kai ."
Sannu ahankali maryama take tafiya tamkar tana jin tausayin qasa ko macijiya dan babu wani karfi a tattare daita cikin shiga ta Kamala riga da sket dinki zamani da kuma dogon hijab mai hannu har qasa fuskarta manne yake da bakin nikaf kalar hijab din jikinta wanda ya zame mata jiki a duk sanda zaka ganta a waje ko a makaranta da wannan nikaf din zaka ganta sam bata yarda ta fita koina batare dashi ba a cikin gidansu ne kawai zaka iya ganinta sadaka yayinda kafad'arta Ke makale da jaka baka mai dogon igiya ,a zahiri kana kallonta kasan a matukar gajiye take dan yanayin tafiyarta ma ya qara yin slow sa'banin na sauran lokuta sakamakon ranar data kwaso gefe da gefenta qawayenta ne subai'a da sumaiya ne suka sakata a tsakiyarsu ."
Tafiya suke a natse suna hirar yadda jarabawar su ta qarshe ta kasance adaidai jeaction din ummahani street suka rabu da kawarta sumaiya tayi hanyar hagu da zai kaita unguwar daji suka cigaba da takawa da subai'a itama dai tafiya kadan sukai tayi dama wato markaz ya saura ita kadai ta cigaba takawa zuwa unguwarsu market street batayi wani doguwar tafiya ba ta qaraso unguwarsu bata tsaya akoina ba sai kofar qaramin get din gidansu wanda kallo daya zaka masa kasan na masu rufin asiri ne dan bazaa kira gidan da gidan mai kudi ba haka zalika bazaa kiran gidan da gidan talaka fútik ba daidai misali gidansu ginin da ne kuma ginin kasa ne filasta ne ya rufawa ginin gidansu asiri da kuma jamar dake rayuwa acikin gidan ."
a natse ta shigo haraban gidan nasu idanunta ya sauka akan kaulat wacce ta sha kwaliya cikin atamfar chiganvy gold black touch of milk ,kallo daya tayi masu ita da wanda ta gani tsaye ta dauke idanuwanta zuwa wani bangaren tana cigaba da tafiya dan wanda suke tsaye da kaulat din ba bako bane a wajenta tasha ganinsu tare ."duk da bilal baya ganin faukarta amman duk sanda ya ganta yana rasa natsuwarsa a kullum burinsa yaga fuskarta yaga yaya take ,kasa cigaba da motsi yayi daga inda yake tsaye yabi tafiyar maryama da wani irin kallo komai nata a natse most especially tafiyarta abun burgewa shi kam ina ma zata yarda ko sau d'aya ta bude nikaf din yaga fuskarta yasan zatai kyau duk da bai ta'ba ganin fuskarta ba."
Kaulat na ganin irin kallon da yake mata taja dogon tsaki yayinda maryama bata sake duban inda suke tsaye ba ta cigaba da tafiya zuciyarta na matukar jin tausayi kaulat dan babu abinda tasa gaba sai aikin tara masu samari marasa inganci a gida maimakon tai concentrate akan karatunta da kullum yake yin baya sai ta maida hankalinta ga tara samari marasa amfani , tare suka shiga jss one ,sukai jss1 tare, sukai jss 2 tare sukai exam na zuwa jss3 ta barta suka wuce ss 1 ita da sakina itama sakina lokacin da zasu shiga ss2 tayi fail ta wuceta sai dataje ss3 sannan kaulat taje ss1 sakina taje ss2 gashi ita yanzu daga rubuta jarabawar karshe ta fito amman ita kuma har kullm cikin repeating take a qalla a tunaninta tayi repeating ya kai sau hudu allah yayi mata jarabawa ta rashin ilimin dan babu abinda tasani daga bokon har islamiyyar zero ce amman ita da mahaifiyarta kullum cikin cin zarafin mutane suke barin ma ita da tarasa dalilin dayasa suka tsaneta suka tsani ganin wani tare daita duk wanda zasu gani tare daita wala mace wala nmj sai sunyi qoqarin rabasu "
"Wai bilal meye haka ne ? ka wani karkace kai kana kallon maryama gbdy ma ka manta ina tare da kai idan kasan ba wajena kazo ba na qara gaba dan na fahimci duk sanda kaga wucewarta sai ka maida attention dinka wajenta ko zuciyarka na kanta ne sai kayi min bayani nasani ba wai ka raba hankalinka gida biyu ba alhalin ina tare da kai "?
"wallahi da tun asali ita na fara gani to da babu abinda zai kawoni wajenki yayi mgnr acikin zuciyarsa amman a zahiri cewa yayi "meye laifi dan kalli halitta mai natsuwa ? ta zaro idanuwata waje tana masa wani irin kallo kafin daga baya cikin d'aga murya cike da maseefa tace "ko zaka koma wajenta ne ko me kake nufi da wannan maganar ?da zan samu haka wallahi da naji dadi sosai "ya sake fad'a acikin ransa "ai daman haka halinku maza yake da zara kunga mata sai kama 'bare 'bare to du ka gama 'bare 'barenka ka hakura dan ita wannnan dai ko ka koma wajenta ma dole ka gudu da kafarka dan idan kasan akanta matsalar duniya ta qare, kana fara soyayya daita komai daka mallaka zai qare idan kayi sa'a ma wani mummunar bala'i bai sameka ba tayi samari day day sun kai guda hud'u kuma duk da aure suke sonta amman da zarar sun fara zuwa zance wani mummunar bala'i Ke samunsu ganin ta inda take shiga ba nan take fita ba yasa ya matsota sosai ya rage murya ya soma magana ."
"Haba kaulat banda sharri fa dan kawai mutun yace yana sonta sai wani mummunar bala'i ya samesa sai kace wata annoba ,wannan ai tafi annoba "to ko zaki hadani daita kawai ina son naga tasirin bala'in dake tattare daita ?tayi shiru kawai tana nazarin maganarsa idan zata kintata daidai son maryama yake cikin karayar da murya kaulat tace "me kake nufi da wannan mgnr ?ya tsura mata idanunshi kawai "kaga bilal banason wannan maganar karka qara min hk da kuka ta qarasa maganar dan duk cikin samarinta tafi qaunar bilal "ya salam !meye kuma abun kuka anan daga wasa ?kuka kaulat take sosai ganin haka hankalinsa ya tashi sosai "kinga wallahi ni wasa nake ya ciro hankacip ya mika mata "wip your tears karki min asarar hawayenki da kyar ya samu ya rarrasheta ta daina kuka ."
Da sallama maryama ta shiga part dinsu inda ta iske habib na zaune akan wata tsohuwar kujera mai zaman mutun uku yana ganinta ya saki fuska yayinda aunty ke zaune akan daddumar sallah , " heartbeat sannu da zuwa "yauwa after dad ta fad'a tana cire nikaf din fuskarta da hijab din jikinta " yau baka fita bane na ganka a gida ?"wallahi na fita ban dai jima bane saboda ranar daake yau tayi zafi da yawa "gsky kam yau an zuba rana ga doguwar tafiyar mun kwaso wallahi a matukar gajiye nake da kyar na qaraso gida , kasan tun daga dopemu da kafa muka shigo agege ya zaro ido yana cewa "halan matsalar mota ?ta gyada masa kai tana rausayar da kwayar idanunta ."