Sashe 39
Karayar Arziki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*_Suhaima_*
Itadai Suhaima akwai banbanci da Lubna, Dan ita amarcin NATA yazo da gargada.
Ashe Ramadan d'an talakawane lik'is, irindai matasannanne masu son k'arya da burgar tsiya, shine Aron kaya shine na mota, dawannan abubuwan yabige tunanin suhaima harta amince ta auresa, Dama kuma tun awaje suke shek'e ayarsu.
Sai lokacin da'aka kaita taganta awani d'an gida kamar BQ d'in gidansu, aiko ranar kwana sukayi tafka bala'i.
Dole washe gari ya yarda suka koma gidanta data samu agadonta itama.
Hakan yamasa dad'i kuwa, Dan kobabu komai ansamu cigaba, dama wancanma babansane Yakama masa Hayar, Dan Ramadan baya aikin komai sai tsalle-tsallen 'yanmata. Sune samarin shaho na wannan zamanin.
('Yammata sai ayi hattara da samarin shaho, Dan akwai irinsu Ramadan dayawa suna yawo cikin duniya).
*_(((S)))......2018_*
*_Luv you all_*
[1/4, 4:45 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_* 💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO.....😜_*
*_page→71-72_*
..........Kiyyyyyy!! Yaja wani wawan birki agabansu. duk arikice suke kallonsa, Salman da shima isowarsa kenan yasa k'asan rigarsa yana toshe hancinsa saboda wata k'ura da Dr jafar ya tayar awajen.
Ganin yanda yafito abirkice yasaka sauran mik'ewa gaba d'aya, har sassarfa yakeyi yana had'a k'afa kamar zai kifa Dan k'ok'arin k'arasawa inda suke zaune.
Saidai kuma yana zuwa garesu kallonsu yacanja akala daga gareshi zuwa bayansa, Hafiz da Kabeer hard'an tureshi gefe sukeyi danson kallon abinda suka gani sosai.
Shima sai kawai ya waiga domin bawa idonsa abinci.
Motar ya Umar ce ta tsaya awajen, gaba kad'an da motar Dr jafar. Fitiwarsace taja hankalinsu wajen kallon mamaki agaresu. Shikam koma Inda suke bai kallaba, ya zagaya inda Asma'u take yabud'e mata k'ofar, fodeyo tafik'o masa, yakar6eshi hannu biyu yana murmushi da fad'in yauwa my dear son! Yau kanashan yawo ko?.
Asma'u tafito tana murmushi, yaya shima aii gara yasan gari ko?.
Cikin kallon k'auna ya ce, ''Kodai ke kinaso kiga garin? yafad'a tareda lakace hancinta.
Dariya sukayi gaba d'aya sannan suka jera atare suka nufi ainahin cikin mall d'in, ya Umar na rungume da fodiyo, ga Asma'u a gefensa cikin farinciki.
Su Hafiz kuwa tamkar sokaye haka suka dafama su ya Umar baya da kallo.
Tun a k'ofar wajen masu bud'e k'ofa suka fara rissinawa suna kwasar gaisuwa wajen uban gidansu.
Shikam cikeda fara'a irinta sanin hak'k'in d'an Adam yake amsawa, da nuna musu iyalinsa. Sunajin haka suka rissinawa suna gaida Asma'u itama.
Acikima bata canja zaniba sai rissinawa ma aikatan sukeyi suna kwasar gaisuwa.
Masu siyayya kam sunyi tsai tsaye suna kallonsu ya Umar d'in.
Wasu 'yammatanma harsun k'yasa😉. (Kunsandai rayuwarnan indai kanada 'Yar daud'ar duniya, to yanzu zakaga 'yan mata Na rawar kai akanka). ALLAH yasa mudace.
Da Sauri sadam yataso ya tarbesu, kar6ar fodiyo yayi daga hannun ya Umar tareda gaishesu.
Cikin zolaya Asma'u ta ce, ''lallai Na Rafi'a dolene kuyi Fari kaida ya Harris, Ashe kullum cikin Ac kuke wuni?.
Dariya sadam yayi, kai antymu kin iya Sheri wlhy, amma nidai bazance komaiba harsai kin bani Rafi'a zakiji bakina.
Dayawan mutanen dake gurin saida suka dara, Asma'u ta birge dayawan mutanen wajen, Dan da watace matar mai irin wannan wajen ai da irin shegen mai girman kannan za'ayi, da d'aukar kai, amma jiba yanda take wasa da dariya da ma'aikatan wajen. Dukdadai da alamar sanayya tsakaninta dashi, amma ta birgesu gskiya.
Ya Umar dake musu dariya ya kamo hannunta, kinga my Husna bar shiriritarnan idan kunje gida kwayi, muje kisayi abinda zaki saya mu wuce.
Kallonsa tayi cikin langa6e kai, yaya sayafa? Muda shagonmu?.
Cikin tsokana ya ce, "kema saikin biya aii".
Juyawa tayi tana kallonsu Harris da hankalinsu gaba d'aya yake kan Fodiyo suda wasu ma'aikata, Baki tad'aga zata kira Sadam, ya Umar yasa hannunsa ya toshe bakin. K lafiyarki kuwa? Mizakiyi?.
Kiransu zanyi naji waye ya kafa dokar?.
Cikin dariya ya Umar ya janye hannunta suka shige wani d'an d'aki, Ashe Office d'insane awajen. K'ofar yamaida yarufe yana dariya, kai my Husna ALLAH ya shiryaminke?.
Itama dariyar tayi tanabin ko'ina Na falon da kallon.
Manya-manyan hotunansu guda biyar tagani a kowace kusurwa ta office d'in, itadashi da fodiyo, akowace kusurwa, saikuma asaman tebur d'in an ajiye wani madaidaici itadashi nanma da fodiyo.
Kallonsa tayi, shikuma ya d'aga mata gira yana murmushi.
Itama ta sakar masa da murmushin tareda zuwa ta rungumeshi, hannu biyu ya kar6eta shima ya k'ank'ame kayansa, burinsa kullum yaga Husnarsa cikin farinci, yarinyar data masa hallacci alokacin damutane masu yawa da muhimmanci arayuwarsa suka gujesa, yarinyar dake sonsa Dan ALLAH badan dukiyarsaba, yarinyar data sadaukar daduk wani farincikinta domin NASA ya inganta, yo idanma yagaza Nuna mata k'auna aii yayi butulci mai yawa.....
Asma'u tad'ago tana kallonsa, amma fuskarta tad'an sauya, cikin langa6ewar kai ta ce, "ya amma banga su twins ba?."
Shima fara'arsa ya rage, sannan ya kauda zancen ta hanyar cewa muje yamma nayi karmu kwasarma fodiyo sanyi yazo yana mura.
Komawa tayi takuma k'ank'amesa, yaya kabani amsar tawa tambayar mana.
Wannan ba maganar nan bace, bari saimunje gida.
Baijira amsartaba yafice abainsa.
Itama dolene ta take masa baya Dan tasan halin kayanta sarai.
Ak'ofar office d'in tasameshi yana jiranta, ahankali suketa zagayawa suna d'aukar abinda suke buk'ata, dawanda fodiyo yake buk'ata, harda Hasiya da inna baito dazata koma gobe idan ALLAH ya kaimu.
Sosai suka Lodi abubuwan buk'ata, suna gamawa wani ma'aikaci yazo ya kar6i kayan, wajen kashiya's yaje Harris da sadam suka kar6a akai total.
Amamakin Asma'u saitaga ya Umar yaje yabasu ATM d'insa sun cire kud'in, aranta ta Ce, "Ashe da gsk yaya yakeyi.
Bayan sungama komai tsaf suna shirin fita saiga Yazeed da Muktar sundawo daga wajen aiki, dama haka sukeyi, idan suka dawo saisu lek'o suga yanda komai yake tafiya kafin sutattafi gida.
Juna suka rungume suna murna.
Muktar ya ce, " mutumina kace soyayya kafito?.
Dariya ya Umar yayi tareda fad'in ALLAH yashiryaka Muktar.
Ameen suka fad'a cikin dariya.
Asma'u ta gaidasu da tambayar aikinsu, duk suka amsa cikin fara'a sannan yazeed yakar6i fodiyo yana fad'in kud'an rakamu wani waje mana kaida madam.
Ya Umar ya ce, ''to aja zuga!, ina kuma zaka kaimi? Mudake shirin tafiya gida?.
Kudai kubiyoni kawai.
Haka kuwa suka rankaya suka tafi, Asma'u Na a bayansu.
Ganin inda suka dosa ya Umar yaja tunga. Cikin had'e fiska yazeed da Muktar sukace babu jayayya a tsakaninmu.
Ya Umar baice komaiba yakad'a kai suka cigaba da tafiya har majallissarsu Dr jafar.
Suna ganin sun nufosu kuwa sukayi gum daga sambatun surutun dasukeyi tun d'azun akan ya Umar.
Hannu sukaita basu ana gaisawa, duk jikinsu yayi sanyi, yazeed yamik'a musu fodiyo, to 'yan uwa gafa Usman fodiyo, ankawoshine shida madam domin Susanya albarka awajen dadynsa Umar daya gyara.
Kalan kallon aka fara, salman d'aya kar6i fodiyo yayi murmishin takaici, aransa ya ce, ''gashi k'yak'yk'yawa kuwa.
Asma'u ta ce, "ya gajiyarku ya iyali? Idan bazaku damuba muna gayyatarku walima ta mik'a godiyarmu ga ALLAH akan ni'imomin daya azurtamu aciki, ga d'aya daga cikinan shine gyara mall d'inmu daya dawo kamarma wuta bata cishiba, na biyu shine ku6utar kayan ya Fharuk daga hannun custom, na Uku shine albarkar haihuwar fodiyo da ALLAH ya azurtamu dasamu.
Yanda take magana adake tayi mugun basu mamaki, shikansa ya Umar kallonta yakeyi cikeda al'ajabi da birgewa, baita6a tunanin matar tasa jaruma baceba sai ayau. Dukda dai yasan dama Asma'u akwai tsiwa, amma azatonsa ta daina.
Muktar da yazeed kam bak'aramin birgesu Asma'u tayiba, Dan sai zabga murmushi sukeyi.
Tana gama fad'a kuwa ta ce, " inafatan zaku amsa gayyatarmu, nabarku lfy, yaya idan kun gama INA mota, tajuya cikin takun girma tabar wajan.
Duk binta sukayi da kallon, saikuma kishi yata6a zuciyar ya Umar, dad'an k'arfi ya ce, "malamai kallon ya Isa haka, ko kun manta matar aurece?.
Ajiyar zuciya suka sauke suduka, kowanne yanamai janye idonsa daga kanta.
Yazeed yamik'a hannu ya kar6i fodiyo dahar yanzu yake a hannun Salman, sai wani k'ara k'ank'amesa yakeyi tamkar nasa.. 😉
Yana kar6a suka bar wajen, acikinsu Dr jafar babu Wanda ya iya koda kwakwkwaran tari har su muktar suka kai ga mitar Ya Umar.
Asma'u naciki yazeed yamik'a mata Fodiyo, sannan ya ce, " madam sannu da k'ok'ari, aibansan haka kema kikeba da jarumta.
Dariya sukayi gaba d'aya, ya Umar ya ce, "tab, ai dama Husna matsiwaciyace, Ku kawai takema alkunya, koba hakaba tawan? Yafad'a yana d'aga mata gira.
Harar wasa Asma'u tama ya Umar ta ce, ''bandadai Sheri my boss."
Nanma dariya sukeyi sosai.
Su Tasi'u duk suna kallonsu, kuma azatonsu su sukema dariyar, Dan haka duk jikinsu yakumayin sanyi, wasuma harsum fara nadamar abinda suka aikata ayau.
Ya Umar yatada motar sukayi sallama dasu yazeed suka tafi.
Dayazo saitinsu Dr jafar ma saida yad'aga musu hannu, amma ko tari babu Wanda yayi acikinsu, Dan duk sunyi gum, tundasu ya Umar suka bar wajen babu Wanda ya iya cewa A acikinsu, saidai kallon kallon kawai da zare idanu.
Nikuwa na ce, "hummmm.
__________________________
Ahanya ya Umar da Asma'u sai hirar abinda yafaru sukeyi suna dariya.
Dahaka har suka isa gida. Ya Umar yakwashi ledojin itakuma tasa6i fodiyo suka Shiga.
Afalo suka iske su hasiya da inna baito sunacin tuwo.
Bayan sun musu hannu suka zauna, ya Umar ya ce, " inna yau tuwo akamana?."
Wlhy tuwo nayi Umaru, nidai nagaji dacin shinkafarnan.
Aii wlhy inna kin taimakemu, nikaina bawani damuwa nayi da irin wad'annan abubuwan naiba, nifa aka bani tuwo to anmin dai-dai. Amma su o, e, aii ba'aso, saidai kayan kwad'ayi.
Asma'u datasan da ita yakeyi, ta cuno baki gaba amma batace komaiba.
Ya Umar yace nidai kar aji haushina bankira sunaba dai ko Hasiya?.
Oho dai, aikowa yay zagi akasuwa yasan dawanda yake. Cewar Asma'u tana Barin wajen.
Dariya suka rakata da ita suduka.
Ya Umar ma yamik'e yana fad'in inna bara na rage kayan jikina naje massalaci, danyau zaman cin tuwo zamuyi.
To Umar afito lafiya.
To innarmu, gobe iyanzu munyi kewarki wlhy, dama kiyi zamanki taredamu kawai, zamuyi farinciki wlhy.
'Yar dariya kawai inna baito tayi, ta ce, "a'a Umar, mijinafa?.
Saidai kuma haka inna, amma jimuke kamar karki tafi. Dariya kawai inna baito tayi. shikuma yashige d'akinsa.
*_Lubna_*
Zaune take a k'ataccen falonta, ta mik'e k'afafu gabanta kayan fruit ne da aka yanka k'anana, gefe kuma ga farfesun kaza daya gama had'uwa.
Itadai Suhaima akwai banbanci da Lubna, Dan ita amarcin NATA yazo da gargada.
Ashe Ramadan d'an talakawane lik'is, irindai matasannanne masu son k'arya da burgar tsiya, shine Aron kaya shine na mota, dawannan abubuwan yabige tunanin suhaima harta amince ta auresa, Dama kuma tun awaje suke shek'e ayarsu.
Sai lokacin da'aka kaita taganta awani d'an gida kamar BQ d'in gidansu, aiko ranar kwana sukayi tafka bala'i.
Dole washe gari ya yarda suka koma gidanta data samu agadonta itama.
Hakan yamasa dad'i kuwa, Dan kobabu komai ansamu cigaba, dama wancanma babansane Yakama masa Hayar, Dan Ramadan baya aikin komai sai tsalle-tsallen 'yanmata. Sune samarin shaho na wannan zamanin.
('Yammata sai ayi hattara da samarin shaho, Dan akwai irinsu Ramadan dayawa suna yawo cikin duniya).
*_(((S)))......2018_*
*_Luv you all_*
[1/4, 4:45 PM] ~🇩 ' 🇯 🇦 🇷 🇭✍: 👩🏻💻.........
💎 *_KARAYAR ARZEEK'I!!_* 💎
*_NA_*
*_Bilyn Abdul_*
*_Sadaukarwa_*
_miss Xoxo na_
_Zarah Bukar_
_Ayusher Muh'd_
*_NIKA'DAI👌🏼 WRITER ASSO.....😜_*
*_page→71-72_*
..........Kiyyyyyy!! Yaja wani wawan birki agabansu. duk arikice suke kallonsa, Salman da shima isowarsa kenan yasa k'asan rigarsa yana toshe hancinsa saboda wata k'ura da Dr jafar ya tayar awajen.
Ganin yanda yafito abirkice yasaka sauran mik'ewa gaba d'aya, har sassarfa yakeyi yana had'a k'afa kamar zai kifa Dan k'ok'arin k'arasawa inda suke zaune.
Saidai kuma yana zuwa garesu kallonsu yacanja akala daga gareshi zuwa bayansa, Hafiz da Kabeer hard'an tureshi gefe sukeyi danson kallon abinda suka gani sosai.
Shima sai kawai ya waiga domin bawa idonsa abinci.
Motar ya Umar ce ta tsaya awajen, gaba kad'an da motar Dr jafar. Fitiwarsace taja hankalinsu wajen kallon mamaki agaresu. Shikam koma Inda suke bai kallaba, ya zagaya inda Asma'u take yabud'e mata k'ofar, fodeyo tafik'o masa, yakar6eshi hannu biyu yana murmushi da fad'in yauwa my dear son! Yau kanashan yawo ko?.
Asma'u tafito tana murmushi, yaya shima aii gara yasan gari ko?.
Cikin kallon k'auna ya ce, ''Kodai ke kinaso kiga garin? yafad'a tareda lakace hancinta.
Dariya sukayi gaba d'aya sannan suka jera atare suka nufi ainahin cikin mall d'in, ya Umar na rungume da fodiyo, ga Asma'u a gefensa cikin farinciki.
Su Hafiz kuwa tamkar sokaye haka suka dafama su ya Umar baya da kallo.
Tun a k'ofar wajen masu bud'e k'ofa suka fara rissinawa suna kwasar gaisuwa wajen uban gidansu.
Shikam cikeda fara'a irinta sanin hak'k'in d'an Adam yake amsawa, da nuna musu iyalinsa. Sunajin haka suka rissinawa suna gaida Asma'u itama.
Acikima bata canja zaniba sai rissinawa ma aikatan sukeyi suna kwasar gaisuwa.
Masu siyayya kam sunyi tsai tsaye suna kallonsu ya Umar d'in.
Wasu 'yammatanma harsun k'yasa😉. (Kunsandai rayuwarnan indai kanada 'Yar daud'ar duniya, to yanzu zakaga 'yan mata Na rawar kai akanka). ALLAH yasa mudace.
Da Sauri sadam yataso ya tarbesu, kar6ar fodiyo yayi daga hannun ya Umar tareda gaishesu.
Cikin zolaya Asma'u ta ce, ''lallai Na Rafi'a dolene kuyi Fari kaida ya Harris, Ashe kullum cikin Ac kuke wuni?.
Dariya sadam yayi, kai antymu kin iya Sheri wlhy, amma nidai bazance komaiba harsai kin bani Rafi'a zakiji bakina.
Dayawan mutanen dake gurin saida suka dara, Asma'u ta birge dayawan mutanen wajen, Dan da watace matar mai irin wannan wajen ai da irin shegen mai girman kannan za'ayi, da d'aukar kai, amma jiba yanda take wasa da dariya da ma'aikatan wajen. Dukdadai da alamar sanayya tsakaninta dashi, amma ta birgesu gskiya.
Ya Umar dake musu dariya ya kamo hannunta, kinga my Husna bar shiriritarnan idan kunje gida kwayi, muje kisayi abinda zaki saya mu wuce.
Kallonsa tayi cikin langa6e kai, yaya sayafa? Muda shagonmu?.
Cikin tsokana ya ce, "kema saikin biya aii".
Juyawa tayi tana kallonsu Harris da hankalinsu gaba d'aya yake kan Fodiyo suda wasu ma'aikata, Baki tad'aga zata kira Sadam, ya Umar yasa hannunsa ya toshe bakin. K lafiyarki kuwa? Mizakiyi?.
Kiransu zanyi naji waye ya kafa dokar?.
Cikin dariya ya Umar ya janye hannunta suka shige wani d'an d'aki, Ashe Office d'insane awajen. K'ofar yamaida yarufe yana dariya, kai my Husna ALLAH ya shiryaminke?.
Itama dariyar tayi tanabin ko'ina Na falon da kallon.
Manya-manyan hotunansu guda biyar tagani a kowace kusurwa ta office d'in, itadashi da fodiyo, akowace kusurwa, saikuma asaman tebur d'in an ajiye wani madaidaici itadashi nanma da fodiyo.
Kallonsa tayi, shikuma ya d'aga mata gira yana murmushi.
Itama ta sakar masa da murmushin tareda zuwa ta rungumeshi, hannu biyu ya kar6eta shima ya k'ank'ame kayansa, burinsa kullum yaga Husnarsa cikin farinci, yarinyar data masa hallacci alokacin damutane masu yawa da muhimmanci arayuwarsa suka gujesa, yarinyar dake sonsa Dan ALLAH badan dukiyarsaba, yarinyar data sadaukar daduk wani farincikinta domin NASA ya inganta, yo idanma yagaza Nuna mata k'auna aii yayi butulci mai yawa.....
Asma'u tad'ago tana kallonsa, amma fuskarta tad'an sauya, cikin langa6ewar kai ta ce, "ya amma banga su twins ba?."
Shima fara'arsa ya rage, sannan ya kauda zancen ta hanyar cewa muje yamma nayi karmu kwasarma fodiyo sanyi yazo yana mura.
Komawa tayi takuma k'ank'amesa, yaya kabani amsar tawa tambayar mana.
Wannan ba maganar nan bace, bari saimunje gida.
Baijira amsartaba yafice abainsa.
Itama dolene ta take masa baya Dan tasan halin kayanta sarai.
Ak'ofar office d'in tasameshi yana jiranta, ahankali suketa zagayawa suna d'aukar abinda suke buk'ata, dawanda fodiyo yake buk'ata, harda Hasiya da inna baito dazata koma gobe idan ALLAH ya kaimu.
Sosai suka Lodi abubuwan buk'ata, suna gamawa wani ma'aikaci yazo ya kar6i kayan, wajen kashiya's yaje Harris da sadam suka kar6a akai total.
Amamakin Asma'u saitaga ya Umar yaje yabasu ATM d'insa sun cire kud'in, aranta ta Ce, "Ashe da gsk yaya yakeyi.
Bayan sungama komai tsaf suna shirin fita saiga Yazeed da Muktar sundawo daga wajen aiki, dama haka sukeyi, idan suka dawo saisu lek'o suga yanda komai yake tafiya kafin sutattafi gida.
Juna suka rungume suna murna.
Muktar ya ce, " mutumina kace soyayya kafito?.
Dariya ya Umar yayi tareda fad'in ALLAH yashiryaka Muktar.
Ameen suka fad'a cikin dariya.
Asma'u ta gaidasu da tambayar aikinsu, duk suka amsa cikin fara'a sannan yazeed yakar6i fodiyo yana fad'in kud'an rakamu wani waje mana kaida madam.
Ya Umar ya ce, ''to aja zuga!, ina kuma zaka kaimi? Mudake shirin tafiya gida?.
Kudai kubiyoni kawai.
Haka kuwa suka rankaya suka tafi, Asma'u Na a bayansu.
Ganin inda suka dosa ya Umar yaja tunga. Cikin had'e fiska yazeed da Muktar sukace babu jayayya a tsakaninmu.
Ya Umar baice komaiba yakad'a kai suka cigaba da tafiya har majallissarsu Dr jafar.
Suna ganin sun nufosu kuwa sukayi gum daga sambatun surutun dasukeyi tun d'azun akan ya Umar.
Hannu sukaita basu ana gaisawa, duk jikinsu yayi sanyi, yazeed yamik'a musu fodiyo, to 'yan uwa gafa Usman fodiyo, ankawoshine shida madam domin Susanya albarka awajen dadynsa Umar daya gyara.
Kalan kallon aka fara, salman d'aya kar6i fodiyo yayi murmishin takaici, aransa ya ce, ''gashi k'yak'yk'yawa kuwa.
Asma'u ta ce, "ya gajiyarku ya iyali? Idan bazaku damuba muna gayyatarku walima ta mik'a godiyarmu ga ALLAH akan ni'imomin daya azurtamu aciki, ga d'aya daga cikinan shine gyara mall d'inmu daya dawo kamarma wuta bata cishiba, na biyu shine ku6utar kayan ya Fharuk daga hannun custom, na Uku shine albarkar haihuwar fodiyo da ALLAH ya azurtamu dasamu.
Yanda take magana adake tayi mugun basu mamaki, shikansa ya Umar kallonta yakeyi cikeda al'ajabi da birgewa, baita6a tunanin matar tasa jaruma baceba sai ayau. Dukda dai yasan dama Asma'u akwai tsiwa, amma azatonsa ta daina.
Muktar da yazeed kam bak'aramin birgesu Asma'u tayiba, Dan sai zabga murmushi sukeyi.
Tana gama fad'a kuwa ta ce, " inafatan zaku amsa gayyatarmu, nabarku lfy, yaya idan kun gama INA mota, tajuya cikin takun girma tabar wajan.
Duk binta sukayi da kallon, saikuma kishi yata6a zuciyar ya Umar, dad'an k'arfi ya ce, "malamai kallon ya Isa haka, ko kun manta matar aurece?.
Ajiyar zuciya suka sauke suduka, kowanne yanamai janye idonsa daga kanta.
Yazeed yamik'a hannu ya kar6i fodiyo dahar yanzu yake a hannun Salman, sai wani k'ara k'ank'amesa yakeyi tamkar nasa.. 😉
Yana kar6a suka bar wajen, acikinsu Dr jafar babu Wanda ya iya koda kwakwkwaran tari har su muktar suka kai ga mitar Ya Umar.
Asma'u naciki yazeed yamik'a mata Fodiyo, sannan ya ce, " madam sannu da k'ok'ari, aibansan haka kema kikeba da jarumta.
Dariya sukayi gaba d'aya, ya Umar ya ce, "tab, ai dama Husna matsiwaciyace, Ku kawai takema alkunya, koba hakaba tawan? Yafad'a yana d'aga mata gira.
Harar wasa Asma'u tama ya Umar ta ce, ''bandadai Sheri my boss."
Nanma dariya sukeyi sosai.
Su Tasi'u duk suna kallonsu, kuma azatonsu su sukema dariyar, Dan haka duk jikinsu yakumayin sanyi, wasuma harsum fara nadamar abinda suka aikata ayau.
Ya Umar yatada motar sukayi sallama dasu yazeed suka tafi.
Dayazo saitinsu Dr jafar ma saida yad'aga musu hannu, amma ko tari babu Wanda yayi acikinsu, Dan duk sunyi gum, tundasu ya Umar suka bar wajen babu Wanda ya iya cewa A acikinsu, saidai kallon kallon kawai da zare idanu.
Nikuwa na ce, "hummmm.
__________________________
Ahanya ya Umar da Asma'u sai hirar abinda yafaru sukeyi suna dariya.
Dahaka har suka isa gida. Ya Umar yakwashi ledojin itakuma tasa6i fodiyo suka Shiga.
Afalo suka iske su hasiya da inna baito sunacin tuwo.
Bayan sun musu hannu suka zauna, ya Umar ya ce, " inna yau tuwo akamana?."
Wlhy tuwo nayi Umaru, nidai nagaji dacin shinkafarnan.
Aii wlhy inna kin taimakemu, nikaina bawani damuwa nayi da irin wad'annan abubuwan naiba, nifa aka bani tuwo to anmin dai-dai. Amma su o, e, aii ba'aso, saidai kayan kwad'ayi.
Asma'u datasan da ita yakeyi, ta cuno baki gaba amma batace komaiba.
Ya Umar yace nidai kar aji haushina bankira sunaba dai ko Hasiya?.
Oho dai, aikowa yay zagi akasuwa yasan dawanda yake. Cewar Asma'u tana Barin wajen.
Dariya suka rakata da ita suduka.
Ya Umar ma yamik'e yana fad'in inna bara na rage kayan jikina naje massalaci, danyau zaman cin tuwo zamuyi.
To Umar afito lafiya.
To innarmu, gobe iyanzu munyi kewarki wlhy, dama kiyi zamanki taredamu kawai, zamuyi farinciki wlhy.
'Yar dariya kawai inna baito tayi, ta ce, "a'a Umar, mijinafa?.
Saidai kuma haka inna, amma jimuke kamar karki tafi. Dariya kawai inna baito tayi. shikuma yashige d'akinsa.
*_Lubna_*
Zaune take a k'ataccen falonta, ta mik'e k'afafu gabanta kayan fruit ne da aka yanka k'anana, gefe kuma ga farfesun kaza daya gama had'uwa.